Sashe 27
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Masha ALLAHU kamar yanda kowa ya sani ne wannan zama mun yishi ne saboda Safwan da Khadija, saboda auren da Ubangiji ya nufa aka yi a tsakaninsu, to Masha ALLAH yanzu Malam Sanda ga gidansu Mijin 'yarka yanda idan ka tashi nemanta kasan ta inda zaka nemeta, Hajiya Balkisu kinga Mahaifin Khadija Malam Sanda wad'annan kuma abokan tafiyarshi ne, Khadija kin ga Mahaifiyar Mijinki Safwan Mahaifinshi kuma tuni ALLAH ya yi masa rasuwa,m sai dai Ni yayanshi tare da wannan k'anenshi tare da sauran 'yan uwanmu Mata da maza da suka rage, shi kam sai dai mu bishi da addu'ar ALLAH Ubangiji ya dad'a masa Rahama a cikin k'abarinshi tare da musulmin duniya gaba d'aya, mu ma idan ta mu ta zo yasa mu cika da imani"
Dukansu suka ce "Ameen Ameen" sannan d'aya bayan d'aya kowa ya yi jawabi tare da neman ma zaman auren nasu albarka, sannan aka ja hankalinsu duka daga shi har ita akan zaman auren tare da nuna masu muhimmancin auren tare da hak'uri a zamantakewar auren duka.
ALHMDLLH shi kanshi Baffahn na Dije yanzu hankalinshi ya kwanta sosai saboda ganin yanda suke Mutane masu karamci, daga nan shi ma ya damk'awa Safwan da Mahaifiyarshi har ma da Iyayen Maza amanar Dijenshi, tare da rok'onsu akan duk abunda ta yi wanda bai dace ba don ALLAH ayi hak'uri da ita da sannu zata dawo dai dai da yanda ake son kowace d'iyar ta kasance, don a fakaice ya yi masu nuni da su yi hak'uri da halayenta don ba ya son ya bayyana k'arara cewa ga laifin 'yarshi, ya fi son idan sun gani a matsayinsu na masu ilimi su fahimtar da ita abunda ya dace su d'orata kan hanya har ta fahimci rayuwar da yanda ake zama cikinta.
Taro ya watse akan cewa gobe tun da sassafe su Baffah'n za su kama hanyarsu ta komawa gida, sannan su Iyaye mazan suka yi sallama da su akan sai goben za su zo su yi sallama da su Baffah'n, Safwan da Hajiyarshi har gindin mota suka rakasu suna yi masu godiya har suka bar Gidan.
Dije kam suna fita ta tashi ta nufi Baffah'nta tana washe baki tace,. "Baffah Kai ma ka ci naman mai yawa ko? WALLAHI baka ga Wanda na ci ba ga abincinsu mai shegen dad'in tsiya"
Baffah ya washe Bakinshi ya ce, "kin samu gidan Aure Dije don ALLAH ki yi biyayya kinji?"
Dije ta d'aga Kai, tana matsa 'yan yatsunta tace,. "Ai ni duk ma aikin da suke so in yi masu zan yi WALLAHI ko don su dinga bani abincina mai dad'i ina ci"
Baffah ya ce,. "Duk abunda Mijinki ya sakaki ki yi masa kinji? haka ma Mahaifiyarshi kin ga dai suna da kirki don ALLAH kada ki yi abunda zai janyo har ace baki kyauta ba"
Dije tace,. ,"Insha ALLAHu Baffah ba Zan yi rashin ji ba ko cen garinmu ai ka ga su ke ja na ai"
Baffah ya ce "Nan ma ai dole su ja ki amman don ALLAH kar ki biyesu ki ce ke dole sai kin rama ki kyalesu da halinsu da sannu zaki ci ribar hak'urinki"
Dije tace "to Baffah amman don ALLAH ka ce da shi ya daina rik'e man hannu WALLAHI Ni bana son inyi ciki gashi yanzu har ciki biyu ya yi mani d'aya nan d'aya a k'auyenmu"
Ta k'are maganar cikin zubowar wasu 'yanmatan hawaye, Baffah zai yi magana kenan sai ga su Safwan d'in sun shigo, dole ya wayance yana fad'in
"Ki yi hak'uri ai ko nan gida ne kamar cen d'in saboda nan da cen duk d'aya ne a wajenki Babu banbanci"
Akafta😛
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Masu buk'atar Littafaina ga su kamar haka:*
*TARTSATSI*
*RUWA DA K'ANK'ARA*
*BAKAN GIZO*
*DIJE K'ARANGIYA*
*BAK'ON YANAYI sai dai shi na kud'i ne da d'ari uku kacal zaki sameshi a complete d'inshi😇*
*Lamba ta 28*
Haka Baffah ya shashantar da zancen aka yi ta fira har aka yi magrib suna tare da Safwan sunata fira duk da ba wani sabawa ya yi da su ba amman ba laifi sun d'an tab'a fira, kiran sallah'r yasa Dije ta yi cikin Gidan tare da matan biyu domin su yi SALLAH, su Baffah kuwa suka yi masallacin da ke k'ofar gidan.
