Sashe 105
Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khadeeja Candy* Page 4 Ammy ta nufo ta cike da rawa jiki Emily kuma bata fasa dosar kofar ba har sai da ta ita da Ammy suka yi kicibus a falon, Ammy ta kai hannu zata taba Emily sai Emily ta matsa baya. "Yata Aisha muna ta nemanki ina kika shiga? Ke ce haka? Ina Ibraheem?" "Aisha ta dade da mutuwa..." Emily ta fada, Turhan ya juyo da sauri daman zuciyarsa bata gama gamsuwa cewar wannan din Aishar da yake nema ba ce domin ta canja gaba daya. "Aisha ta mutu tun a ranar da kika yi son zuciya kika aurawa mugun danki ita, wannan Emily ce ina yata?" Ammy ta kalli Turhan idonta na cika da hawaye sannan ta kalli Emily tace. "Aisha ki yi hakuri.. Wallahi..." "Ba maganarku na zo ji a nan ba, ina yata take?" "Tana nan lafiya, Aisha dan Allah ki saurare ni mu yi magana, na san kina cikin bakinciki amman yadda zuciyarki take raya ba haka ba ne" "Where is my baby? Bani da wata alaka da ku, and bana cikin bakinciki ni baki gan ni ba? Na wuce yadda kuke tunani, ina yata take?" "Tana gidana dan Allah Aisha ki saurare ni mu yi magana, tsawon shekara shida kenan muma nemanki, ba ni da lafiya amman da na ga sanadin ganinki sai na ji na warke, daman ciwon har da ke ne" Emily ta tabe baki. "A tsawon shekarun nan Ammy kike tunanin zan sake yarda da shirinki ne? Kin yi amfani da kyautatawarki kika cutar da ni yanzu kuma kina tunanin amfani da ciwonki zai saka na yarda ke sake cutar da ni ne?" "Wallahi ban yi dan na cutar da ke ba! Duk wani abu da Turhan yayi miki ban san zai miki ba, ban san haka zai faru ba, ki fahimce ni mana wannan duk ba halinki ba ne waye hore miki kunne haka?" Ammy na maganar cikin kuka domin gaba daya Aisha ta canja mata tun daga shigarta har kalamanta da kamaninta sun sauya. "Ni da na zauna da kazakin mutum kamar wacan har jira nake wani ya hore min kunne" "Kina cikin fushi ne kawai har yanzu, da zaki yi hakuri ki bi ni gida zamu karshe duk wannan" "Har abada ni da gidanki, ba ni ba wata alaka da ke" Turhan ya karaso gurin yana jin ransa na baci saboda kalaman da take furtawa ga Ammy. "Aisha da ni kike da matsala ba da Ammy ba, wannan...." Be karasa ba ta dauke shi mari, Ammy ta rufe baki Turhan kuma ya runtse ido ya bude ya kalleta idonsa har suna canja kala. "Har yanzu haukarka na baka zaka iya kiran sunana? How dare you? How dare you zaka tsaya a gabana har ka ambaci sunana? A tunaninka har yanzu wacan yarinyar ce da ka maida baiwa a bakar masarautarku? Ka fadawa kowa kurma ce? Ka hana ta magana? Hadiman matarka suke dokanta? Matar da aka sadakar a matsayin baiwa ga wasu mutanen? Ai Abun kunya ne aji kana nemanta, ko da yake mutane irinka ba su da kunya" "Aish..." Yana sake bude baki ta sake dauke shi da mari. Sannan ta kalli Ammy ta ce "Ina yata take?" "Tana nan lafiya ki yi hakuri ko dan ita ki saurara ni" "Baki da wannan matsayin Ammy, kin rusa wacan kallon da nake miki, saboda kin nade bakin maciji a farin kyale kika damka min, saboda na yarda da ke kuma ya tsare ni, ban mutu ba sai dai wani abu da ya alakance ki da zuri'arki ya mutu tun a wacan ranar, baki da wannan kimar a ido na yanzu, saboda haka ina Yata take?" "Aish..." Turhan na bude baki zai furta sunanta Emily ta sake juyowa ta dauke shi da wani mahaukacin mari sai da ya nisa "Ahhhh" Ya cije hakora ji yake kamar ya rama amman ya kasa. "Huhmmm Aliyu yana ba ni mamaki, indai Har zai iya boye min inda kike da kuma alakata Fatima to zai iya komai" Yayi furucin da yakinin shirya mata komai aka yi aka hure mata kunne domin sanin da yayi ma Emily ba zata iya tsayawa tana fada masa magana haka ba, amman gashi har da mari, kuma ya san ba kowa zai yi haka ba sai Aliyu mutumen da ya dauka a matsayin aboki ashe makiyinsa ne be sani ba. "Kana nemana saboda ka maida ni masarautarku na cigaba da bautawa matarka? Idan akana akwai wata alaka ta nesa ko ta kusa tsakaninka da Fatima to hauka kake yi" Ta nufi kofa zata fice Ammy ta riko jacket din Dr A-B dake hannun Emily tana rokonta. "Ina zaki je? Aisha dan Allah ki saurare ni ko dan shekaruna?" Emily ta tsaya kamar abun arziki ta juyo. "Danki ya kamata ki fadawa wannan, shi ya kamata ya fi kowa sanin daraja da kimarki ya kyautata miki ya ri e amanarki, shi be yi ba sai ni da ban hada komai da ke ba?" Ammy ta girgiza kai. "Wannan ba Aisha da na sani ba ce" "Wacan