Sashe 28
Turken Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
 Daga haka kawai na fara ƙokarin tuɓe kaya da sauri ya taso ya rike ni lokaci ɗaya ya na faɗin"Ban riga na natsu na ga kwalliyar ba. Ballantana har na yaba na biya tukwaici shi ne kuma za ki hana ni samun wannan ladan?
 Ya faɗa ya na tsare da ido. A idanuwansa na fahimci ya gaji kuma ya na bukatar wanka ya huta. Sai kawai na ƙwace hannuna ina faɗin" Na yau dai ka makara. Amman ƙila gobe in ba ka makara ba ka rabauta"
 Da sauri ya riko ni na faɗo jikinsa sai ya rumgumeni ya na faɗin" kin manta kin ce yau zamu sabunta amarci? Na taho mana da kazar amarcin mu part 2"
"Shima ka Makara. Amarci kuma ka gama shan romonsa shekaru goma sha a baya."
 Na faɗa ina ƙokarin kwace kaina kai sai ya juyo da ni muna fuskantar juna na buɗe baki zan yi mgana ya haɗe bakin mu waje ɗaya yana kissing ɗina ni kuma na ƙi bashi haɗin kai sai kawai ya matse min cikina da ɗayan hannunsa ɗayan kuma ya riƙe wuyana dashi tamau yadda ya matse bakin mu waje ɗaya in na ce zan ƙwace kaina da karfi zan wahala sai kawai na saki na miƙa masa kaina tare da ragamar rayuwata bayan nima na saka duka hannunawa na zagaye ƙugun shi.
 Mun daɗe muna sumbatar juna har sai da ya gaji sannan ya sake ni. Ya na maida numfashi ina maidawa. A tare muka kalli juna gira ya ɗagamin kafin ya ce" Amarya ta."
Hararan shi na yi kafin na ce" Haka ake Ango kai duk ya fara furfura? Ni jarumi ne angona."
 Na faɗa ina gyara zaman rigata da ya zame min. Wata dariya ya yi kafin ya ce"Bari in yi wanka yau ƙila da rabon har Gwaggo sai ta zo jinya ina ga."
 Ina jin haka na ɗaga hannu ina faɗin" Yallaɓai na."
Rigarsa ya cire yana yar É—ariya ya ce"Sadiya ta."
Na san halin shi wallahi in ya so mugunta in na shiga hannu har sai na dawo ina magiya. Har mamaki na ke yi Yallabaina kullum kamar ƙara masa ƙarfi ake yi. Duk da mun yi aure yana tashen samartaka. Amman yanayinsa na yanzu ya na ninka yanayinsa a baya ne.
 Bin sa a baya na yi ina faɗin" Yallaɓai gajiyan tafiya ba ta sake ni ba. Ko na kwanta ne?
 Tiolet ya shige ya na faɗin"Ki kwanta mana na hana ki ne? Gwara dai ki yi ma kanki faɗa ki ɗauko kazar amarcinki a fridge ki fara ci kafin na fito. Zan karɓi maiƙon kazata a daran nan in sha Allahu."
 Nakwa nakwa na yi da fuska har lekoni ya yi yana dariya. Ba ni da mafita kitchen na fita na bude fridge ɗin na ga kazan dankwaleliya ce a faranti na sako mana kazar dai ta bakin shi ta sha maiƙo ga albasa da kabeji.
 Ruwa na ɗauko mana da lemu bedroom ɗin na kawo mana ba daɗewa sai gashi ya fito daga wanka ɗauro da Babban Towel a ƙugunsa ya ganni zaune saman cafet da farantin kaza a gabana.
 Ya kalleni sai ya saka dariya ni kuma sai na gimtse fuska cikin nishaɗi ya ce" Ke fa kika ce na taho da kazar amarci yau za mu tuna amarcin mu. Kin ga fa ke kika saka mini rai da kwaɗayi."
 Shuru na yi kawai na fara gutsiran kazan ina ci, shima sai da ya shafa mai ya saka gajeren wando sannan ya zo ya zauna ya na tayani cin kazan tun ina share sa har na saki yana bani a baki ina bashi mun ci kaɗan ba da yawa ba. Sannan na kwashe komai na maida kitchen sauran kazan kuma na saka a fridge.
