← Book details Turken Gida Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 76

Sashe 3

Turken Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hararata ya yi ba tare da ya yi mgana ba, cak ya ɗaga Baby sama. Ni kuma sai na ƙarisa na rumgume Jidda wacce ke faɗin"Ina kwana Umman mu."
Ina shafa kumatunta na ce"Lafiya lau Jiddan Umma "
Mirmishi ta yi irin na babanta kafin ta ce"Umma mun gama shiryawa, har na É—umama mana sauran shinkafan da kika dafa jiya mun ci ni da Baby"
Baki na washe kafin na ce"Good girl to lunch box É—in ku fa?
Kai tsaye ta ce" Na soya mana doya Umma sai na haÉ—a mana tea za mu tafi dashi."
Farinciki ya cika ni domin na gaji har daman fargaban aikin safe nake yi na sake rumgume Jidda ina faÉ—in" Allah ya yi ma Jiddan Umma albarka.
Ta amsa da Amin Umma bayan mun gama ta ƙarisa wajen Abbansu bayan ya sauke Baby itama ya rumgumeta bayan ta gaishe su.

Ina dariya na ce" Yallaɓai ni fa yau Jidda ta fanshe ni bari na koma barci."
Ya na kallona ya mele baki kafin ya ce"To daman Sadiya yar laushi."
Ina shirin hawa kan gadon ban san lokacin da na fasa ba, hannu na saka na daki kafaÉ—an Yusuf ina hararansa kaucewa ya yi yana Æ´ar dariya idanuwana kamar za su faÉ—o wajen hararan shi, shi kuma yana ta faman dariya ya rike hannun Jidda da Baby yana faÉ—in"Mu je daga falo kafin mai mashin É—in ku yazo. Mu bar Sadiya yar laushi ta huta dakyau.."
Filon dake kan gadon na É—auka na wurga masa ina faÉ—in"Tafida bana son sunan nan fa."
  Da gudu daga shi har su Jidda suka fice daga ɗakin suna min dariya, nima mirmishin na yi sannan na koma na kwanta na lulluɓa da blanket ina tuna sunan da ya kira ni da shi, ko a baya a gida in aka kirani da wannan sunan sai Alhajinmu ya yi sharia faɗan ke rabuwa, Allah ya jiƙan Mama da Rahama ita ta lanƙayamin sunan nan da har gobe bana kaunarsa.
Ƙara gyara kwanciya nayi, ina tunanin me kuma wannan karon aka je aka gaya ma Alhaji akan abin da ya faru tsakanina da Ma'u?

Wayata na zura hannu na ɗauko na shigar da kaina cikin blanket ina duba wayar tawa, Missed calls na Rahila ba adadi tun jiya take kirana ban ɗauka ba har Yaya Murja na ga ta kirani har da Ma'u, kai matar nan ba karamar makira ba ce, uban ta zan yi mata da ta kirani bayan sun haɗu ita da ƙawarta sun ci mini mutumci? Kwafa na yi ni kaɗai na buɗe data ina ganin saƙonni na ta tururuwan shigowa, abin da ya fi jan hankalina ganin group ɗina gidanmu na S. YASHE'S sai faman tagging ɗina ake yi ko shiga ban yi ba saboda nasan zagi nake sha wajen su Yaya Abubakar tunda an taɓo yar gwal wacce ba ta laifi a wajensu, su na ba ni mamaki ta ya ya za ka yanke ma bangare ɗaya hukunci ba tare da an ji bayani daga ɗaya bangaren ba? Na rasa gane wani irin tasiri Ma'u ke da shi a wajen yan gidanmu da suke fifita damuwarta sama da damuwar ni da nake ƙanwarsu jininsu.

Na ga Yaya Murja ta min Vioce note mai tsawo ko buÉ—ewa ban yi ba, na ga ma mganar Yaya Abubakar naga dai a farko ya ce Sadiya ke wai ba ki jin mgana ko?
Sai saƙon Rahila rututu wajen ashirin na tsaki ma na kashe datan ta je ga ta ga Ma'un ta zaɓe ta sama da ni yar'uwanta da muke uba ɗaya, wulla wayar na yi can gefe na sake gyara kwanciya ina tunanin abin da zan gaya ma Alhaji, ba ni da damuwa da Yusuf saboda nasan halin mijina ɗan ba ruwan shi ne duk abinda na ce masa zai ce ya yi dai dai ne, mutum ne mai ƙoƙarin girmama duk wani abu da nake so da wanda ba na so duk da baya sanin wasu rigimgimun dake tsakanina da Ma'u amman shi shaida ne ni da ita ba ma ga maciji.

Rufe idanuwana na yi ina tuna abin da ya faru a shekaranjiya asabar wajen sunan ƴar ƴar'uwata da muke uba ɗaya Rahila wacce muka taso tare tun muna yara aure ma rana ɗaya aka yi mana. Tsabar baƙin ciki sai da na ji taruwan ƙwalla na yi saurin shanyewa, daga kan gado ina jin mganar Yusuf ta haraban gidan tunda window ɗakin na ta wajen haraba kenan su Jidda ya raka Salisu mai mashin ɗin da yake kaisu makaranta ya zo, ina kuma kwancen ba jimawa ya shigo ɗakin sai na yi luf kamar ina barci ina jinsa ya zo ya ɗauki wayarsa da laptop ɗinsa sannan ya kashe min hasken ɗakin ya fice bayan ya rufo min ƙofar. Sai na koma na ƙara lafewa na lumshe ido ina wani tunani a cikin raina ban sa na furta a fili ba sai da na riga na furta cewa" Ya Allah ka ƙara bani haihiuwa ko guda ɗaya ne na ƙara haifa."
Idanuwana suna yi wani luu kamar zan fashe da kuka in na tuna wautar da kuruciyar da na tafka a zamanin baya gashi yanzu abin da na aikata na neman ya zo ya dame ni.