Aishar da kika sani ai ita kika aurawa mutumen da ya tsoratata tun gabanin a daura masa aure da ita, mutumen da ya gargadeta kar ta yarda ta aure shi, ita kuma a kokarinta na maida alheri da alheri ta danna komai ta aureshi, wacan Aisha itace Aishar da ya tofawa yawu a fuska a ranar da aka daura aurensu, ita ce ya kira ranar da aka dauranta da shi a matsayin bakar rana a gurinsa, ita ce macen da ya maida baiwa ya masarautarsu, take bautawa matarsa, ita ce ya gabatar a matsayin kurma a masarautarsu kuma ya cilasta mata amsa haka, wannan kuma Emily ce ta sha banban da wacan" Ta fisge rigar ta fice abunta, Ammy ta kafe idonta akan danta cikin wani kalar yanayi na bakinciki da takaici, matsawa yayi kusa da ita kamar zai mata bayani amman ya kasa cewa komai sai motsa baki yake. "Da gaske ne abun data fada?" Yayi shiru kamar ba zai amsa ba. "Duk abun da ya faru Ammy kuskure ne" Tasssss Ammy ta wanke shi da mari, hawaye na sauko mata. "Allah ya wandaranka, wace irin zuciya ce a kirjinka? Ba ni da Martaba da zaka mutunta ni ashe? Ashe karyar biyayya kake min? Bayan idona ka aikata abun da zai zubar da kimata? Ka rusa duk wani mafarkina da buri da nake da shi, ban taba tambayar wace kalar zamantakewa kuka yi ba amman raina be taba kawo min irin wannan kazamar rayuwar ba, kalli wuyanta ka gani sarkar cross ce a jiki, ka kalli shigarta ta tashi daga musulunci ta koma kafirci, Allah ya biyaka na gode" Gaba daya jikin Turhan yayi sanyi duk neman Emily da yake saboda Ammy ne, ba dan yana jin be kyauta mata ba, amman a yau ya dan ji wani iri. "Zan gyara komai Ammy na miki alkawari, ko dan yar dake tsakaninmu, kuma na faranta miki" Ammy bata ce masa komai ba ta juya ta fice daga falon ta fita ta shiga motar da aka kawo ta, direban ya juya da ita, Turhan na tsaye a entrance yana kallon motar har suka fice sannan ya juya ya kalli kofar falon yana jin kamar ya bankawa gidan wuta domin a yanzu ba shi da babban makiyi kamar Aliyu. "Ina zata je?" Wata zuciyar ta tambaye shi, sai ya sauka entrance din ya bude mota da sauri ya shiga yayi reverse ya fice yana ta kalle kalle zuciyarsa na raya masa wata kila ta tafi ta samu Aliyu wani gurin ne gashi be san inda zai ganshi ko ita ba. Haka ya bi titi yana tafe yana kalle kalle har Napep idan ya gani lekawa yake duk yake dare ne ba lallai ya ganta ba shi dai ya rike kamanin gashinta da hasken fatarta, kamaninta na baya da a yanzu sun hade masa har yanzu ganin yake kamar ba Aisha da yake nema ba ce ya gani. A hankali yake tuka motar yana bin gefen hanya da kallo idan ya ga napep sai ya mika kai ya leka, idan ya ga mota ma sai kallo yana son tantance motar da Aliyu ya zo da ita gidan domin be rike kamanin motar da kyau ba, yayi tafiya mai nisa har yana shirin juyawa ya koma gidan Ammy saboda wata zuciyar na raya masa wata kila Aliyu ya koma gidan ko kuma ita Emily, sai ya hango mai kama da ita an sauke ta a napep ta shiga wani shago da aka kawata shi da haske, da sauri ya faka can gefe yana kallon shagon. EMILY POV. Tana fita gidan ta samu Napep ta hau ba tare da ta fada masa inda zai kaita ba, kawai ta fada masa su yi ta tafiya, tana zaune a Napep din tana jin kamar ta yi kuka amman ta danne zuciyarta da idonta daga zubar da hawaye, tana jin a yanzu jaruma ya kamata ta zama. Ta ina zata samu yarta shi ne abun da yake damunta a yanzu, ta dayan gefen kuma tana jin tsanar Aliyu a ranta domin shi ne silar faruwar komai, meyasa ma ta yarda da shi tun farko? Gashi yanzu saboda abun da ya aikata har Turhan ya samu damar tsayuwa a gabanta da Ammy su yi magana da ita. "Huhmmm Aliyu yana bani mamaki, indai Har zai iya boye min inda kike da kuma alakata Fatima to zai iya komai" Furucin Turhan na dazun ya fado mata a rai, sai kuma ta tuna yadda yake kokarin fahimtar da ita ba shi ya shirya wannan ba, it could be true amman idan ba shi bane miyasa har yanzu be dawo gareta da Fatima ba? Meyasa be kirata ba? Idan ba haka ba meyasa ya zo da Fatima? Wane irin uzuri ne da ba zai fada mata ba? "Ina zan kaiki Hajiya?" Mai Napep din ya tambaya ganin ana ta tafiya bata ce komai ba. "Ka sauke ni gurin da zan samu mai Pos ba ni da cash" Tayi furucin tana gwada kiran number layi da layin yake hannun Fatima sai ta ji layin a akashe, ta gwada dayan layin na Aliyu da wayar take hannunsa nan ma ta ji wayar a kashe, gaba daya