Ko da dare ya yi Hajiya Mama ta saka Dije ta yi wanka da kanta ta nuna mata yanda zata yi kwalliya ba irinta haukarta da ta saba ba, ta d'auko wasu sababbin kayan bacci masu shegen kyau tace ta saka, Dije kam saboda hud'ubar da Baffah'nta ya yi mata sannan da kashedin da Safwan d'in ya yi mata shi yasa ta rage shirme in taga wani abu da bata sani ba sai ta yi shiru ba zata yi ta surutu ba, bakinta alekum ta saka kayan tare da fessesa mata turaren da Hajiya Mama ta yi sannan ta kira Surry tace da ita ta je ta Kai Dije d'akin Safwan, Dije ta zaro Ido waje tace
"Hajiya me zanyi wajenshi Sabida ALLAH Ni kam cikin daren nan yanzu??"
Hajiya ta dafe goshinta tace,. "Ki je ki yi kwanciyarki a cen kafin da safe sai a kaiki gidanki in da zaku zauna da Mijin naki"
Dije ta zaro Ido waje tace,. "Kina nufin gidan nan zan bari???, WALLAHI idan na barshi an cuceni wa zai bani irin abincin da na ci d'azu mai d'an karen dad'i?"
Hajiya Mama ta dafa kafad'arta tace,. "Ki kwantar da hankalinki insha ALLAHu abincin da zaki ci a cen har sai ya fi na wannan Gidan dad'i, yanzu dai ki je da safe idan kika zo zan yi maki bayanin komi"
Dije ta marairece cikin kuka tace,. "Yanzu tsakaninki da ALLAH d'akin Namiji zaki kaini inje in kwana???bayan nasan ke ma kanki kinsan cewa hakan bai dace ba amman kike k'ok'arin turani???"
Hajiya Mama ta dafe goshinta ba shiri ta kai zaune tace da Surry da ke sunne kai tana k'umshe dariya da ta je, sannan ta janyo hannun Dijen ta zaunar da ita kan gadon ta yi shiru na d'an lokaci sannan tace
"Ai dai kinsan cewa an yi maki aure da shi ko?"
Dije ta d'aga kanta, Hajiya Mama tace
"Masha ALLAH to ai kinga shi baya cikin jerin mazan da aka haramta ki je d'akinsu ko?"
Dije ta yi shiru na d'an lokaci tana tunani tace,. "To Ni dai tsakani da ALLAH Innata ta hanani ko magana in dinga tsayawa ina yi da maza sosai, kuma yanzu idan Baffahna ya ji ai WALLAHI dole ma ne ya dakeni, Ni dai don hasken da ALLAH ya yi wa Qur'ani kada ki bari ya sake yi man ciki na uku"
Hajiya Mama ta zaro ido waje tace,. "Ciki na Uku?????"
Dije tace, "Eh ya yi man d'aya a k'auyenmu yanzu gashi d'azu lokacin da ya zo kirana muje wurinku sai da ya yi man d'aya yanzu haka Ina jin macizai sun fara taruwa a cikina kin gani WALLAHI cikina ya k'ara yin k'ato"
Hajiya Mama ta yi shiru tana nazarin maganganun Dijen sai cen ta nisa tace,. "To ta yaya yake yi maki cikin halan don inji in yi masa fad'a ya daina kada ya sake??"
Dije ta b'ata fuska tare da ciro hannunta duka biyu ta nunawa Hajiya Mamar tace,. "Duba ki gani kowane hannu nawa da kike gani akwai cikinshi d'auke a ciki, gashi ina jin tsoron macizai da yawa idan na haifosu bansan ya zanyi da su ba"
Hajiya Mama ta yi murmushi irin nasu na manya tace "waton hannun naki ya rik'a ko ko ya abun yake ne?"
Dije ta goge hawayenta tace,. "Eh rik'e man ya yi har sau biyu shiyasa Nike jin tsoron ya sake yiman cikin, idan ba haka ba WALLAHI zan yi addu'a in mutu kafin lokacin sai ya san yanda zai yi da macizan idan sun fasa cikina sun fito"
Hajiya Mama ta rik'o hannunta tace,. "Wa ya sanar da ke hakan halan??"
