Sashe 73
Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khadeeja Candy* SARAC STARS. C - Pen... Page 3 Ta sauke wayar tana murmushi wani irin jindadi da farinciki suka lullube ta na jin muryar Aliyu, daman tana ta tunanin ta ina zata bullo ta fara gaisawa da shi babu dama, domin a yanayin yadda ta fahimce shi ba irin mazan da mata suke saurin burgewa ba ne, kuma ba irin mazan da ake zuwa ma da bukata kai tsaye ne ba, kusan zuwan Kameela gurinta ya taimaka mata sosai gurin samun damar magana da Aliyu tun a bayan da ta sace Numbersa a wayar Emily. Ta dade tana murmushi kamin murmushin dake fuskarta ya gushe kamar mai tunanin wani abu, ta goge number a gurin kira sannan ta fito bandaki da aje wayar a karamin gadonta ta fito falo ta samu Kameela da ta ci kuka har idonta ya canja kala. "Toh ke yanzu miye amfanin kukan da kike yi?" "Ba zaki gane ba, baki san minene soba Tasmia ba" Tasmia ta zauna kusa da ita ta dafa ta With Straight face. "Na san miye so, so yana iya haukata mutum domin yana saka ka ka aikata abun da ba halinka ko kuma baka yi niya ba, so yana maida kai kamar wani wawa ko kuma kakkarfa, shi so wani abu ne da ba a iya cusa shi sau daya yake shiga zuciyar mutum, kuma ya hanaka zaman lafiya har sai ka biya bukatarsa" Ta lumshe ido ta bude. "Amman ke irin son da kike yi ma Aliyu yayi tawa Kameela shi ya kamata ace yana miki irin wannan son, ke fa mace ce, gashi yanzu har yana kokarin wulakantaki akan wata banza da addininmu ma ba daya ba, ba tare da kin masa komai ba" "Ban masa komai ba sai kawai dan na zagi Emily, yanzu haka baya gidan yayi tafiyarsa, kuma yace na bar masa gidansa na koma gida wai zai samu likitan da zai duba ni, mahaukaciya ma ya dauke ni kenan, shiyasa na rasa me ke min dadi naji bana son zaman gidan gashi ba ni da kowa a garin nan" Tasmia ta bude baki. "Ahhh lallai kuwa mahaukaciya ya dauke ki, amman kin yi hakuri nuna masa kishi da kike ai soyayya ce, shi duk be gani ba sai kora da hali? Da ni ce ke ba zan sake kwana a gidansa ba sai na koya masa darasi" Kameela ta kalleta. "Ni ba inda zan je ina son mijina Wallahi, idan na tafi ai na bawa Emily din damar ta rika magana da shi tana samun yadda take so gashi ma gurin aikinsu daya" Tasmia ta girma mata kai. "Kameela ke fa yar manyan mutane ce, kina da gata ina da yan'uwa da kudi, be kamata Aliyu ya wulakanta kuma ki zauna ba, ai tun da har ta kai ya furta ki koma gida idan baki koma ba ai zai cigaba da wulakanta ki ne, ai kawai ki yanki ticket gobe ki kama hanyar gidanku sai ya nemi ki, ai ba ayi ma namiji haka, tun da har ya iya nuna wata ta fiki kara ya san darajarki" "Akwai abun da baki sani ba Tasmia, iyayenmu ba san auren za su iya raba auren idan suka ji cewar Aliyu ya kore ni saboda na kira wata a gurin aikinsu na zageta saboda tana budurwarsa" Tasmia ta daka mata tsawa. "Ke dalla can Aliyu autan maza ne da kike ta wannan rawan jiki da tsoron rasa shi? Haba Kameela sai kace maza sun kare aduniyar nan ne" "Tasmia Aliyu na dabam ne fa, cikin maza dari irinsa daya ake samu, ni na san yana hakuri da ni, yana min komai kuma be taba wulakanta ni irin haka ba sai da bakar Emilyn nan ta zo" Tasmia ta shiru tana kara jin kalamanta cewar Aliyu na dabam. "Toh yanzu ko number shi zaki ba ni na kira na ba shi hakuri? Domin na lura baki shirya tafiya gida ba, kin shirya karbar wulakancinsa ne, daman maza ai idan suna son ka babu abun da ba za su maka ba, idan kuma suka ki ka zaka fara ganin wulakanci kala kala" "Tasmia ko hauka nake dai ai ba zan dauki number wayar mijina da kaina na ba ki ba, tafiya gida dai zan tafi ko dan ya gane ni ba kanwar lasa ba ce" Tasmia ta watsa mata harara. "Kin dauka kowa irin Emily ne? Ko mazan duniya sun kare an fada miki ni zan iya auren mijin da zai nuna ya fi son matar waje da matarsa?" Kameela ta watsa mata wani kallo tana jin zafin kalaminta. "Mijina ba manemin mata ba ne, balle ki ce ya fi son matar waje akan ta gida" "Idan ba haka ba akan me zai fifita Emily take da suna ko Imily akan ki? Ke mai dai ki yi tunani mana" Kameela ta nuna ta da yatsa. "Ke ki iya bakinki, ban zan dan bana son mijina ba, sai dan na rasa gurin da zanje a cikin daren nan, tun da na zo na fada miki damuwata sai wani zuga ni kike kina zagin mijina, an fada miki rabuwa muka yi ne? Ni fa na zo