Sashe 70
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Rigiji Gabji wani kaya sai Amalii ina gwanayen wasu ga nawa 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻har ga ALLAH ruwan sharhinku akan book ɗin Ƙarangiya yana faranta man rai ba kaɗan ba, haƙiƙa dole inyi alfakhari da ku saboda ku ɗin nawa ne ba ƙarya,ina miƙa ɗinbin godiyata gareki ƴargata Maman Sultan, irin godiyar da baki ba zai taɓa iya zayyanowa ba, alkhairin ALLAH ya kai maki har ƙasar Niger cikin gidan Baban Sultan akan gadonki wanda kike bacci a kuma gefen da kike kwanciya😝😜*
*Lamba ta 64*
A zafafe Ruma ta yi wani tsalle ta cafke ashanar cikin wani firgici da tashin hankalin da ya ziyarceta, don garin cafke ashanar fetur ɗin da ke malale ƙasa tyles ɗin ya jata ta faɗi tim! A ƙasa, amman duk da hakan sai dai ta yiwa ashanar murzar bala'i duk da zafin ƙunar da ya ratsa hannun nata, cikin fushi ta miƙe ta yo kan Zee zata ƙwace ashanar, Zee ta ƙara yin baya cikin bushewar zuciya da ta yi dacen aka janye mata imani a zuciyar don babu abunda take so irin ta ƙonesu da kowa ma da ke gidan har itama kanta, saboda a ganinta hakan ne kawai zata yi ta cire zafin abunda take ji a zuciyarta, Ruma tana girgiza kai cikin ruɗewa tace
"Kar ki aikata abunda zaki zo ki yi danasani daga baya"
Hawaye suna zuba akan fuskar Zee da idonta suka rikiɗe zuwa jajaye saboda tsallar tsagwaron bushewar da zuciyarta ta yi, ta sake kunna wata ashanar hawaye suna zuba akan fuskarta tace
"Matuƙar na barsu da rai bazan taɓa yafewa kaina ba, ya zama dole su ɗanɗani azabar mutuwa dai dai da cin amanar da suka aikata ma....."
Wani mari ne da ya sauka akan fuskarta ne yasa ta yi saurin sakin guntuwar ashanar da ta kusa cenyewa a hannunta, Ruma ta yi saurin taketa da ƙafa ta murje, a zafafe Zee ta waiga domin taga wace mai ƙarfin halin ce ta mareta, yanda ta ga fuskar Surayya da ke tsaye gefenta tana huci yasa ta yi wata gajerar dariya ta ce
"Wow sannu fa ki ce masu mutuwar yau yawa ne da su? To ki jira ke ma saura kaɗan naki ajalin ya iso ku sa da ke"
Tana ƙare maganar ta fiddo wata ƙwarar ashana kafin ta kyasta ta sake jin wani uban naushi da Surayya ta sauke mata a gefen fuskarta, ba shiri ta saki ashanar ƙasa Ruma ta ɗauke ta fice da ashanar cikin sauri, Zee ko ta yi cikin Surayya suka fara kaiwa juna duka, kafin ka ce damben bala'i ya kacame a tsakaninsu ƴan'uwan Zee ɗin su biyu da ke tsaye suna kallon abunda ke faruwa suna rabon faɗan, sai ga Husnah aguje itama kamar wata zakanya ta rufarwa Zee suka yi ta mazgarta ita da Surayya, sai dukanta suke yi kamar ALLAH ya aikosu tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta koma laƙwas Husnah ta kwashe mata ƙafafuwa ta faɗi ƙasa ba shiri, Surayya ta yi saurin haye ruwan cikinta suna ta duka duk da ƙoƙarin hanasu da ƴan'uwan Zee suke yi, amman hakan bai hanasu yi mata dukan kawo wuƙa ba.
Safwan da Dijenshi kam basu ma san me ke faruwa ba har sai da Surayya ta kirasu a waya ne take sanarwa da Safwan ɗin abunda Zee take yi don a lokacin itama suna sashen Dijen ne wani ma'aikaci ya zo aguje yake sanar da su abunda ke faruwa, shiyasa hankalin Surayya a tashe ta kira Safwan ɗin saboda zuciyarta ta bata cewa Zee ba alkhairi zata shuka ba, tun yanayin da ta ganta lokacin da suka dawo ta yi sashenta cikin fushi, bayan ta gama kiran Safwan ɗin ta sanar da shi abunda aka faɗa masu ne ta ce da su Husnah su kira Aunty Ummi su sanar da ita kafin ta je ta ga abunda ke faruwa, aiko sai gashi tana zuwa ta ji kalaman da Zee take faɗa Shiyasa bata yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata hannu.
