← Book details Turken Gida Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 76

Sashe 20

Turken Gida Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

  Haka ya faɗa ya na tusa hannunsa a cikin rigata, wani sanyi na ji a cikin raina nima sai na kai hannuna saman kirjinsa ina shafawa kafin na ce.

  "Yallaɓai na, kana son ka ƙara aure ko?

Ya ji ni, amman bai yi mgana ba ina wasa da gashin ƙirjinsa cikin wani salo, mirginawa ya yi kaina ya kama bakina ya na kissing, nima sai na tallafi kanshi, daga nan mu ɗan birkita juna da salon wassani kafin mu koma muna maida nunfashi, tunda mai jan mota ya yi bakare a ƙofar boda ba halin shiga kuma ba halin fita.

  "Ƙarin aure hukunci ne na ubangiji. In Allah ya kaddaromin zan iya ƙarawa, amman ni a yanzu ba ni da ra'ayi domin duk abinda namijin kwarai ke nema a wajen mace ina samu a wajen ki, me zan nema kuma a wajen wata macen?
RaÉ—a na yi masa a kunne sai ya zille ya na dariya kafin ya mirgina ni na dawo saman shi ya É—aga ni na zauna a saman cikinsa yana kallona ya ce" Ina samun natsuwa a tare da ke, har ina jin ba Namijin da ya kai ni morewa ma aure. Ko wata na aura an ya za ta kai ki a wajena?
Ina dariya na ce"Oho. Amman dai ni nasan halin maza ne, kun ce ba kwa ta cin shinkafa ba sirki ba, gwara ku sirka da taliya ko macaroni"

  Dariya ya fashe dashi ina taya shi.
"To ni ke ce komai na, Taliyar macaronin tuwon duka kowani nau'in"
Kafaɗa na noƙe ina faɗin"Ba na son yaudara da daɗin baki"

"Sadiya ni zan yaudare ki? Yusuf É—in ki ne fa?

  Sukuwa na yi a kansa ina faɗin"Daɗin bakin maza ba, shi ne yaudaran"
Nishi ya yi kafin ya ce"Ba dadin baki fa a tsakanin Yusuf da Sadiyarsa. Allah da gaske na ke yi  ke ce duka kayan daɗi na."

  Ya faɗa ya na saka duka hannuwansa cikin rigata ta ƙasa, ya fara matsa min ciki da karfi, ina bige hannunsa ina cewa ya bari yaƙi, sai da na mirgina ya bina ya hau kaina yana ta matse mini ciki ina ta dariya har da hawaye sai da ya ga zan shiɗe sannan ya ɗagani yana faɗin"Ba daɗin baki Yusuf ke yi ba ko?
Ina dariya na ce"Yallaɓaina ba ya daɗin baki."

  Sai ya koma gefe ya na faɗin"Good. Girl."
Kafa na saka na shure sa ina faÉ—in" Sai na rama"
Yana dariyan keta ya ce"To taho mana, zo ki rama."

  Ya faɗa yana ƙokarin kamoni na matsa baya ina dariya na san halinshi, yanzu sai ya yi min mugunta, bi na ya yi yana faɗin taho ki rama mana Allah ba komai,

  Na haura ƙarshen gado ina faɗin" Ina ga na yafe maka." Dariya saka irin ta nishaɗin nan, sai da na tabbatar da ya ce ba zai min komai ba sannan na dawo jikinsa muka kwanta muna maida numfashi.

"Ka matse min ciki, in ka kashemin ƙwayayon haihuwata fa?

Ya na ƙokarin mikewa ya ce" Mu ga ni?  Ni fa na san in da na matse."

  Hannunsa na bige ina faɗin" Wato su ƙarishe mutuwa ka samu hujjar ƙara aure ko? Na faɗa ina yar dariya shi kuma ya daina dariyan ya koma ya kwanta kawai na fahimci baya son maganar yasa na koma na lafe saman kirjinsa ina faɗin.

"Ka sa ni ko aure ka ƙara ba zan taɓa juya maka baya ba. Saboda duk abin da ka kake so nima ina so, sannan ina son ka tara zuru'a kaima, amman abu ɗaya na ke so, don Allah kar ka yi hakuri ka ji a ranka saboda ban cike maka wani gurbi ba, mun kusa cika adadin shekaru sha biyar da auran mu, har ga Allah ban sa a raina zamu dauwama mu kaɗai ba, amman ina fatan lokacin da za ka yi auran ka wadatamu ka wadata kanka kada ka ɗauko aure ba tare da ka shirya ma hakan ba ka ji ko Yallabai na?

"Na ji."

  Haka kawai ya ce, na san halin kayana sai na fara shafa fuskarsa zuwa gemunsa ina faɗin" Ka yi fushi da ni ne?
Hannuna ya riƙe kafin ya ce"Ko ɗaya. Na ji maganarki amman ina so ki sani ko mata nawa zan aura a bayanki ne, kin zama Turken gidana ke ce tsanin duk matakin da na taka arayuwata. Ki bar ni da maganar auren nan."

  "Mu kwanta mu yi barci"

  Haka ya faɗa ganin ina shirin yin magana, dare ya yi domin ɗaya ma ta gota. Lafewa na yi saman kirjinsa shima haka tun muna jin bugun zuciyar juna, har barci ya kwashe mu gabaɗaya.

