← Book details Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 177

Sashe 67

Abokin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Khadeeja Candy* SARAC STARS. C - Pen... FOLLOW ME ON FACEBOOK https://www.facebook.com/profile.php?id=100008156177914 TIKTOK https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1 INSTAGRAM https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0 CHANNEL https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01 KHADEEJA CANDY STORE https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08 Page 2 "Sunana Aliyu Aliyu AA Bappa Mudallab, sunan mahaifina Aliyu Mudallab amman ana kiransa da Bappa Mudallab kasancewarsa da na farko a gurin mahaifinsa, mahaifina dan siyasa amman a baya yayi aikin gobnati kamin ya sinci kansa a siyasa, ya fara da commissioner kamin yayi dan majalisar hijar kaduna har sau uku daga baya ya tsallaka zuwa tarayya neman sanata, mahaifina manomi ne sosai, kusan siyasar ta karbe shi ne kawai har yayi suna a ciki, amman abun da ya dogara da shi muma muka jingina, ni kaina na kam taba noman a lokacin damina, mahaifina kuma yana nema a rana da damina da baraza, yana da gonaki da gidajen shanu da ake saffara Madara da Fresh kirdirmo, da manshanu, haka kuma mahaifina yana kiwon fili da kaji. Mahaifiyata kuma mace ce da bata komai sai rainon yayanta uku da Allah ya bata, Ummi bata sana'ar fari balle na baki, mu uku kawai ta haifa Yayana Yusuf, sai kuma ni Aliyu sai kanwarmu da ta zo bayan an fidda rai da samuwarta wato Ramla. Ummi ita kadai ce a gurin Mahaifinmu bayan ita be sake auren wata matarba, kuma har yanzu ba mu taba jin wani abu tsakaninsu ba, ko da yake ita da shi yayan wa da yayan kanwa ne, wato su kansu abokan wasan junansu ne. Yayana samanin tattalin arziki ne, gwararre ne sosai a bangaren Economics shiyasa mahaifinmu ya dauke shi ya damka masa rabin ragamar kasuwanci a yanzu shi yake tafiyar da komai, Mahaifina kuma ya maida hankali gurin Siyasa, ni kuma na karanta Engineering ne wannan ya saka ake yawo da ni gari gari gurin aiki, na zauna a sokoto na yi zama a Kano na zauna a Lagos daga baya aka dawo da ni part hart-cour, tarbiyar gidanmi Alhamdulillah Ummi ta yi kokari da jajircewar Daddynmu, ta bangaren karatun addini duk gidanmu babu rago, ba dan karki ce na yi son kai ba da sai na je na fi kowa kokari ta bangaren Karatu, domin na yi karantar wa a islamiya har uku ba dan a biya ni ba, sai dan na samu ladar kawai, hasali ma ni nake musu ihisani a duk wata, da dare kuma sai na je wata islamiyar maza da ta zama majalisi na karo karatu, a islamiyar ne ma na hadu da matata wadda nake aure a yanzu, Kameela. Dalibata ce mai kokari sosai tana da kaifin basira tana yawan zuwa makaranta even though dai takan taba rashin jin magana sosai a makaranta domin ana yawan kawo min kararta, amman ni ban duba wannan ba, na duba karatunta ne domin ni ina son mace mai addini saboda yayana su samu uwa ta gari, sai dai kamin mu auri junanmu mun sha gwagwarmaya saboda iyayenta bata so na, ni ma kuma Ummi na ba wani gamsuwa ta yi da auren ba kawai dai ta mara min baya ne saboda tana son abun da yayanta suke so, banbanci jam'iya da kuma yin nasara da faduwa ya yi tasiri sosai a gurin iyayenta har ta kai suna kallonmu a matsayin makiyansu, ada abun ya fi haka tsami ma, amman dai auren mu ya saka an yafe wasu abubuwa wasu abubuwan kuma an ba shi baya, a lokacin akwai masu son Kameela ita kuma ni take so, iyayenta kuma Governor da yake Mulkin garin Kaduna a yanzu His Excellency Rilwan Mu'azu Mai Nasara shi suka so ta aura, domin abokin mahaifina ne kuma gashi yana Governor, da ta aure shi ita ce zata zama first Lady domin matarsa bata yi karatu mai surfi da zata iya tsayawa a gaban mutane ta yi turanci ba, amman kishi be bar Kameela ta amince da zabin iyayenta ba, kuma kishi be bari kudi ya rufe mata ido ba. Kameela mace ce mai kishi sosai gaskiya, daga lokacin da na fara soyayya da ita na gano haka, bata bari kowace daliba ta kalle a inda nake karantarwa, tun ina boye alakarmu ina jin kunya sai ga shi ta bayyanawa duniya, yadda take yawan fada da dalibai a makarantar a kaina sai ki dauka ni kadai ne namiji, kuma wasu da yawa ba so na suke ba kawai gaisuwar mutunci ce da girmamawa a matsayina na Malaminsu amman duk bata duba wannan ba, an kai ruwa rana tsakanina da iyayenta da kuma iyayena har ta kai na ce ni na janye daga auren saboda ba zan dauki wulakanci ko raini ba, sai dai damuwar da Kameela ta shiga a lokaci saboda tana tsananin so na ya saka na dawo na yarda zan aureta, amman duk wani hidima da ake ta biki like event ban yi ba sai ta Walima ita ta maza kawai ban da mata, ita