Dije ta goge hawayenta tace,. "Innata"
Hajiya Mama ta yi Yar dariya sannan tace,. "Alhmdllh Innarki ta yi gaskiya sai dai ita baki gano abunda take nufi ba shiyasa, abunda take nufi shine idan har wani daban wanda ba Mjinki ba ya rik'a hannunki to anan ne za ki yi cikin macizan, amman kuma in dai har Mijinki ne ya tab'a hannun anan kam ba wani cikin macizai da zaki yi sai ma lada da zaki samu, ki yi tunani shin lokacin da ya rik'a hannun naki anyi maku aure ne ko kuma kafin ayi?"
Dije cikin sanyin jiki ta ce,. "Bayan anyi addu'ar d'aurin auren ne"
Hajiya Mama tace "Alhmdllh to kinga yanzu gaskiya ta fito saboda haka tashi mu je in rakaki da kaina ki yi kwanciyarki a cen da safe ki zo in baki wani labari"
Dije ta marairece Hajiya Mama ta rik'o hannunta suka nufi d'akin Safwan, Safwan kam yana kwance Kan gadonshi ya zurfafa dogon tunanin abunda yake so ya aiwatar saboda cikar muradin Abokinshi, yana cikin nazarin ne sai gashi ya ji k'wank'wasar d'akin cikin sanyin jiki yace
"Come in!"
Dije ta shigo kanta a duk'e tana zunb'urar baki, ba shiri ya yi zumbur ya mike tare da nunata da d'an yatsa yana fad'in
"Wa ya kawoki d'akin......."
Maganarshi ta mak'ale ne saboda ganin Hajiya Mama a bayanta, cikin sage hannu ya sosa kanshi ya sami gefen gadon ya zauna tare da duk'e kanshi yana feso iska a bakinshi, Hajiya Mama ta zaunar da ita a Kan gadon tace
"Ga Matarka nan sai da safe Ubangiji ALLAH ya baka ikon rik'e 'yar Mutane amana"
Tana k'are maganar ta d'ago fuskar Dije da hawaye suka wanke mata fuska shab'e shab'e tace
"Sai da safe 'yata ALLAH ya baku hak'urin zama da junanku"
Sannan ta fice daga Safwan har Dijen ba wanda ya yi dogon motsi har aka kwashi tsawon lokaci, sannan Dije ta mik'e tsaye zata fita ya yi saurin rik'o hannunta aiko ba shiri jikinta ya d'auki rawa tare da kallon hannun tana k'ok'arin k'wacewa, sai dai kasancewar ba rik'on wasa ya yi mata ba shiyasa bata sami damar k'wace hannun ba, cikin fushi tace
Dukansu suka ce "Ameen Ameen" sannan d'aya bayan d'aya kowa ya yi jawabi tare da neman ma zaman auren nasu albarka, sannan aka ja hankalinsu duka daga shi har ita akan zaman auren tare da nuna masu muhimmancin auren tare da hak'uri a zamantakewar auren duka.
ALHMDLLH shi kanshi Baffahn na Dije yanzu hankalinshi ya kwanta sosai saboda ganin yanda suke Mutane masu karamci, daga nan shi ma ya damk'awa Safwan da Mahaifiyarshi har ma da Iyayen Maza amanar Dijenshi, tare da rok'onsu akan duk abunda ta yi wanda bai dace ba don ALLAH ayi hak'uri da ita da sannu zata dawo dai dai da yanda ake son kowace d'iyar ta kasance, don a fakaice ya yi masu nuni da su yi hak'uri da halayenta don ba ya son ya bayyana k'arara cewa ga laifin 'yarshi, ya fi son idan sun gani a matsayinsu na masu ilimi su fahimtar da ita abunda ya dace su d'orata kan hanya har ta fahimci rayuwar da yanda ake zama cikinta.
Taro ya watse akan cewa gobe tun da sassafe su Baffah'n za su kama hanyarsu ta komawa gida, sannan su Iyaye mazan suka yi sallama da su akan sai goben za su zo su yi sallama da su Baffah'n, Safwan da Hajiyarshi har gindin mota suka rakasu suna yi masu godiya har suka bar Gidan.
Dije kam suna fita ta tashi ta nufi Baffah'nta tana washe baki tace,. "Baffah Kai ma ka ci naman mai yawa ko? WALLAHI baka ga Wanda na ci ba ga abincinsu mai shegen dad'in tsiya"
Baffah ya washe Bakinshi ya ce, "kin samu gidan Aure Dije don ALLAH ki yi biyayya kinji?"