  Sanin halin da na ke ciki ya sa Yusuf bai ma tashe ni ba, ko da na tashi har su Jidda sun tafi makaranta. Yusuf ya yi musu abin karyawa da na lunch box, sannan muma ya dafa mana Tea ya soya mana ƙwai, ina ta shi ya ta sani tiolet ya ce na yi wanka ko da na fito ya zubomin tea a mug ya ce na sha sannan shima ya shiga wanka,  ban yi mamakin Yusuf ba sanin halin shi, ba shi da ƙiyuwar aiki, ya kuma iya komai yanzu ne ma aiki ya yi masa yawa amman zamanin farko farkon auran mu ai na mori Yusuf sosai. Shi ya yi zaman Bording School, shi ya sa aiki ba ya gagaran shi na tuna haihuwan Jidda na farko a gida na haihu kafin Gwaggo ta zo har ya gama wanke duka kayan jinin nan, haka zan tafi makaranta ban gyara gida ba sai dai na dawo na ga ya gyara gidan ya yi mana abinci, lokacin nan har makaranta ya ke rakani ya ɗaukar min Jidda,  kafin ya samu aikin nan na shi ya kankama mun gina wata rayuwa ne mai wuyar mantawa.

  Har ya bar gidan nan bai barni na ɗauki ko kofi ba. Sai da na raka shi ya tafi sannan na je na wanke kayana na jiya  da na ɓata na fita haraba na shanya, na ɗaga waya na kira wayar Saude na ce yau ta zo da wuri, kasala na ke ji na kasa komai gashi har lokacin jinin bai tsaya ba amman dai ba ya zuba sosai.

Da wuri Saude ta zo ta yi mini aikace aikace ta yi girki, sai wajen ukun rana na ba ta kuɗin mota ta koma gida, sukuku sukuku dai na yini Hauwa ma ta kira ni wai jiya ba ta san tafiya na ba, na ce ban jin daɗi ne, ta yi min sannu har ta na cewa ko zan leƙo can gidan Haliman? Na ce gaskiya a'a saboda ba na jin ƙarfin jikina ta yi min sannu sannan muka yi sallama.
Ni fa ko lafiyata ƙalau ba zan koma ba ko Rahila da ta haihu sau ɗaya na je sai ana gobe suna da ranar suna na koma.

  Saboda yanayina tun ranar ban ƙara fita ba ina gida ina shirin tafiya Zariya. Na gama haɗa duka takardun gwaje gwajen da aka yi min a asibitocin kano da tests da sauransu waje ɗaya saboda kar na manta. Na ma kira Anty Khaleesat na faɗa mata ina nan zuwa, Yaya Hamzan dai na kira shi ban samu ba.
Ranar asabar da yamma muka je gidanmu tare da Yara na sanar da Gwaggo tafiyata Zariya ta ce Allah ya sa a dace. Na jira har Alhajinmu ya dawo shima na faÉ—a masa.

"Allah ya sa ki je a sa'a. Allah ya sa a samu abin da ake nema."

  Na amsa masa da Amin Amin, mun daɗe a gidan sai wajen goman dare Yallaɓai ya zo ya ɗauke mu, shima baya samun zama a Rano ya ke yini, saboda ya samu kwangilan gina wannan gidan biredin, gabaɗaya ya kwashe kuɗin hannunsa ya zura a ciki.
Sai da muka dawo gida mun yi shirin kwanciya na ji suna waya da Uncle Abba, na ji kuma ya na faÉ—in bashi da kuÉ—i.

  Sai da suka gama waya, ina gaban madubi ina saka Humra, yau ni amarya ce domin jinin ya ɗauke min yau da safe,shi kuma ya na zaune gefen gado daga shi sai ƙaramin wando.

"Wai an ya za ka samu rakani asibitin nan kuwa?

  Na faɗa ina kallon bayansa ta cikin madubi, bai juyo ba na ji ya ce"Ina tunanin haka nima, saboda aikin nan kuma kin ga ana buƙata ta a wajen"
 
  Sai da na gama fesa turaren na gyara gashina da na kasa kitso har yau, kuma na kasa wanke shi a gida na kuma kasa zuwa a sake wanke mini.

  Gabansa na zagayo ina faɗin"In ba ka da lokaci ka bari gobe kawai na tafi, in na ga likitan zuwa jibi sai na dawo in sha Allahu."

  Kallona ya yi kafin ya ijiye wayarsa a gefe, ya saka hannu ya jawo ni na zauna a saman cinyarsa ya zagaye hannayensa a kuguna muna kallon juna.

"Kin tabbatar da ba matsala in kika tafi ke kaÉ—ai?

  Ina yar dariya na ce"Haba! Kamar wata yarinya? Ba matsala Allah tunda aiki ne ya hana ka rakani."
Sai ya jinjina kai kafin ya ce"Ga lambar Dr Fadil Abba ya turamin ya ce sun yi mgana in kika je asibitin shi za ki fara nema."

  Sai na gyaɗa masa kaina gudun mantuwa sai ya ce na ɗauko wayata na kwashe lambar, tashi na yi na ɗauko ya faɗamin na saka na yi saving ina so na yi masa maganar kuɗi amman kuma sai na fasa na san Yusuf game da lafiyata in dai yana da shi ba abin da ba zai yi min ba, ni ina da kudi a hannuna 40k, na so na siya ma Halima turmi atamfa da rigan yaro amman sai na ga Yusuf ba shi da kuɗi ya saka a wannan aikin sai na dakata, in har bai ba ni da yawa ba sai na ɗauka na ƙara dashi.

  A daran mun raba dare muna farantama juna rai.
Muna ƙamƙame juna, cikin shauƙi da kauna.

"I miss you Sadiya ta."
Chapter 20 · 0% Book details