Sashe 52
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Inna tace "izininshi zamu nema ai saboda duk abunda zai sa ta kamo hanya tun daga cen har nan to abun ba ƙarami bane, saboda haka don ALLAH idan ya zo ka nuna masa kana son a bar Dijen nan ta ɗan kwana biyu"
Baffah cike da mamakinta yace, "ke fa kika ce da ni ga dalilin da yasa ta gudo to kuma yanzu sai ya zo tafiya da ita kuma muce a barta ta yi kwana biyu?, Ni fa bana son abunda zai sa mutanen nan su ga rashin kyautawarmu, ko dai akwai wani abu bayan wannan ne?"
Cikin damuwa Inna tace, "babu wani abu amman kasani ko yanzu tsugunne bata ƙare ba, matuƙar ta koma ba tare da an fahimtar da ita minene auren ba da abunda ya ƙumsa, saboda ina jin tsoron tace zata sake biyo doguwar hanyar nan ita kaɗai ko don gudun wani abu mara kyau ya sameta"
Baffah ya yi shiru yana nazari sannan yace, "to kuma Hasiya kin yi nazari anan, to ALLAH yasa shi ma idan ya zo ya amince ya bar muna ita ɗin"
Inna tace "ai nuna masa ɓacin ranka zaka yi akan sakacin da ya yi har ta biyo wannan uwar hanyar ita kaɗai"
Baffah ya yi saurin faɗin, "kar fa ki janyo inji kunya wajen surukina?"
Inna tace "ba wani jin kunya hakan da zaka yi shine zai ƙwatowa Dije ƴancinta, saboda gobe ya ji tsoron ƙara yin sakaci da ita har ta biyo hanya ba tare da sananinshi ba"
Tofa Inna uhum da kinsan halin da mijin Dijen yake ciki da ba ki ce haka ba😔
Akafta😉
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*DOMIN JIN DAƊINKU MASOYANA ku natsu tsaf ku ci gaba da kwasar ganima😂😝*
*Lamba ta 50*
Safwan kam firgicin da yake ciki ne yasa ya baje ƙasa cikin kiɗimewa yana ta sambatun kiran sunan Dijen, tare da faɗin
"Ina kika shiga ne don ALLAH ki dawo wallahi ina sonki ke ma kinsani ai"
Har dare ya raba yana ta abu ɗaya zuwa lokacin mutane sun fara taruwa kanshi ana tambayarshi mafari, da dai ya fahimci ya tarawa kanshi ƴan kallo ne ya tashi ya faɗa Motarshi ya nufi gidansu wani ɗan uwansu kuma abokinshi, cike da tsantsar tashin hankali yake yi masa bayanin duk abunda yake faruwa, Abokin nashi ya jinjina abun a ranshi sannan ya ce
"A gaskiya Abokina ka yi kuskure babba yanzu mafita ɗaya ce ka je ka baiwa Hajiyar Haƙuri kafin ka kama hanyar zuwa garinsu yarinyar, saboda jikina yana bani ta yi gida don ta gaji da abunda kake yi mata ne shiyasa ta gudu"
Sannan Safwan ya tuno da wayarshi ya ɗaukota da nufin kiran Hajiyar sai ga kiran Lawi da Kamal ya fi ashirin a wayar, cikin sauri ya kira Lawin da rawar baki yake faɗin
"An ganta?"
Lawi murya mai cike da damuwa yace "WALLAHi ba'a ganta ba ni na fara zargin ko ta yi garinsu"
Safwan ya dafe kanshi cikin wani sabon firgici yace,. "Don Allah Abokina ka roƙar mani Hajiya in dawo gidan in bata haƙuri WALLAHi gobe tun da sassafe zan kama hanyar garinsu Khadija in dawo da ita"
Lawi yace "kayi haƙuri Abokina WALLAHi Hajiya ta shiga damuwa sosai akan ɓatan khadija yanzu haka ma da ƙyar na lallasheta ta daina kuka, ga gidan gaba ɗaya hankalinsu ya tashi madadin farin ciki gida ya koma na jimami"
Safwan a kiɗime ya kashe wayar tare da furta "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un Allahumma la sahla illa maja'altahu sahla, ALLAH ka tsare yarinyar nan a duk inda take, Ubangiji ka bani ƙarfin gwiwar tunkarar wannan mummunar ƙaddara da ta faɗowa rayuwata"
Ya kalli Abokin nashi da jajayen idanuwanshi yace, "bari inje Mubarak banga ta zama ba tunda har nine na janyo komi"
Mubarak cike da tausayinshi yace, "ba dai yanzu kake nufin zaka bi bayanta ba?"