Ko da Safwan ɗin da Dije suka fito cike da firgici akan fuskarsu, sai ga wani sabon firgicin da ya sake sakasu ruɗewa saboda ganin gaba ɗaya falon warin fetur ne da wani wanda bai ƙasara bin iska ba malale a ƙasa, Safwan ya kai kallonshi inda su Surayya da ke ta jibgar Zee har lokacin, ya yi saurin katsa masu wata uwar tsawa suka zabura cikin firgici daga su har ita Zee ɗin da ke kwance ligya ligya don ta daku ba ƙarya.
Ya ƙasaro wajensu ya kallesu ɗaya bayan ɗaya ya ɗaga murya a fusace ya ce
"Wai me ke faruwa ne wai??"
Zee ta miƙe da ƙyar ta kalleshi cikin wani kallon reni da kumburarren bakinta da suka fashe ta ce
"Ni zaka tambaya don ni ce zan yi ajalinku dukanku ka sani ka ƙara sani dukanku sai na kasheku"
Tana ƙare maganar ta yi sashenta aguje ko wa ya bita da kallo, cikin fushi Safwan ya bita ƴan'uwan Zee ɗin da Ruma suka biyoshi a baya suna bashi haƙuri, Dije ko ta yi wurinsu Surayya tana tambayarsu mafarin abun.
Safwan yana kaiwa sashen nata sai ga ta sun ci karo da ita da sharɓeɓiyar wuƙarta ta nufoshi gadan gadan da nufin ta soka masa ita, ya yi jarumtar riƙe tsinin wuƙar ya fisgeta da ƙarfi wuƙar ta yankeshi sosai amman duk da hakan bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata wani wahalallen mari har sai da taga taurari, sannan ya dinga kai mata duka ta ko'ina kamar wani zaki, itama har da su ƙarfin halin kuwar faɗin sai ta kasheshi duk da uban kashin da take sha, don kuwa da ya yi wani ball da ita har sai da ta kai bango, sannan ya damƙo gashinta ya janyota ƙiii ya fito da ita har gindin Motarshi, sannan ya jefata motar ya saka lock sannan ya faɗa cikin zafin nama ya tada motar ya yi wani uban ribas sannan ya fisgeta da ƙarfin tsiya ya fice, bai zame ko'ina da ita ba sai headquarter'r ƴansanda, kai tsaye ya nemi ganin D.p.o ya damƙa masu ita da hannunshi tare da sanar da su cewa Matarshi ce take son kasheshi, su riƙe ta a hannunsu su yanke mata hukunci dai dai da laifinta, suka karɓeta suka jefata ɗakin ajiya suka kulle sannan suka sanar da shi zasu yi ƙwaƙƙwaran bincike akan case ɗin idan har komi ya kammala ta aikata abunda ake tuhumarta da shi to zasu yanke mata hukunci dai dai da laifinta.
Sannan ya baro wurinsu tare da wasu ƴansanda da za su zo yin bincike akan abunda ya faru, shima ya nufo gida saboda damunshi da kiran da ake ta yi, don yaso zuwa ayi masa kanikancin hannun da ya yanke da shi, amman yanda yake jin zuciyarshi ne yasa ko kiran da ake ta yi masa ɗaya bai ɗaga ba, sai na Hajiyarshi ko shi don baya iya ganin kiran yaƙi ɗauka, sai dai bai iya furta ko kalma ɗaya ba sai "to" kawai da ya faɗa, saboda tsananin ɓaci ran da ya cunkushe masa zuciya.
Ko da suka shiga gidan suka taradda kowa a harabar gidan ana jiran zuwanshi, cike da ruɗewa Aunty Ummi ta nufoshi tana faɗin
"Ba abunda ya sameka ko to Alhmdllh mun godewa ALLAH Hajiyarmu ba abunda ya sameshi"
Ya baiwa ƴansandan dama suka shiga ciki suna ta bincikensu, har wuƙar da galam ɗin fetur duk sai da suka fito da su duka, sannan suka fara yiwa mutane tambaya ɗaya bayan ɗaya, don har su kansu ma'aikatan gidan ba'a barsu ba sai da aka tambayesu suka faɗi abunda suka sani, sannan ƴansandan suka bar gidan tare da rahotannin da suka naɗa a wayoyinsu.