Dije ta d'aga Kai, tana matsa 'yan yatsunta tace,. "Ai ni duk ma aikin da suke so in yi masu zan yi WALLAHI ko don su dinga bani abincina mai dad'i ina ci"
Baffah ya ce,. "Duk abunda Mijinki ya sakaki ki yi masa kinji? haka ma Mahaifiyarshi kin ga dai suna da kirki don ALLAH kada ki yi abunda zai janyo har ace baki kyauta ba"
Dije tace,. ,"Insha ALLAHu Baffah ba Zan yi rashin ji ba ko cen garinmu ai ka ga su ke ja na ai"
Baffah ya ce "Nan ma ai dole su ja ki amman don ALLAH kar ki biyesu ki ce ke dole sai kin rama ki kyalesu da halinsu da sannu zaki ci ribar hak'urinki"
Dije tace "to Baffah amman don ALLAH ka ce da shi ya daina rik'e man hannu WALLAHI Ni bana son inyi ciki gashi yanzu har ciki biyu ya yi mani d'aya nan d'aya a k'auyenmu"
Ta k'are maganar cikin zubowar wasu 'yanmatan hawaye, Baffah zai yi magana kenan sai ga su Safwan d'in sun shigo, dole ya wayance yana fad'in
"Ki yi hak'uri ai ko nan gida ne kamar cen d'in saboda nan da cen duk d'aya ne a wajenki Babu banbanci"
Akafta😛
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Masu buk'atar Littafaina ga su kamar haka:*
*TARTSATSI*
*RUWA DA K'ANK'ARA*
*BAKAN GIZO*
*DIJE K'ARANGIYA*
*BAK'ON YANAYI sai dai shi na kud'i ne da d'ari uku kacal zaki sameshi a complete d'inshi😇*
*Lamba ta 28*
Haka Baffah ya shashantar da zancen aka yi ta fira har aka yi magrib suna tare da Safwan sunata fira duk da ba wani sabawa ya yi da su ba amman ba laifi sun d'an tab'a fira, kiran sallah'r yasa Dije ta yi cikin Gidan tare da matan biyu domin su yi SALLAH, su Baffah kuwa suka yi masallacin da ke k'ofar gidan.
Ko da dare ya yi Hajiya Mama ta saka Dije ta yi wanka da kanta ta nuna mata yanda zata yi kwalliya ba irinta haukarta da ta saba ba, ta d'auko wasu sababbin kayan bacci masu shegen kyau tace ta saka, Dije kam saboda hud'ubar da Baffah'nta ya yi mata sannan da kashedin da Safwan d'in ya yi mata shi yasa ta rage shirme in taga wani abu da bata sani ba sai ta yi shiru ba zata yi ta surutu ba, bakinta alekum ta saka kayan tare da fessesa mata turaren da Hajiya Mama ta yi sannan ta kira Surry tace da ita ta je ta Kai Dije d'akin Safwan, Dije ta zaro Ido waje tace
"Hajiya me zanyi wajenshi Sabida ALLAH Ni kam cikin daren nan yanzu??"
Hajiya ta dafe goshinta tace,. "Ki je ki yi kwanciyarki a cen kafin da safe sai a kaiki gidanki in da zaku zauna da Mijin naki"
Dije ta zaro Ido waje tace,. "Kina nufin gidan nan zan bari???, WALLAHI idan na barshi an cuceni wa zai bani irin abincin da na ci d'azu mai d'an karen dad'i?"
Hajiya Mama ta dafa kafad'arta tace,. "Ki kwantar da hankalinki insha ALLAHu abincin da zaki ci a cen har sai ya fi na wannan Gidan dad'i, yanzu dai ki je da safe idan kika zo zan yi maki bayanin komi"
Dije ta marairece cikin kuka tace,. "Yanzu tsakaninki da ALLAH d'akin Namiji zaki kaini inje in kwana???bayan nasan ke ma kanki kinsan cewa hakan bai dace ba amman kike k'ok'arin turani???"
Hajiya Mama ta dafe goshinta ba shiri ta kai zaune tace da Surry da ke sunne kai tana k'umshe dariya da ta je, sannan ta janyo hannun Dijen ta zaunar da ita kan gadon ta yi shiru na d'an lokaci sannan tace
"Ai dai kinsan cewa an yi maki aure da shi ko?"
Dije ta d'aga kanta, Hajiya Mama tace
"Masha ALLAH to ai kinga shi baya cikin jerin mazan da aka haramta ki je d'akinsu ko?"