A zafafe ya faɗa motarshi yana faɗin "banga ta zama ba ai kuma matuƙar ba ganin yarinyar nan nayi ba....."
Kiran wayarshi ne ya katse maganar da yake yi cikin sauri ya ɗaga saboda ganin numbar Hajiyarshi ce, kafin ma yayi magana yaji muryarta cikin muryar kuka tace
"WALLAHi matuƙar baka dawo man da yarinyata ba to kada ka kuskura ka tako ƙafarka cikin gidan nan"
Cikin rawar murya yace, "ki bini da addu'ar tsari kawai Hajiyata, nayi maki alkƙawali bazaki ganni ba sai tare da Khadija insha ALLAHu"
Kittt! Hajiyar ta kashe wayar saboda wani kukan tausayin kansu da ya kamata, Surayya dake ta bata haƙuri ta yi saurin faɗin
"Don girman ALLAH Hajiyarmu ki yi haƙuri Insha ALLAHu ba abunda zai sami Khadijah ALLAH zai kareta a duk inda take"
Hajiya ta miƙe ta nufi toilet Surayya da Fiddo da yayyensu biyu mata da wasu ƴanuwasu da ke ɗakin suka bita da kallon tausayi, saboda yanda ta ɗaga hankalinta sosai akan rashin ganin Dijen, kowa sai faɗin albarkacin bakinshi yake yi akan lamarin.
Wannan shine abunda ya faru kafin Hajiya ta kira garinsu Dijen ta ji labarin cewa tana cen, don ko shi Safwan ɗin yana kan hanyarshi ne ya sami labarin cewa tana garinsu a bakin Surayya, saboda ƙoƙarinta na son rage masa damuwar da yake ciki.
Ranar yinin bikin Surayyar ma bikin ba wani armashi saboda damuwar da uwar bikin take ciki, haka aka tattara aka kai Surayya ɗakin Mijinta ita kanta zuciyarta ba daɗi saboda halin damuwar da ta baro Hajiyarsu a ciki.
Safwan kam sai da ya ganshi a babban birnin su Dijen sannan hankalinshi ya fara daidaito, ya yi masauki anan sannan ya kimtsa sosai cikin shiga ta alfarma ya buga Motarshi ya nufi ƙauyensu Dijen, zuciyarshi cike da jin daɗin matsalarshi ta zo ƙarshe, saboda fushin da Hajiyar take yi da shi ya fi komi ɗaga masa hankali fiye da duk wani hali da yake ciki.
Dije kam kasancewar daga ita sai kayan jikinta ta shigo garin, Inna ta ɗauki turminta biyu ta baiwa Usmanu tace ya kai babban birninsu inda aka yi wa Hansai ɗinkinta na aure ayowa Dijen ɗinkin Express saboda mijinta yana kan hanya, ya karɓa ya tafi yana dariyar yanda Inna take son farantawa surukinta.
Da marece sakaliya Usmanu ya dawo da ɗinkunan Inna ta karɓa tana ta murna Dije kam iyakacinta ido, don gaba ɗaya jin take yi zama gidan ya gundureta saboda jin da ta yi ance Safwan yana kan hanyar zuwa garin.
Kasancewar shagar dare ya yiwa garinsu Dijen shiyasa da yawa mutane basu san da zuwan nashi ba, cike da jin daɗi ya yi parking ƙofar gidan ya fito yana baza babbar riga sai tashin ƙamshi yake yi.
Jin ƙarar ajiye motar yasa Usmanu saurin fitowa saboda daman cen kowa da tsumayin zuwan nashi yake a gidan, bayan sun yi musabaha ne Usmanu ya ce da shi ya shigo, Safwan ya biyo bayanshi zuciyarshi sai dakan lugude take yi saboda tsoron kada Dijen ta bashi kunya a gaban surukan nashi, da sallamarshi a baki ya shiga Baffah da Inna baki har kunne suke amsa masa sallamar, Dije da ke ɗaki tana gunguni tun daga cen ta ji yo ƙamshin turarenshi, ta yi saurin duƙunkunewa kan gadon har da su lulluɓewa duk da gayun da Inna tasata ta yi na tarbon Safwan ɗin.
Safwan cikin ladabi da jin nauyinsu ya rusuna yana gayar dasu, inda suma ɗin suke amsawa cikin mutunta juna da karamci irin na surukantaka, bayan an ƙare gaishe gaishen ne Safwan ya ɗan muskuta tare da ƙara sunne kanshi yace
"Don ALLAH ayi haƙuri da zuwan da Khadija ta yi WALLAHi bansan da zuwan na ta ba a yafe mani don ALLAH"
Dije daga cen ɗaki jin abinda ya faɗa yasa ta yi zumbur ta fito tana huci tace
"Ba kai kace......."