 Wanka na shiga na gyara jikina. Bayan na fito na shafa mai na saka humra sai na saka wata rigar barcina ƙarama mai buɗewar gaba Yallabai na saman gado ya na jirana da na tsaya masa yanga ma tasowa ya yi yana faɗin" Kin san dai ina da karfin iya ɗaukan ki ko?
Cak ko ya É—aga ni sama amman sai da ya yi nishi.
"Wai wai. A gaishe da Yusuf."
Ya faɗa ya na jinjina nauyina ni kuma sai na kwashe masa da dariya na ƙara hantsila kafata da ya sa na gagari karfinsa mu ka faɗa kan gado. Bin sa na yi na danne ina faɗin" Wayyo karfin Yallaɓaina ya fara ƙarewa."
Ya na jin haka ya mirgina ni na dawo kasan sa ya kalleni sai kawai ya girgiza kai ya sauka daga kaina. Gadon ma ya sauka gabaɗaya ya je ya kashe hasken ɗakin sanɗa ya fara yi in ganin duhunsa na yi gefe ina dariya ina faɗin" Yallaɓai wasa fa nake yi"
Ban tsira ba sai da ya yi sufa ya dira kaina a saman gado. Ya turmusheni yana faɗin" Ƙarfin Yallaɓai ya ƙare ko?
Ina ta dariya. Haka muka dinga mirgina daga kudu zuwa yamma kafin dai mu natsa sai da muka yi wassanin da muka saba. Ni da Yallaɓai muna da wasu abubuwan da in ba mu yi ba ba ma jin daɗi. Yallaɓai ya ɗauke ni a komai na shi haka nima, za mu yi ta wassani muna dariya kafin mu faɗa farantama juna, cakulckuli ya rika yi mini kamar zan shiɗe sannan ya bi ni ya danne ya haɗe bakin mu waje ɗaya.
 Baki shi ke yanka wuya. Domin da gaske amarcin aka sake maimaitawa. Ni fa har da su Mama na ke kira da asuba Yallaɓai na ta yi min dariya ko kallon shi ban yi ba. Dirza na sha a hannun shi har sai da na gane ba ni da wayau ta bakin shi ya ce ya goge reni ne ina tunanin ƙarfin sa ya kare har ce min ya yi ko mata goma ne budare zai iya da su a dare ɗaya ai sai na saki baki ina kallon shi. Domin ai Yallaɓai ya fi ƙarfina.
 Ranar bai fita ba a gida muka yini tare. Kuma ta bakin shi maiƙon jikina duk sai da ya gama siɗe shi. Sai dare muka samu fita zuwa ɗorayi muka je na duba Alhajinmu daga nan na shiga gidan su Saude na yi ma Balaraba godiya.
 Washegari na shirya ya sauke ni gidan Halima na ƙara gaishe ta. Tunda ban samu suna ba na kuma ɗan jima tun da har girki na yi mata ita kaɗai a gidan ga jego. Jawahir ce ke zuwa mata kuma ta koma makaranta sai ƙanwar mijinta itama kuma yau ɗin ba ta samu zuwa ba.
Muna ta hira a bakin ta ma na ke jin wai Yaya Usman zai ƙara aure mijin Zabba'u.
Na girgiza da jin zai ƙara aure. In na duba yadda Anty Zabba ta ke son mijin nan na ta bata iya haɗa shi da kowa ga ta da kishin tsiya. Halima na faɗa min saboda maganar auren bai faɗa mata har sai da aka saka rana ta yi ta tashe tashen hankula daga karshe ma ta yi yaji a mganar da ta ke gaya min ma tana gidansu anan kano.
 Sai uku na rana na koma gida saboda girki. Saude suna da walima sauka a islamiyarsu ba ta zo ba. Ni dai na yini ina mamakin auran Yaya Usman ko alama Yallaɓai bai faɗa mini ba Hauwa ma ina ga ba ta sani ba. Munnira mun kwana biyu ba mu waya ba. Ita kuma daman Anty Zabba ɗin ba ma yi sosai iyaka in an haɗu a gaisa ne kawai tunda ba ma garin suke ba in ba wani sha'ani ko rashi ba sai mu shekara ba mu ga juna ba. Daman mutuniyata Hauwa ce sai Munniran da ba kamar yadda muke da Hauwa ba.