Dije ta yi shiru na d'an lokaci tana tunani tace,. "To Ni dai tsakani da ALLAH Innata ta hanani ko magana in dinga tsayawa ina yi da maza sosai, kuma yanzu idan Baffahna ya ji ai WALLAHI dole ma ne ya dakeni, Ni dai don hasken da ALLAH ya yi wa Qur'ani kada ki bari ya sake yi man ciki na uku"
Hajiya Mama ta zaro ido waje tace,. "Ciki na Uku?????"
Dije tace, "Eh ya yi man d'aya a k'auyenmu yanzu gashi d'azu lokacin da ya zo kirana muje wurinku sai da ya yi man d'aya yanzu haka Ina jin macizai sun fara taruwa a cikina kin gani WALLAHI cikina ya k'ara yin k'ato"
Hajiya Mama ta yi shiru tana nazarin maganganun Dijen sai cen ta nisa tace,. "To ta yaya yake yi maki cikin halan don inji in yi masa fad'a ya daina kada ya sake??"
Dije ta b'ata fuska tare da ciro hannunta duka biyu ta nunawa Hajiya Mamar tace,. "Duba ki gani kowane hannu nawa da kike gani akwai cikinshi d'auke a ciki, gashi ina jin tsoron macizai da yawa idan na haifosu bansan ya zanyi da su ba"
Hajiya Mama ta yi murmushi irin nasu na manya tace "waton hannun naki ya rik'a ko ko ya abun yake ne?"
Dije ta goge hawayenta tace,. "Eh rik'e man ya yi har sau biyu shiyasa Nike jin tsoron ya sake yiman cikin, idan ba haka ba WALLAHI zan yi addu'a in mutu kafin lokacin sai ya san yanda zai yi da macizan idan sun fasa cikina sun fito"
Hajiya Mama ta rik'o hannunta tace,. "Wa ya sanar da ke hakan halan??"
Dije ta goge hawayenta tace,. "Innata"
Hajiya Mama ta yi Yar dariya sannan tace,. "Alhmdllh Innarki ta yi gaskiya sai dai ita baki gano abunda take nufi ba shiyasa, abunda take nufi shine idan har wani daban wanda ba Mjinki ba ya rik'a hannunki to anan ne za ki yi cikin macizan, amman kuma in dai har Mijinki ne ya tab'a hannun anan kam ba wani cikin macizai da zaki yi sai ma lada da zaki samu, ki yi tunani shin lokacin da ya rik'a hannun naki anyi maku aure ne ko kuma kafin ayi?"
Dije cikin sanyin jiki ta ce,. "Bayan anyi addu'ar d'aurin auren ne"
Hajiya Mama tace "Alhmdllh to kinga yanzu gaskiya ta fito saboda haka tashi mu je in rakaki da kaina ki yi kwanciyarki a cen da safe ki zo in baki wani labari"
Dije ta marairece Hajiya Mama ta rik'o hannunta suka nufi d'akin Safwan, Safwan kam yana kwance Kan gadonshi ya zurfafa dogon tunanin abunda yake so ya aiwatar saboda cikar muradin Abokinshi, yana cikin nazarin ne sai gashi ya ji k'wank'wasar d'akin cikin sanyin jiki yace
"Come in!"
Dije ta shigo kanta a duk'e tana zunb'urar baki, ba shiri ya yi zumbur ya mike tare da nunata da d'an yatsa yana fad'in
"Wa ya kawoki d'akin......."
Maganarshi ta mak'ale ne saboda ganin Hajiya Mama a bayanta, cikin sage hannu ya sosa kanshi ya sami gefen gadon ya zauna tare da duk'e kanshi yana feso iska a bakinshi, Hajiya Mama ta zaunar da ita a Kan gadon tace
"Ga Matarka nan sai da safe Ubangiji ALLAH ya baka ikon rik'e 'yar Mutane amana"
Tana k'are maganar ta d'ago fuskar Dije da hawaye suka wanke mata fuska shab'e shab'e tace
"Sai da safe 'yata ALLAH ya baku hak'urin zama da junanku"
Sannan ta fice daga Safwan har Dijen ba wanda ya yi dogon motsi har aka kwashi tsawon lokaci, sannan Dije ta mik'e tsaye zata fita ya yi saurin rik'o hannunta aiko ba shiri jikinta ya d'auki rawa tare da kallon hannun tana k'ok'arin k'wacewa, sai dai kasancewar ba rik'on wasa ya yi mata ba shiyasa bata sami damar k'wace hannun ba, cikin fushi tace