← Book details Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 84

Sashe 74

Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cike da jin daɗi ta fara cin wani dambun nama tana ci tana kaɗa kai alamun ya yi daɗi sosai, hannunshi riƙe da plate ɗin tana ci yana yi mata dariya, bayan ta ci abunda zata iya ci ne ya bata magani ta sha sannan ya je ya taimaka mata ta yi wanka, wanda ko shi ɗin sai da suka ɓata lokaci sosai sunata wasarsu ta ma'aurata, tare suka yi wankan suka fito sannan suka shirya cikin taimakekeniyar juna, kafin ka ce me sai ga su dukansu sun fito shar! Abunsu kowane sai tashin ƙamshi yake yi, duk da ta yi rama amman hakan bai hana kwalliyar ta yi kyau ba, don kuwa fatarta ta washe sosai ta yi haske dai dai jikinta, haka ma ta ƙara yin kyau masha ALLAH dukiyar fulaninta sun ƙara cikowa sosai a ƙirjinta, waɗanda a kullum baya gajiya da lalacewa akansu yana santin yanda suke ta ƙara hawa tamkar an hura masu iska ga taushi tamkar balombalom, dole ba don ta so ba take sakin jiki ta barshi ya yi abunda yake so don duk da ciyon ta wannan ɓangaren baya ɗaga ƙafa, a cewarshi wai duk wani maganin da zata sha bai kai wannan tasiri a jikinta ba, da wayo da lallami yake samun abunnda yake ƙulafuci, don idan ma ta ce zata yi tirjiya ma ba haƙura zai yi ba shiyasa take ta danne zuciyarta tana faranta masa, amman ita sam bata son damuwa a wannan lokacin da zai barta na tsawon watanni da tafi sha'awar hakan fiye da yanda yake manne mata akan biyan buƙatarshi.

Bayan sun gama kimtsa komi da ko'ina ne Safwan ya kawo falo ya ce ta zauna ta jirashi minti biyar kacal zai je ya tarbo baƙinshi ya dawo, aikuwa cike da mamakin da son ganin waɗanni baƙi ne haka?, Ta zauna tare da su Surayya suna kallo a falo suna fira jefi jefi, don ko ita ya ja kunnenta sosai akan kada ta sanarwa da Dijen zuwansu Baffahn ya fi so ta gansu unexpected, ai kuwa suna nan suka ji saukar motoci, Surayya ta yi tsalle ta kalleta ta ce

"Yau fa manyan baƙi ne da mu a garin namu"

Dije ta yi wata dariya tare da cewa "ai kam ga shi na ga alama don ko mu mun sheda da waɗannan manyan baƙi"

Surayya ta nufi hanyar fitq falon da sauri tana murna duk da itama cikin ne a jikinta, Dije ta bi ta da kallo ta ce

"Aunty Surayya dai ba'a girma ba har yanzu, da cikinki kike wannan uban rawar jikin ki je ki janyo muna jidali muna zaman zamanmu"

Surayya ta ɗaga murya kafin ta ƙarasa ficewa ta ce "ai sawun Giwa ya take na raƙumi wannan abun murnar dole ne mu nuna farin cikinmu"

Dije haka kawai ta ji ta kasa ɗauke idonta a ƙofar da ake shigowa falon, saboda jinta da take yi cikin ɗokin ganin su wanene waɗannan baƙin, ai kuwa sai ga Surayya riƙe da Abba yaron Usmanu wanda aka yiwa Baffah takwara da shi, cike da mamaki ta zaro ido cen sai ga Hansai bayan Surry, a zabure ta miƙe Baki a sake zata yi magana kenan ta hango Inna a bayan Hansai, aiko ba shiri ta fasa wata uwar kuwwa ta nufosu aguje tana kururuwa sai ga Baffah ta hango da Usmanu tare da Habibynta, cike da tsantsar mamaki ta dinga rufe ido tana budewa tare da murzasu tana faɗin

"Wayyo ALLAHna shin mafalki nike yi ko gaske?"

Hansai ta riƙo hannunta cike da jin daɗin ganinta ta ce

"Ido buɗe ne mune muka kawo maku ziyara"

Dije ta ruƙunƙumeta tana murna ta saketa ta nufi Inna ta faɗa jikinta tana ihun jin daɗi, ta saki Inna ta zo gaban Baffahnta ta riƙo hannunshi tana faɗin

"Ashe ko da gaske kai ne Baffahnah wayyo daɗi kasheni Ni Dije"

Usmanu ya hararota ya ce "ashe dai har yanzu da sauran hankalin?"

Tana dariya ta saki Baffah ta ce

"Yaya Usmanu ya zu fa na girma kai ma ka sani ai"

Surayya ta kai su Inna har falon sannan ta dawo ta ce da su Baffahn su shigo a gaisa kafin a kaisu muhallin da aka tanadar masu, Safwan dai tsaye kawai yake hannunshi a aljihu yana kallon Matarshi wadda ita har kullum bata gajiya da abun dariya, haka ma shagwaɓarta da wautarta suke ƙara dulmiyashi cikin ƙaunarta, waɗanda a cen inda aka fito yake ganin shirmenta amman sai ga shi yanzu sun yi masa rana, don kuwa salon ba ƙaramin burgeshi yake yi ba.

Bayan sun zazzauna ne aka sake sabuwar gaisuwa Dije baki yaƙi rufuwa saboda murna, Hansai kam sai yi take yi tana satar kallon falon saboda ganin tamkar ba a duniya take ba, don ko ita kanta Inna ta jinjina irin wannan daula da Dijenta ta ke ciki, shi kam Baffah ba ma maganarshi ake yi ba don sai hamdala yake yi cikin zucinshi akan wannan ni'ima da Allah ya wadata Dijenshi da ita.