ma ta yi nata dabam, amman wani shagalin biki da zai janyo shidai a lamarinmu ban aikata ba, kasancewar ni ba mutum ne mai son bidi'a ba, shekara daya da aurenmu Allah ya ba mu karuwa, amman abun be zo da rai ba, yanzu haka Kameela tana gida gurin wankan amman ta gama tana shirye shiryen dawowa ne, loka cin da kika kira ni naje ganinta ne wayar tana hannunta, kin san mace mai kishi bata iya rike kanta idan ta ji muryar wata macen a wayar mijinta, amman dai na ja mata kunne, wannan shi ne takaitaccen labarina, ina fatar a yanzu hankalinki zai kwanta da Aliyu" Ta yi murmushi sosai ta ji dadin yadda yake tsara mata labarinsa cikin natsuwa da kwanciyar hankali muryar ma kasa kasa kamar mai magana da karamar yarinya. "Ba ki tambayi ya aka yi na san Turhan ba, ko ya aka yi ni da shi muka zama abokan juna" A take murmushin dake fuskarta ya gushe, Aliyu ya saci kallonta kadan. "Kamar na taba fada miki mahaifina yayi rashin nasara har sau uku ko? Sai a na hudu ya samu nasara? Toh a rashin nasararsa ta farko gurin takarar sanata bayan ya fadi zabe sai Shugaban kasa na wacan lokacin ya nada shi ambassador Nigeria to Sudan, a lokacin ne ya tafi har da ni domin Ummi bata yarda yaranta su yi nesa da ita, kusan da mu take shawarar komai da mu take hira kuma Allah ya dora mata son yaya kamar dai yadda kike ji Fatima a yanzu, da muka koma can sai kyakkyawar alaka ta shiga tsakanin Sarkin Sudan na yanzu da kuma mahaifina" Ya mike tsaye ya nufi windows din office din ya bude. "Na manta ban fada miki ba, ni mutum ne mai son wasan tseren doki, wani da wata wasa sai ita a koda yaushe idan na samu free time haka zan hau doki na yi ta zaga gari, idan kuma akwai gurin wasan zan tafi na yi, a Khartoum muke zaune babban birnin kasar sunan a birnin akwai wani babban filin wasa na wasa da dawaki, na kam tafi yin wasa duk Weekend, duk yadda nake da son wasan dokin nan Turhan ya fi ni, kuma ya fini gwanewa domin shi dan sarauta ne ni kuma haye na yi, a duk lokacin da muke je wasa akan shirya tsare tsakanin yayan manya ko yan sarauta, wata rana sai aka hada mu na nuna gwanewa shi kuma ya nuna min ya fi kwarewa akai, da haka dai muka sabu ya zama mun san junanmu idan an shigo za a gaisa, har kai idan na shigo be shigo ba wasan baya dadi ni ma bana shi dadi haka shi ma ta bangarensa. Muka fara following juna da a social media, har ta kai muna gaisawa a waya ko chat, har mukan hadu mu yi hira ko mu tafi wani gurin shakatawa da dawaki. A lokacin Turhan ba shi da ikon shiga Nigeria ba Nigeria kadai ba mahaifinsa be yarda ya bar kasar ba, har ya kan bukaci na ba shi tarihin Nigeria da yadda kasar take, da ya ji cewar daga kaduna na fito sai yake ba ni labarin mahaifiyarsa yar kaduna ce amman baya zuwa gurinta mahaifinsa ya hana shi fita Kasar saboda kar ya tsallaka ya tafi gurinta, amman ita an mata lamuni tana zuwa ganinsa, kuma suna magana da waya, wata rana tsaman sai gashi ta shigo da kokon bararta gurin Mahaifina ta hanyar Ummi, tana son Daddy yayi mata tsaye a bawa Turhan damar ziyararta a duk lokacin da ta so, mahaifina ya sha wahala sai da ya jajirce sannan sarkin ya yarda domin ganin yake kamar Ammy zata karbe masa Turhan ne, kuma su a gurinsu bakar fata ba shi da wata kima, like kamar mahaifin Turhan be so mahaifiyar Turhan ta zama bahaushiya har Nigeria ba, mu kan mu saboda muna yayan manya ne a lokacin ya saka ake daga mana kafa a dole, mahaifina yayi nasarar karya dokar sarkin aka bawa Turhan damar ziyararta kasar a duk lokacin da ya so, saman kuma bayan ni yana da wani amini Munir dan Nigeria ne sosai shi kuma a can yayi karatu a can yayi rayuwa daga baya ya dawo gida, Ummi ta san Turhan, Ammy ma ta san ni ta dalilin abota da kuma abubuwan da suka faru, sai ya zama abotarmu ta kara kwari sosai, kusan rabin hausar da ya iya gurina da Ummi da yaran da Ummi take riko a lokacin ya koya, daman kuma na tarar da shi mahaifiyarsa ta shimfida masa kaunarta da yarenta da rabin al'adarta a zuciyarsa da kansa, amman ma kaunarta Turhan yana son Ammy sosai, daga haka abotarmu ta daure har yau" Ya sauke numfashi a hankali. "Na yi mamaki da na ji kin tsani Turhan har kina gudun ganinsa, domin ban san wani hali mummuna na Turhan ba, shiyasa na kagu na ji wane irin zama kuka yi da shi, taya rayuwarsa ta sauya har ya munana miki haka?" Emily ta kalli hannun Aliyu dake sanye da agogon data dawo masa da shi. "Baka yi tunani ba? Da ace ni yar sarki ce ko kuma balaraba kamar shi ba zai wulakanta ni ba? Farkon abun da Turhan ya fara kushewa a tattare da ni shi ne halittata, kamin ya muzanta tubana, sannan ya kaskanta asalina" Ta yi shiru idonta na cika
Chapter 67 · 0% Book details