nan ne saboda na samu mafitar yadda zan shirya da mijina, amman sai wani zakewa kike kina ta zaginsa" Tasmia ta yi murmushi. "Matsala ta dake ke zahila ce, idan yabon Aliyu kike son ayi ai nan zaki zo ba, dan ni na san darajar kaina ba zan baki shawarar zama da mutum da har yanzu baki gama sanin ba, Aliyu yana neman hanyar rabuwa da ke ne kawai shiyasa yake wulakantaki domin ba Emily ce kadai budurwarsa ba" Tasmia ta karasa fuskarta babu alamar wasa. "Me kike nufi?" Har Tasmia ta daga wayar sai kuma ta fasa abun da ta yi niya ta dauke kai. "Ki daina yarda da namiji dai kawai" "Ai ke baki yi auren ba balle ki fada min kabli da bad'adin namiji" Fadar bata yi aure Tasmia ta ji abun kamar gorin auren take mata a take zuciyarta ta haye sama san lokacin da ta mayar mata da zazzafar amsa ba. "Kara ni ban yi auren ba, ke da kika yi auren ai ta wuje ta fiki daraja a gurin mijinki, mijin ma da Emily kadai yake nema ba ni kaina da kansa ya saka min Number wayarsa, kuma idan kin koma ki tambaye shi sau nawa ya zo gidan nan gurina" "Karya kike yi Wallahi ai ko Aliyu zai kula mata ba irinki zai kula ba, domin ba ki fini da komai ba, sai idan ke kika nemi shiga gurinsa saboda an yi kwantai babu miji kuma ga bakin jini, ga kuma rashin tarbiya, idan ba rashin tarbiya ba yaushe mace cikakkiya rikakkiya kamar ke zata zo ta kama gidan kanta set-contain da sunan bautar kasa? Duk garin Kaduna be ishe ki zama ba sai kin tsallako kin zo garin da mijina yake saboda shi ne abun farautarki ko?" Ta dago wayar ta kama Number Aliyu ta kira shi na farko be daga ba sai a na biyu. "Assalamu Alaikum" Ya fada Tasmia bata ce komai ba ta katse kiran daman burinta Kameela ta ji muryarsa domin ta gasgata karyarta. "Komai zaki fada ki fada ni dai na riga na gama da ke Wallahi" Kameela ta rufe ta duka Tasmia ta maida himma suka fara dukan dukan gashi babu mai raba su, ta ko'ina Kameela dukan Tasmia take ba kuma dan ta fi Tasmia karfi ko jiki ba halima Tasmia ta fita cika amman ta yi mata kwance galala tana dukanta, da ta gama da ita ta koma gurin kayan falon ta fara watse su. "Wallahi Wallahi akan Mijina sai na kashe ki Tasmia, daga ke har Emily sai na yi maganinku" Ta Dauki Jakarta ta fice daga gidan tana huci. Sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta samu abun hawa ta hau ta koma gida, tana shiga ta fadi kan kujerarta ta fashe da kuka bakinciki ya mata yawa, yanzu mayakan sun zame mata biyu kuma ba kowa ya janyo ba sai Aliyu, ta san wani abun da Tasmia ta fada gaskiya ne cewar yana neman rabuwa da ita ne shiyasa yanzu yake wulakanta ta, a yanzu ta gano dalilinsa na yi mata alkawarin ba zai kara aure ba ashe saboda yana son ya tara mata awaje ne, gashi daga tafiyarta haihuwa komai ya canja kamar daman dagawarta kawai yake jira, a daren ta siye flight ticket daga PH to Lagos daga Lagos ta hau jirgin Kaduna kwana ta yi tana kuka tana bakincikin da nadamar dama ace ta bar shi ya ci abincin dazun da yanzu duk bata ji wannan ba. EMILY POV. Kanta a sama tana kallon taurarin da suka yi ma samaniya ido, har lokacin hakoranta ba su rufu daga dariyar da take na wayar da ta yi da Aliyu ba, bata sauke kanta kasa ba sai da mai gadin gidanta ya bude gate motar Vito ta kunno kai a harabar gidan, tana kallonsa har yayi farkin sannan ta sauka ta karasa inda motarsa take, ya bude motar ya fito yana mata wani irin kauna da ke kara tabbatarwar kaunarta a zuciyarsa musamman data nuna masa kulawa da tsoronta na gudun kar wani abu ya same shi. "How are you?" "I'm good, ba su maka komai ba" "Ba su yi ba, kuma ba su samu komai ba" "Taya hakan ta faru" "Saboda cikin kasa nake aje abun da yake dole a gidan, kuma ina da yaran da suke hango abun da zai faru idan suka ga bakuwar fuska sai su shirya komai" Ta yi murmushi. "Na jidadi da wani abu be sameka ba" "Daman babu abun da zai same ni ai, sai dai ya samu wanda ya shirya hakan" Ya wuce ya nufi Gardenta gurin da ya binne bindigarsa sai ta bi bayansa da tambaya. "Ka gano ko waye ne" "Ban gano ba amman zan gano, kuma idan na gane kowaye sai ya dandani kudarsa, sai ya raina kansa" Har yayi ginar ya ciro bindigarsa bata sake cewa komai ba, mikewa yayi tsaye ya matsa kusa da ita. "Kin damu da ni Emily ko ba haka ba?" Ta yi shiru bata amsa masa ba. "Miya haka ki aurena? Mi ya rike ki