 Mu da ɗan yawa mu surukan a gidan marigayi Alhaji inuwa. Mu shidda ne har da Amaryan muhammad Kabir da bai daɗe da yin auran ba. Shi likitan jini ne yana katsina yana aiki da medical center can ya ke zaune da matarsa.
Ni da yake kowa ya san halina ba ni da shisshigi kuma in ma ka shige min ba lalle na iya mu'amala dakai ba sai in Allah ya haɗa jininmu to ballatana ma mai hali irin na Anty Zabba da shigen takama da ji da kai. Ko don ta na taƙamar mijinta na ta kuɗi sannan iyayenta ma wasu ne babanta tsohon alƙali ne a jihar kano mahaifiyarta kuma daga masarautar zazzau ta ke. Ni iyakata da ita in an yi wani abu da ya kamata na kira ina kiranta itama an aka yi min rasuwa ko rashin lafiya ta kan kirani ta gaishe ni. Ba sanayyar da zan iya kiran ta na ji labarin abin da ya faru ko Halima saboda ta na yar gida ce shi ya sa ta ji labarin.
 Har wajen biyar na yamma ina ta tunane tunane na kasa ma tashi na ɗora girki. Na kira wayar Hauwa ba ta shiga na ji kanun labari in ta sani sai kuma ban same ta ba. Ni kuma ba na son kiran Munnira ko yaya ne ina ɗan rike girma na, ganin har su Jidda sun kusa dawowa makaranta ban yi girki ba ya sa na tube na shiga kitchen store na fara dubawa sai na ga gabaɗaya kayan abinci sun yi ƙasa shinkafa ba ta wuce tiya daman shine buhun ƙarshe sannan taliya kwara biyu macaroni ma ya ƙare indomie ma ina ga tun ina Zariya ta ƙare tun da daman ko da zan tafi ƙawayanni na bari.
 Shinkafa tuwo ce kawai ta rage da ɗan yawa. Na yi tagumi ina kallon store ɗin ko kayan su maggi robobin sun yi ƙasa na tuna suma tun watan can da ya gabata ba a siye su ba. Kayan abinci kuma daman in Yusuf ya samu kuɗi ya kan siya da yawa haka in shinkafa ne buhu biyu uku haka taliya da macaroni katan uku ko biyu da yawa dai yadda za mu daɗe ba mu nema ba. Ina tunanin gashi kayan abinci ya ƙare kuma Yallaɓai bashi da kuɗi.
 Ya faɗa ya na tsare da ido. A idanuwansa na fahimci ya gaji kuma ya na bukatar wanka ya huta. Sai kawai na ƙwace hannuna ina faɗin" Na yau dai ka makara. Amman ƙila gobe in ba ka makara ba ka rabauta"
 Da sauri ya riko ni na faɗo jikinsa sai ya rumgumeni ya na faɗin" kin manta kin ce yau zamu sabunta amarci? Na taho mana da kazar amarcin mu part 2"
"Shima ka Makara. Amarci kuma ka gama shan romonsa shekaru goma sha a baya."
 Na faɗa ina ƙokarin kwace kaina kai sai ya juyo da ni muna fuskantar juna na buɗe baki zan yi mgana ya haɗe bakin mu waje ɗaya yana kissing ɗina ni kuma na ƙi bashi haɗin kai sai kawai ya matse min cikina da ɗayan hannunsa ɗayan kuma ya riƙe wuyana dashi tamau yadda ya matse bakin mu waje ɗaya in na ce zan ƙwace kaina da karfi zan wahala sai kawai na saki na miƙa masa kaina tare da ragamar rayuwata bayan nima na saka duka hannunawa na zagaye ƙugun shi.
 Mun daɗe muna sumbatar juna har sai da ya gaji sannan ya sake ni. Ya na maida numfashi ina maidawa. A tare muka kalli juna gira ya ɗagamin kafin ya ce" Amarya ta."
Hararan shi na yi kafin na ce" Haka ake Ango kai duk ya fara furfura? Ni jarumi ne angona."
 Na faɗa ina gyara zaman rigata da ya zame min. Wata dariya ya yi kafin ya ce"Bari in yi wanka yau ƙila da rabon har Gwaggo sai ta zo jinya ina ga."
 Ina jin haka na ɗaga hannu ina faɗin" Yallaɓai na."
Rigarsa ya cire yana yar É—ariya ya ce"Sadiya ta."