Bayan an ƙare gaiigasawa ne Dukansu aka kaishi masaukinshi, Inna da Hansai aka kaisu wani ɗakin baki da ke cikin sashen Dijen, Baffah da Usmanu kam takanas Safwan ya yi masu jagora zuwa ɓangarenshi, inda aka kaisu wani ɗakin alfarma da aka haɗashi tamkar ɗakin wasu sarakuna don kuwa ya sha ado ta ko'ina sai ƙamari ke ta shi.

Sannan aka kawo masu abincinsu da aka tanadar masu kala kala, bayan sunyi Sallah ne suka fara lodawa cikinsu suna jinjina irin wannan uwar gara da aka tanada donsu kawai, Usmanu ya buɗe ƙafafuwa sai jan girki yake yi yana faɗin

"Ashe Baffah shiyasa kake ta farin ciki saboda kasan inda ka kawo ƴarka?, To Wallahi a ja kunnenta duk tsanani ta ci gaba da yi masa biyayya, don ko watarana ta yi masa shirme ya kaita ƙofar gida ya ce ya ce ta fi gida, to ta ce masa ita ba inda zata je don taga wurin zama, yana kaita tana dawowa har sai ya gaji don kanshi ya haƙura ya ƙyaleta"

Baffah nama cike da bakinshi ya ce "ba ma zata aika shirmen ba bale har akaita ƙofar gidan, don haka ka godewa ALLAH ka godewa Dijengalata don sanadinta ne kake cin wannan naman"

Haka suka dinga firarsu da suka saba cikin raha da tsantsar farin ciki da jin daɗin ganin Dijensu ta yi dacen aure.

Inna Kam da Hansai su ma suna inda aka saukesu Hansai tare da yaronta sai jan gara suke yi Inna kam cike da jin nauyi take tsakura abincin, Dije tana kallonta cike da jin daɗi ta ce

"Inna ki saki jikinki don ALLAH ki ci abincinki, ba fa kowa daga Ni sai ku ko Surayya ta barku ku ji daɗin cin abincinku cikin nutsuwa"

Inna ta maka mata harara tace "don ma kin ci sa'a na zo? Ba yanda banyi da Baffah'nki da Mijinki ba akan a barni ba sai na zo ba suka ce dole da ni za'a yi tafiyar, Ni ban saba da wannan rashin kunyar ba ta ƴan zamani, zuwa gidan Suruki har da zube ɗuwawu a cenye abincin Suruki, kai Ni Hasiya wannan zamani ina zaka da mu? Kin ga Inna Tumba har ALLAH ya yi mata rasuwa bata taɓa tako ƙafarta ɗakina ba" cewa da Mahaifiyarta da ta haifeta ma'ana kakar Dijen.

Dije tana dariya ta ce

"Cabɗi to ai Ni Inna duk wanda ma zai auri ɗiyana dole ne ma ya yi man nawa ɗakin a gidanshi yanda ya yiwa Mahaifiyarshi"

Inna da Hansai suka zaro ido, Dije ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "ALLAH kuwa zama zan yi yanda ta zauna idan aka muzgunawa ƴata in fito mu raba gari Ni da Uwarshi WALLAhi"

Inna ta ce "laaa! Na ga aya ashe Dijen har yanzu ba ta yi hankali ba, to ai sai ki janyo a tattaroki tare da ƴar a watsoku waje da kayanku kusan na yi WALLAhi"

Dije da Hansai suka dinga dariya Surayya ta shigo da wasu sauran kulolin itama ta zauna aka ci gaba da firar da ita anata dariya.

Da ƙyar suka ciyo kan Inna ta ci abincin sai dai ta ƙi cin sauran abubuwan a gaban Surayya da Hansai, saboda surukutar da ke tsakaninsu, ganin haka yasa Dijen ta ja Hansai ɗakinta suka bar Inna nan ita kaɗai sannan ta cisgi garar itama cikin ɗar! ɗar! don kada a risketa bata sani ba.

****

Zee kam a ranar bata kwana gidansu ba don kuwa Baaba Asabe ta kwasheta da kayanta suka nufi gidanta, suna shiga tashin farko ta ce da ita

"Bani wayarki"

Zee ta ce "ai Ni tun ranar da na bar gidan ban sake ganinta da idona ba, tana cen Yola a falona ban sani ba ko ya ɗauke mani ko kuma ma an sace oho"

Baabaah Asabe haɗe da fuska ta ce "to je ki kai kayanki ɗakinsu Inna Dela ki dawo ki ji"

ZEE ta zaro Ido waje ta ce "Inna Dela fa kika ce Gwaggo?"

Kai tsaye ta ce "eh ita nace ko a cikin halittar jikinki akwai abunda su babu irinsu jikinsu?? "

Zee ta girgiza kai tare da sosa kai murya ƙasa ƙasa ta ce "ƴan aiki ne fa Gwaggo, Ni dai don ALLAH ki barni ko ɗakin waje ne zan zauna amman ba ɗakinsu Dela ba"

Baabaah Asabe ta katsa mata wata arniyar tsawa ta ce "za ki je ki kai kayan ko sai na haɗaki da buloli yanzu?"

Zee ta zabura aguje ta nufi inda ɗakin na ma'aikatan gidan yake saboda tsabar tsoron Baabaah Asaben da take yi, tana tafe tana gunguni Baabaah Asabe ta ɗaga murya ta ce
Chapter 74 · 0% Book details