Safwan da ke jikin Motarshi tsaye ya ƙaraso wajen Hajiya Mama yana dafe kai ya zauna kan wani ɗan dakalin da aka zagaye wasu flowers, hannunshi da suka hango da ya yi bala'in walshewa da wuƙa kowa hankalinshi ya tashi, Hajiyarmu ta ƙaraso wajenshi ta ce
"Garin ya ya haka ta faru??"
Ya yi shiru sannan ya yarfa hannu saboda jinin da ke ɗiga har lokacin ya ce
"Ni ma bansan abunda yake faruwa ba har sai da Surayya ta sanar da ni"
Hajiya Mama cikin damuwa ta ce
"Ina ita Zainab ɗin?"
Ya yi shiru sannan ya ce, "tana hannun ƴansandan"
Ko wa ya yi shiru yana nazarin abun a ranshi sannan Hajiyar ta ce
"To ka je a yi maka dressing ɗin hannun sannan ka dawo muna jiranka"
Safwan ya miƙe zuciyarshi kamar zata fashe ya kalli su Ruma da ke tsaye dukansu sun sha jinin jikinsu ya ce
"Kada in dawo in taradda ku cikin gidana"
Sannan ya ja Motarshi ya fice aguje, su Hajiya Mama suka yi sashen Dijen suka zauna, inda su ke ta lallahin Dijen da ke ta kuka saboda tunda ta ji abunda Zee ta ce a bakin Surayya hankalinta ya tashi ta fara kuka, sai ga shi kuma ta hango Safwan ɗin yana jan Zee a ƙasa hannunshi sai zubar jini yake yi, akan hakan ta sake ruɗewa tana ta kuka don jin take yi kamar ma ta bar masu gidansu ta koma garinsu tun kafin a kasheta ga banza, don ganin ƴansandan ma yasa ta ji wani tsoro ya sake kamata.
Ko da Safwan ya dawo an ɗaure masa hannu da bandeji bayan an ɗinke masa ƙatuwar yankuwar da ya yi, ya shigo ya zauna idonshi akan Dijenshi da ke sharar ƙwallah idonta sun yi ja saboda kukan da ta sha, cikin sanyin jiki ya ce
"To ke me kike wa kuka kuma yanzu?"
Aunty Ummi ta ce "dole ta yi kuka tunda bata taɓa ganin irin wannan bala'i ba a rayuwarta, wannan matar ƙaddara ai babu mai fatar ALLAH ya haɗashi da ita bale ta zowa mutum a matsayin kishiya"
Ta ƙare maganar cikin yin wani kalar mere kamar wata yarinya, Hajiya Mama ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce
"Yanzu dai abunda ya faru ya riga da ya faru fatanmu kawai ALLAH ya taƙaita wahala kuma ya tsare gaba"
*Lamba ta 64*
A zafafe Ruma ta yi wani tsalle ta cafke ashanar cikin wani firgici da tashin hankalin da ya ziyarceta, don garin cafke ashanar fetur ɗin da ke malale ƙasa tyles ɗin ya jata ta faɗi tim! A ƙasa, amman duk da hakan sai dai ta yiwa ashanar murzar bala'i duk da zafin ƙunar da ya ratsa hannun nata, cikin fushi ta miƙe ta yo kan Zee zata ƙwace ashanar, Zee ta ƙara yin baya cikin bushewar zuciya da ta yi dacen aka janye mata imani a zuciyar don babu abunda take so irin ta ƙonesu da kowa ma da ke gidan har itama kanta, saboda a ganinta hakan ne kawai zata yi ta cire zafin abunda take ji a zuciyarta, Ruma tana girgiza kai cikin ruɗewa tace
"Kar ki aikata abunda zaki zo ki yi danasani daga baya"
Hawaye suna zuba akan fuskar Zee da idonta suka rikiɗe zuwa jajaye saboda tsallar tsagwaron bushewar da zuciyarta ta yi, ta sake kunna wata ashanar hawaye suna zuba akan fuskarta tace
"Matuƙar na barsu da rai bazan taɓa yafewa kaina ba, ya zama dole su ɗanɗani azabar mutuwa dai dai da cin amanar da suka aikata ma....."