"Kul!" Katon kashedin da Inna ta yi mata kenan wanda ya sata yin shiru ba shiri, ta yi saurin komawa ɗakin tare da fashewa da kuka tana faɗin
"Shikenan Ni komi na yi bani da gaskiya ai"
Baffah ya kalli Safwan da kyau yace, "ka yi haƙuri da halinta don ALLAH don alamu duk sun nuna ba ƙaramin surutu take sakaku ba, don ko wannan zuwan da ta yi hakan ya tabbatar mani da cewa har yanzu bata san minene auren ba, ina mai ƙara baka haƙuri akan shirmen da take yi maku don ALLAH ku ƙara haƙuri da ita, insha ALLAHu da sannu komi zai daidaita har ma ku yi alfahari da zamanta cikinku"
Safwan ya duƙe kai yana murmushi yace, "ba komi Baffah insha ALLAHU ma komi ya wuce daga yanzu, saboda gobe idan ALLAH ya kaimu lafiya nike son mu koma tare da ita"
Baffah ya yi shiru sannan ya ce, "ina neman alfarmarka Muhammadu akan ka yi haƙuri ka bar muna ita anan zuwa wani ɗan lokaci, Insha ALLAHu zamu fahimtar da ita komi saboda gudun irin wannan matsalar da ta faru ta sake faruwa"
Kirjin Safwan ya buga dirim! dim! Cikin firgici yace, "don ALLAH ka yi haƙuri in tafi da ita Baffah, saboda WALLAHi idan ban koma da ita ba akwai matsala, saboda yanzu haka Hajiya fushi take yi da ni sosai akan zuwan da Khadija ta yi, kuma ta sanar da ni cewa muddin ban dawo ƙafata ƙafarta ba to kada ma in koma gidan, gashi ina son in koma makaranta saboda saura shekara ɗaya in kammala karatuna"
Baffah ya yiwa Inna wani kallon neman shawara ta ɗaga masa kai a fakaice, cikin sauki ya ɗauko hannu sannan ya ce
"To ya yi ai ba komi ALLAH ya nuna muna goben lafiya kuma ya tsare hanya ku je lafiya"
Cike da jin daɗi Safwan ya washe baki ya ce, "Ameen Baffah" Inna ta ce da shi 'ka yi haƙuri ko ruwa bamu baka ba"
Baffah cike da mamakinta yace, "ke fa kika ce da ni ga dalilin da yasa ta gudo to kuma yanzu sai ya zo tafiya da ita kuma muce a barta ta yi kwana biyu?, Ni fa bana son abunda zai sa mutanen nan su ga rashin kyautawarmu, ko dai akwai wani abu bayan wannan ne?"
Cikin damuwa Inna tace, "babu wani abu amman kasani ko yanzu tsugunne bata ƙare ba, matuƙar ta koma ba tare da an fahimtar da ita minene auren ba da abunda ya ƙumsa, saboda ina jin tsoron tace zata sake biyo doguwar hanyar nan ita kaɗai ko don gudun wani abu mara kyau ya sameta"
Baffah ya yi shiru yana nazari sannan yace, "to kuma Hasiya kin yi nazari anan, to ALLAH yasa shi ma idan ya zo ya amince ya bar muna ita ɗin"
Inna tace "ai nuna masa ɓacin ranka zaka yi akan sakacin da ya yi har ta biyo wannan uwar hanyar ita kaɗai"
Baffah ya yi saurin faɗin, "kar fa ki janyo inji kunya wajen surukina?"
Inna tace "ba wani jin kunya hakan da zaka yi shine zai ƙwatowa Dije ƴancinta, saboda gobe ya ji tsoron ƙara yin sakaci da ita har ta biyo hanya ba tare da sananinshi ba"
Tofa Inna uhum da kinsan halin da mijin Dijen yake ciki da ba ki ce haka ba😔
Akafta😉
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*DOMIN JIN DAƊINKU MASOYANA ku natsu tsaf ku ci gaba da kwasar ganima😂😝*
*Lamba ta 50*
Safwan kam firgicin da yake ciki ne yasa ya baje ƙasa cikin kiɗimewa yana ta sambatun kiran sunan Dijen, tare da faɗin
"Ina kika shiga ne don ALLAH ki dawo wallahi ina sonki ke ma kinsani ai"
Har dare ya raba yana ta abu ɗaya zuwa lokacin mutane sun fara taruwa kanshi ana tambayarshi mafari, da dai ya fahimci ya tarawa kanshi ƴan kallo ne ya tashi ya faɗa Motarshi ya nufi gidansu wani ɗan uwansu kuma abokinshi, cike da tsantsar tashin hankali yake yi masa bayanin duk abunda yake faruwa, Abokin nashi ya jinjina abun a ranshi sannan ya ce
"A gaskiya Abokina ka yi kuskure babba yanzu mafita ɗaya ce ka je ka baiwa Hajiyar Haƙuri kafin ka kama hanyar zuwa garinsu yarinyar, saboda jikina yana bani ta yi gida don ta gaji da abunda kake yi mata ne shiyasa ta gudu"
Sannan Safwan ya tuno da wayarshi ya ɗaukota da nufin kiran Hajiyar sai ga kiran Lawi da Kamal ya fi ashirin a wayar, cikin sauri ya kira Lawin da rawar baki yake faɗin
"An ganta?"