Na san halin shi wallahi in ya so mugunta in na shiga hannu har sai na dawo ina magiya. Har mamaki na ke yi Yallabaina kullum kamar ƙara masa ƙarfi ake yi. Duk da mun yi aure yana tashen samartaka. Amman yanayinsa na yanzu ya na ninka yanayinsa a baya ne.
 Bin sa a baya na yi ina faɗin" Yallaɓai gajiyan tafiya ba ta sake ni ba. Ko na kwanta ne?
 Tiolet ya shige ya na faɗin"Ki kwanta mana na hana ki ne? Gwara dai ki yi ma kanki faɗa ki ɗauko kazar amarcinki a fridge ki fara ci kafin na fito. Zan karɓi maiƙon kazata a daran nan in sha Allahu."
 Nakwa nakwa na yi da fuska har lekoni ya yi yana dariya. Ba ni da mafita kitchen na fita na bude fridge ɗin na ga kazan dankwaleliya ce a faranti na sako mana kazar dai ta bakin shi ta sha maiƙo ga albasa da kabeji.
 Ruwa na ɗauko mana da lemu bedroom ɗin na kawo mana ba daɗewa sai gashi ya fito daga wanka ɗauro da Babban Towel a ƙugunsa ya ganni zaune saman cafet da farantin kaza a gabana.
 Ya kalleni sai ya saka dariya ni kuma sai na gimtse fuska cikin nishaɗi ya ce" Ke fa kika ce na taho da kazar amarci yau za mu tuna amarcin mu. Kin ga fa ke kika saka mini rai da kwaɗayi."
 Shuru na yi kawai na fara gutsiran kazan ina ci, shima sai da ya shafa mai ya saka gajeren wando sannan ya zo ya zauna ya na tayani cin kazan tun ina share sa har na saki yana bani a baki ina bashi mun ci kaɗan ba da yawa ba. Sannan na kwashe komai na maida kitchen sauran kazan kuma na saka a fridge.
 Wanka na shiga na gyara jikina. Bayan na fito na shafa mai na saka humra sai na saka wata rigar barcina ƙarama mai buɗewar gaba Yallabai na saman gado ya na jirana da na tsaya masa yanga ma tasowa ya yi yana faɗin" Kin san dai ina da karfin iya ɗaukan ki ko?
Cak ko ya É—aga ni sama amman sai da ya yi nishi.
"Wai wai. A gaishe da Yusuf."
Ya faɗa ya na jinjina nauyina ni kuma sai na kwashe masa da dariya na ƙara hantsila kafata da ya sa na gagari karfinsa mu ka faɗa kan gado. Bin sa na yi na danne ina faɗin" Wayyo karfin Yallaɓaina ya fara ƙarewa."
Ya na jin haka ya mirgina ni na dawo kasan sa ya kalleni sai kawai ya girgiza kai ya sauka daga kaina. Gadon ma ya sauka gabaɗaya ya je ya kashe hasken ɗakin sanɗa ya fara yi in ganin duhunsa na yi gefe ina dariya ina faɗin" Yallaɓai wasa fa nake yi"
Ban tsira ba sai da ya yi sufa ya dira kaina a saman gado. Ya turmusheni yana faɗin" Ƙarfin Yallaɓai ya ƙare ko?
Ina ta dariya. Haka muka dinga mirgina daga kudu zuwa yamma kafin dai mu natsa sai da muka yi wassanin da muka saba. Ni da Yallaɓai muna da wasu abubuwan da in ba mu yi ba ba ma jin daɗi. Yallaɓai ya ɗauke ni a komai na shi haka nima, za mu yi ta wassani muna dariya kafin mu faɗa farantama juna, cakulckuli ya rika yi mini kamar zan shiɗe sannan ya bi ni ya danne ya haɗe bakin mu waje ɗaya.
 Baki shi ke yanka wuya. Domin da gaske amarcin aka sake maimaitawa. Ni fa har da su Mama na ke kira da asuba Yallaɓai na ta yi min dariya ko kallon shi ban yi ba. Dirza na sha a hannun shi har sai da na gane ba ni da wayau ta bakin shi ya ce ya goge reni ne ina tunanin ƙarfin sa ya kare har ce min ya yi ko mata goma ne budare zai iya da su a dare ɗaya ai sai na saki baki ina kallon shi. Domin ai Yallaɓai ya fi ƙarfina.