Wani mari ne da ya sauka akan fuskarta ne yasa ta yi saurin sakin guntuwar ashanar da ta kusa cenyewa a hannunta, Ruma ta yi saurin taketa da ƙafa ta murje, a zafafe Zee ta waiga domin taga wace mai ƙarfin halin ce ta mareta, yanda ta ga fuskar Surayya da ke tsaye gefenta tana huci yasa ta yi wata gajerar dariya ta ce
"Wow sannu fa ki ce masu mutuwar yau yawa ne da su? To ki jira ke ma saura kaɗan naki ajalin ya iso ku sa da ke"
Tana ƙare maganar ta fiddo wata ƙwarar ashana kafin ta kyasta ta sake jin wani uban naushi da Surayya ta sauke mata a gefen fuskarta, ba shiri ta saki ashanar ƙasa Ruma ta ɗauke ta fice da ashanar cikin sauri, Zee ko ta yi cikin Surayya suka fara kaiwa juna duka, kafin ka ce damben bala'i ya kacame a tsakaninsu ƴan'uwan Zee ɗin su biyu da ke tsaye suna kallon abunda ke faruwa suna rabon faɗan, sai ga Husnah aguje itama kamar wata zakanya ta rufarwa Zee suka yi ta mazgarta ita da Surayya, sai dukanta suke yi kamar ALLAH ya aikosu tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta koma laƙwas Husnah ta kwashe mata ƙafafuwa ta faɗi ƙasa ba shiri, Surayya ta yi saurin haye ruwan cikinta suna ta duka duk da ƙoƙarin hanasu da ƴan'uwan Zee suke yi, amman hakan bai hanasu yi mata dukan kawo wuƙa ba.
Safwan da Dijenshi kam basu ma san me ke faruwa ba har sai da Surayya ta kirasu a waya ne take sanarwa da Safwan ɗin abunda Zee take yi don a lokacin itama suna sashen Dijen ne wani ma'aikaci ya zo aguje yake sanar da su abunda ke faruwa, shiyasa hankalin Surayya a tashe ta kira Safwan ɗin saboda zuciyarta ta bata cewa Zee ba alkhairi zata shuka ba, tun yanayin da ta ganta lokacin da suka dawo ta yi sashenta cikin fushi, bayan ta gama kiran Safwan ɗin ta sanar da shi abunda aka faɗa masu ne ta ce da su Husnah su kira Aunty Ummi su sanar da ita kafin ta je ta ga abunda ke faruwa, aiko sai gashi tana zuwa ta ji kalaman da Zee take faɗa Shiyasa bata yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata hannu.
Ko da Safwan ɗin da Dije suka fito cike da firgici akan fuskarsu, sai ga wani sabon firgicin da ya sake sakasu ruɗewa saboda ganin gaba ɗaya falon warin fetur ne da wani wanda bai ƙasara bin iska ba malale a ƙasa, Safwan ya kai kallonshi inda su Surayya da ke ta jibgar Zee har lokacin, ya yi saurin katsa masu wata uwar tsawa suka zabura cikin firgici daga su har ita Zee ɗin da ke kwance ligya ligya don ta daku ba ƙarya.
Ya ƙasaro wajensu ya kallesu ɗaya bayan ɗaya ya ɗaga murya a fusace ya ce
"Wai me ke faruwa ne wai??"
Zee ta miƙe da ƙyar ta kalleshi cikin wani kallon reni da kumburarren bakinta da suka fashe ta ce
"Ni zaka tambaya don ni ce zan yi ajalinku dukanku ka sani ka ƙara sani dukanku sai na kasheku"
Tana ƙare maganar ta yi sashenta aguje ko wa ya bita da kallo, cikin fushi Safwan ya bita ƴan'uwan Zee ɗin da Ruma suka biyoshi a baya suna bashi haƙuri, Dije ko ta yi wurinsu Surayya tana tambayarsu mafarin abun.
Safwan yana kaiwa sashen nata sai ga ta sun ci karo da ita da sharɓeɓiyar wuƙarta ta nufoshi gadan gadan da nufin ta soka masa ita, ya yi jarumtar riƙe tsinin wuƙar ya fisgeta da ƙarfi wuƙar ta yankeshi sosai amman duk da hakan bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata wani wahalallen mari har sai da taga taurari, sannan ya dinga kai mata duka ta ko'ina kamar wani zaki, itama har da su ƙarfin halin kuwar faɗin sai ta kasheshi duk da uban kashin da take sha, don kuwa da ya yi wani ball da ita har sai da ta kai bango, sannan ya damƙo gashinta ya janyota ƙiii ya fito da ita har gindin Motarshi, sannan ya jefata motar ya saka lock sannan ya faɗa cikin zafin nama ya tada motar ya yi wani uban ribas sannan ya fisgeta da ƙarfin tsiya ya fice, bai zame ko'ina da ita ba sai headquarter'r ƴansanda, kai tsaye ya nemi ganin D.p.o ya damƙa masu ita da hannunshi tare da sanar da su cewa Matarshi ce take son kasheshi, su riƙe ta a hannunsu su yanke mata hukunci dai dai da laifinta, suka karɓeta suka jefata ɗakin ajiya suka kulle sannan suka sanar da shi zasu yi ƙwaƙƙwaran bincike akan case ɗin idan har komi ya kammala ta aikata abunda ake tuhumarta da shi to zasu yanke mata hukunci dai dai da laifinta.