Lawi murya mai cike da damuwa yace "WALLAHi ba'a ganta ba ni na fara zargin ko ta yi garinsu"
Safwan ya dafe kanshi cikin wani sabon firgici yace,. "Don Allah Abokina ka roƙar mani Hajiya in dawo gidan in bata haƙuri WALLAHi gobe tun da sassafe zan kama hanyar garinsu Khadija in dawo da ita"
Lawi yace "kayi haƙuri Abokina WALLAHi Hajiya ta shiga damuwa sosai akan ɓatan khadija yanzu haka ma da ƙyar na lallasheta ta daina kuka, ga gidan gaba ɗaya hankalinsu ya tashi madadin farin ciki gida ya koma na jimami"
Safwan a kiɗime ya kashe wayar tare da furta "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un Allahumma la sahla illa maja'altahu sahla, ALLAH ka tsare yarinyar nan a duk inda take, Ubangiji ka bani ƙarfin gwiwar tunkarar wannan mummunar ƙaddara da ta faɗowa rayuwata"
Ya kalli Abokin nashi da jajayen idanuwanshi yace, "bari inje Mubarak banga ta zama ba tunda har nine na janyo komi"
Mubarak cike da tausayinshi yace, "ba dai yanzu kake nufin zaka bi bayanta ba?"
A zafafe ya faɗa motarshi yana faɗin "banga ta zama ba ai kuma matuƙar ba ganin yarinyar nan nayi ba....."
Kiran wayarshi ne ya katse maganar da yake yi cikin sauri ya ɗaga saboda ganin numbar Hajiyarshi ce, kafin ma yayi magana yaji muryarta cikin muryar kuka tace
"WALLAHi matuƙar baka dawo man da yarinyata ba to kada ka kuskura ka tako ƙafarka cikin gidan nan"
Cikin rawar murya yace, "ki bini da addu'ar tsari kawai Hajiyata, nayi maki alkƙawali bazaki ganni ba sai tare da Khadija insha ALLAHu"
Kittt! Hajiyar ta kashe wayar saboda wani kukan tausayin kansu da ya kamata, Surayya dake ta bata haƙuri ta yi saurin faɗin
"Don girman ALLAH Hajiyarmu ki yi haƙuri Insha ALLAHu ba abunda zai sami Khadijah ALLAH zai kareta a duk inda take"
Hajiya ta miƙe ta nufi toilet Surayya da Fiddo da yayyensu biyu mata da wasu ƴanuwasu da ke ɗakin suka bita da kallon tausayi, saboda yanda ta ɗaga hankalinta sosai akan rashin ganin Dijen, kowa sai faɗin albarkacin bakinshi yake yi akan lamarin.
Wannan shine abunda ya faru kafin Hajiya ta kira garinsu Dijen ta ji labarin cewa tana cen, don ko shi Safwan ɗin yana kan hanyarshi ne ya sami labarin cewa tana garinsu a bakin Surayya, saboda ƙoƙarinta na son rage masa damuwar da yake ciki.
Ranar yinin bikin Surayyar ma bikin ba wani armashi saboda damuwar da uwar bikin take ciki, haka aka tattara aka kai Surayya ɗakin Mijinta ita kanta zuciyarta ba daɗi saboda halin damuwar da ta baro Hajiyarsu a ciki.
Safwan kam sai da ya ganshi a babban birnin su Dijen sannan hankalinshi ya fara daidaito, ya yi masauki anan sannan ya kimtsa sosai cikin shiga ta alfarma ya buga Motarshi ya nufi ƙauyensu Dijen, zuciyarshi cike da jin daɗin matsalarshi ta zo ƙarshe, saboda fushin da Hajiyar take yi da shi ya fi komi ɗaga masa hankali fiye da duk wani hali da yake ciki.