 Ranar bai fita ba a gida muka yini tare. Kuma ta bakin shi maiƙon jikina duk sai da ya gama siɗe shi. Sai dare muka samu fita zuwa ɗorayi muka je na duba Alhajinmu daga nan na shiga gidan su Saude na yi ma Balaraba godiya.
 Washegari na shirya ya sauke ni gidan Halima na ƙara gaishe ta. Tunda ban samu suna ba na kuma ɗan jima tun da har girki na yi mata ita kaɗai a gidan ga jego. Jawahir ce ke zuwa mata kuma ta koma makaranta sai ƙanwar mijinta itama kuma yau ɗin ba ta samu zuwa ba.
Muna ta hira a bakin ta ma na ke jin wai Yaya Usman zai ƙara aure mijin Zabba'u.
Na girgiza da jin zai ƙara aure. In na duba yadda Anty Zabba ta ke son mijin nan na ta bata iya haɗa shi da kowa ga ta da kishin tsiya. Halima na faɗa min saboda maganar auren bai faɗa mata har sai da aka saka rana ta yi ta tashe tashen hankula daga karshe ma ta yi yaji a mganar da ta ke gaya min ma tana gidansu anan kano.
 Sai uku na rana na koma gida saboda girki. Saude suna da walima sauka a islamiyarsu ba ta zo ba. Ni dai na yini ina mamakin auran Yaya Usman ko alama Yallaɓai bai faɗa mini ba Hauwa ma ina ga ba ta sani ba. Munnira mun kwana biyu ba mu waya ba. Ita kuma daman Anty Zabba ɗin ba ma yi sosai iyaka in an haɗu a gaisa ne kawai tunda ba ma garin suke ba in ba wani sha'ani ko rashi ba sai mu shekara ba mu ga juna ba. Daman mutuniyata Hauwa ce sai Munniran da ba kamar yadda muke da Hauwa ba.
 Mu da ɗan yawa mu surukan a gidan marigayi Alhaji inuwa. Mu shidda ne har da Amaryan muhammad Kabir da bai daɗe da yin auran ba. Shi likitan jini ne yana katsina yana aiki da medical center can ya ke zaune da matarsa.
Ni da yake kowa ya san halina ba ni da shisshigi kuma in ma ka shige min ba lalle na iya mu'amala dakai ba sai in Allah ya haɗa jininmu to ballatana ma mai hali irin na Anty Zabba da shigen takama da ji da kai. Ko don ta na taƙamar mijinta na ta kuɗi sannan iyayenta ma wasu ne babanta tsohon alƙali ne a jihar kano mahaifiyarta kuma daga masarautar zazzau ta ke. Ni iyakata da ita in an yi wani abu da ya kamata na kira ina kiranta itama an aka yi min rasuwa ko rashin lafiya ta kan kirani ta gaishe ni. Ba sanayyar da zan iya kiran ta na ji labarin abin da ya faru ko Halima saboda ta na yar gida ce shi ya sa ta ji labarin.
 Har wajen biyar na yamma ina ta tunane tunane na kasa ma tashi na ɗora girki. Na kira wayar Hauwa ba ta shiga na ji kanun labari in ta sani sai kuma ban same ta ba. Ni kuma ba na son kiran Munnira ko yaya ne ina ɗan rike girma na, ganin har su Jidda sun kusa dawowa makaranta ban yi girki ba ya sa na tube na shiga kitchen store na fara dubawa sai na ga gabaɗaya kayan abinci sun yi ƙasa shinkafa ba ta wuce tiya daman shine buhun ƙarshe sannan taliya kwara biyu macaroni ma ya ƙare indomie ma ina ga tun ina Zariya ta ƙare tun da daman ko da zan tafi ƙawayanni na bari.
 Shinkafa tuwo ce kawai ta rage da ɗan yawa. Na yi tagumi ina kallon store ɗin ko kayan su maggi robobin sun yi ƙasa na tuna suma tun watan can da ya gabata ba a siye su ba. Kayan abinci kuma daman in Yusuf ya samu kuɗi ya kan siya da yawa haka in shinkafa ne buhu biyu uku haka taliya da macaroni katan uku ko biyu da yawa dai yadda za mu daɗe ba mu nema ba. Ina tunanin gashi kayan abinci ya ƙare kuma Yallaɓai bashi da kuɗi.