Sannan ya baro wurinsu tare da wasu ƴansanda da za su zo yin bincike akan abunda ya faru, shima ya nufo gida saboda damunshi da kiran da ake ta yi, don yaso zuwa ayi masa kanikancin hannun da ya yanke da shi, amman yanda yake jin zuciyarshi ne yasa ko kiran da ake ta yi masa ɗaya bai ɗaga ba, sai na Hajiyarshi ko shi don baya iya ganin kiran yaƙi ɗauka, sai dai bai iya furta ko kalma ɗaya ba sai "to" kawai da ya faɗa, saboda tsananin ɓaci ran da ya cunkushe masa zuciya.
Ko da suka shiga gidan suka taradda kowa a harabar gidan ana jiran zuwanshi, cike da ruɗewa Aunty Ummi ta nufoshi tana faɗin
"Ba abunda ya sameka ko to Alhmdllh mun godewa ALLAH Hajiyarmu ba abunda ya sameshi"
Ya baiwa ƴansandan dama suka shiga ciki suna ta bincikensu, har wuƙar da galam ɗin fetur duk sai da suka fito da su duka, sannan suka fara yiwa mutane tambaya ɗaya bayan ɗaya, don har su kansu ma'aikatan gidan ba'a barsu ba sai da aka tambayesu suka faɗi abunda suka sani, sannan ƴansandan suka bar gidan tare da rahotannin da suka naɗa a wayoyinsu.
Safwan da ke jikin Motarshi tsaye ya ƙaraso wajen Hajiya Mama yana dafe kai ya zauna kan wani ɗan dakalin da aka zagaye wasu flowers, hannunshi da suka hango da ya yi bala'in walshewa da wuƙa kowa hankalinshi ya tashi, Hajiyarmu ta ƙaraso wajenshi ta ce
"Garin ya ya haka ta faru??"
Ya yi shiru sannan ya yarfa hannu saboda jinin da ke ɗiga har lokacin ya ce
"Ni ma bansan abunda yake faruwa ba har sai da Surayya ta sanar da ni"
Hajiya Mama cikin damuwa ta ce
"Ina ita Zainab ɗin?"
Ya yi shiru sannan ya ce, "tana hannun ƴansandan"
Ko wa ya yi shiru yana nazarin abun a ranshi sannan Hajiyar ta ce
"To ka je a yi maka dressing ɗin hannun sannan ka dawo muna jiranka"
Safwan ya miƙe zuciyarshi kamar zata fashe ya kalli su Ruma da ke tsaye dukansu sun sha jinin jikinsu ya ce
"Kada in dawo in taradda ku cikin gidana"
Sannan ya ja Motarshi ya fice aguje, su Hajiya Mama suka yi sashen Dijen suka zauna, inda su ke ta lallahin Dijen da ke ta kuka saboda tunda ta ji abunda Zee ta ce a bakin Surayya hankalinta ya tashi ta fara kuka, sai ga shi kuma ta hango Safwan ɗin yana jan Zee a ƙasa hannunshi sai zubar jini yake yi, akan hakan ta sake ruɗewa tana ta kuka don jin take yi kamar ma ta bar masu gidansu ta koma garinsu tun kafin a kasheta ga banza, don ganin ƴansandan ma yasa ta ji wani tsoro ya sake kamata.
Ko da Safwan ya dawo an ɗaure masa hannu da bandeji bayan an ɗinke masa ƙatuwar yankuwar da ya yi, ya shigo ya zauna idonshi akan Dijenshi da ke sharar ƙwallah idonta sun yi ja saboda kukan da ta sha, cikin sanyin jiki ya ce
"To ke me kike wa kuka kuma yanzu?"
Aunty Ummi ta ce "dole ta yi kuka tunda bata taɓa ganin irin wannan bala'i ba a rayuwarta, wannan matar ƙaddara ai babu mai fatar ALLAH ya haɗashi da ita bale ta zowa mutum a matsayin kishiya"
Ta ƙare maganar cikin yin wani kalar mere kamar wata yarinya, Hajiya Mama ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce
"Yanzu dai abunda ya faru ya riga da ya faru fatanmu kawai ALLAH ya taƙaita wahala kuma ya tsare gaba"