Dije kam kasancewar daga ita sai kayan jikinta ta shigo garin, Inna ta ɗauki turminta biyu ta baiwa Usmanu tace ya kai babban birninsu inda aka yi wa Hansai ɗinkinta na aure ayowa Dijen ɗinkin Express saboda mijinta yana kan hanya, ya karɓa ya tafi yana dariyar yanda Inna take son farantawa surukinta.
Da marece sakaliya Usmanu ya dawo da ɗinkunan Inna ta karɓa tana ta murna Dije kam iyakacinta ido, don gaba ɗaya jin take yi zama gidan ya gundureta saboda jin da ta yi ance Safwan yana kan hanyar zuwa garin.
Kasancewar shagar dare ya yiwa garinsu Dijen shiyasa da yawa mutane basu san da zuwan nashi ba, cike da jin daɗi ya yi parking ƙofar gidan ya fito yana baza babbar riga sai tashin ƙamshi yake yi.
Jin ƙarar ajiye motar yasa Usmanu saurin fitowa saboda daman cen kowa da tsumayin zuwan nashi yake a gidan, bayan sun yi musabaha ne Usmanu ya ce da shi ya shigo, Safwan ya biyo bayanshi zuciyarshi sai dakan lugude take yi saboda tsoron kada Dijen ta bashi kunya a gaban surukan nashi, da sallamarshi a baki ya shiga Baffah da Inna baki har kunne suke amsa masa sallamar, Dije da ke ɗaki tana gunguni tun daga cen ta ji yo ƙamshin turarenshi, ta yi saurin duƙunkunewa kan gadon har da su lulluɓewa duk da gayun da Inna tasata ta yi na tarbon Safwan ɗin.
Safwan cikin ladabi da jin nauyinsu ya rusuna yana gayar dasu, inda suma ɗin suke amsawa cikin mutunta juna da karamci irin na surukantaka, bayan an ƙare gaishe gaishen ne Safwan ya ɗan muskuta tare da ƙara sunne kanshi yace
"Don ALLAH ayi haƙuri da zuwan da Khadija ta yi WALLAHi bansan da zuwan na ta ba a yafe mani don ALLAH"
Dije daga cen ɗaki jin abinda ya faɗa yasa ta yi zumbur ta fito tana huci tace
"Ba kai kace......."
"Kul!" Katon kashedin da Inna ta yi mata kenan wanda ya sata yin shiru ba shiri, ta yi saurin komawa ɗakin tare da fashewa da kuka tana faɗin
"Shikenan Ni komi na yi bani da gaskiya ai"
Baffah ya kalli Safwan da kyau yace, "ka yi haƙuri da halinta don ALLAH don alamu duk sun nuna ba ƙaramin surutu take sakaku ba, don ko wannan zuwan da ta yi hakan ya tabbatar mani da cewa har yanzu bata san minene auren ba, ina mai ƙara baka haƙuri akan shirmen da take yi maku don ALLAH ku ƙara haƙuri da ita, insha ALLAHu da sannu komi zai daidaita har ma ku yi alfahari da zamanta cikinku"
Safwan ya duƙe kai yana murmushi yace, "ba komi Baffah insha ALLAHU ma komi ya wuce daga yanzu, saboda gobe idan ALLAH ya kaimu lafiya nike son mu koma tare da ita"
Baffah ya yi shiru sannan ya ce, "ina neman alfarmarka Muhammadu akan ka yi haƙuri ka bar muna ita anan zuwa wani ɗan lokaci, Insha ALLAHu zamu fahimtar da ita komi saboda gudun irin wannan matsalar da ta faru ta sake faruwa"
Kirjin Safwan ya buga dirim! dim! Cikin firgici yace, "don ALLAH ka yi haƙuri in tafi da ita Baffah, saboda WALLAHi idan ban koma da ita ba akwai matsala, saboda yanzu haka Hajiya fushi take yi da ni sosai akan zuwan da Khadija ta yi, kuma ta sanar da ni cewa muddin ban dawo ƙafata ƙafarta ba to kada ma in koma gidan, gashi ina son in koma makaranta saboda saura shekara ɗaya in kammala karatuna"
Baffah ya yiwa Inna wani kallon neman shawara ta ɗaga masa kai a fakaice, cikin sauki ya ɗauko hannu sannan ya ce
"To ya yi ai ba komi ALLAH ya nuna muna goben lafiya kuma ya tsare hanya ku je lafiya"
Cike da jin daɗi Safwan ya washe baki ya ce, "Ameen Baffah" Inna ta ce da shi 'ka yi haƙuri ko ruwa bamu baka ba"