Barci ya kwashe ni sama sama ban daɗe ba na tashi saboda na ji karan ruwa a Tiolet kenan Yusuf ya shiga wanka sai na miƙe duk da ina jin kasala na saka takalma na tsakar gida mai taushi na fita daga ɗakin na buɗe kofar kitchen ɗina na shiga mai girma ne, irin kitchen ɗin zamani amman ya yi kaca kaca saboda manya sun yi aiki mirmishi nayi Jidda, ba ni ta biyo ba karsashinta irin na Babanta ne amman da ni ta biyo ba za ta iya taimakamin kamar yadda take taimakamin yanzu ba, ta yi ma Baby wanka ta shiryata sannan ta shirya kanta ta kuma yi musu abin karyawa da na tafiya makaranta sai in naga dama na ke fitowa na yi wani abun. Gyara kitchen ɗin na yi sannan na dora ruwan tea bayan na saka haɗe haɗen ganyen shayi. Nima doyar na fere na soya mana sai na yi mana yar source ɗin miya ta albasa.
Na kwshe komai zuwa dining kenan Yusuf ya fito cikin shirin fita, sanye da shadda mai ruwan ƙasa dinkin riga da wando tazarce da hula a saman kansa kuɓe takalmin kafarsa mai buɗewa ne baƙi

A falon muka haÉ—u yana ta tashin kamshi sai na tsaya ina kallonsa har sai da ya tsole min ido kafin ya ce"Kallon fa? Na koma miki saurayi ne?
Mirmishi na yi kafin na ce" Ko da yaushe Saurayi ka ke a idanuwan Sadiya Injiniya Yusuf, ina kallon ka ne kamar yau É—in ne na fara ganinka a hanyar dawowata daga BUK a wata ranar laraba."
Na faÉ—a ranar ta na dawo mini a cikin tunanina a tare muka saki mirmishi, kujera na ja masa na dining ya zauna lokaci É—aya ya na faÉ—in"Na ce Æ´an mata doguwa sallamu alaikum ba, ki ka wani juyo kina min fari da ido kika juya kika cigaba da tafiyarki"
Ina dariya ban yi mgana ba ina tsaye ina haÉ—a masa tea shi kuma yana faman kallona, basarwa na yi ina faÉ—in" Yau sai ka shirya ba ka jirani na zo na shirya ka ba ko?
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"Na bar Sadiya yar laushi ta huta ne."
Da gangan na ɗiga masa ruwan zafi a hannunasa dake ɗaure da agogon fata baƙi, da sauri ya cire hannunsa a wajen ya na yarfewa ni kuma sai na haɗe rai ban ma kalleshi ba, cikin kallona ya ce"Sadiya bayan Tekwondon ɗin dare kin fara na safe ne? Kafarsa na taƙa dake cikin Takalmi da sauri ya janje kafarsa ya na faɗin"Akwai matsala kam."

Ina tura masa Mug É—in tea
ɗin gabansa da Doyar da na saka masa amman ban kalle shi ba. Na juya zan tafi ya riko hannuna amman sai na ƙi juyowa daman raina a jagule ya ke, amman sai ya yi tunanin mganarsa ne ya ɓata min rai, tasowa ya yi ya rumgumeni ta baya yana faɗin"Kin ji haushi ne? To Allah ya baki hakuri Sadiya ta."
Mirmishi na saki ina riƙe hannunsa kafin na juyo da shi muna fuskantar juna, gemunsa na shafa zuwa sajensa kafin na ce"Ka ji ka wani haushi? Sadiya ce fa da Yusuf? Ka manta.? Sai ya duka ya sumabaci goshina tunda ya fi ni tsawo kafin ya ce"To ai na ga za ki tafi ki barni ni kaɗai ahalin ba haka muka saba ba."
Da sauri na ce"Ruwa zan É—auko kasanni da shan ruwa"

Tuna haka yasa ya sakar min hannu na fice daga falon zuwa falo na biyu kitchen na koma na É—auko karamin mug na koma wajen depenser na tsiyaya ruwa mai É—an sanyi sannan na koma falon na ja kujera gefensa na zauna muka fara karyaawa.
Amman ni ba wani ci nake yi ba sai juya cokali na ke yi yana ta min hira kan wani kwangila gina makaranta da aka ba kamfanin shi sun gina wajen shekaru biyu ba a biya su kuÉ—in aikinsu ba to daman an kira shi tun wancan sati ana saka ran payment É—in shi ne ya ke ta mini surutu ba na wani fahimta gabaÉ—aya natsuwata ba ta tare da ni
Sai da na ji ya na kiran sunana.

"Sadiya."

"Sadiya."
Chapter 3 · 0% Book details