← Book details Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 112

Sashe 29

Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saliha kuwa tana fita d'akin Rynt ta nufa tana shiga Rynt tace"ya akayi ne saliha ko ya dawo ne? Komai saliha bata ce ba sae d'aukar jakarta tayi ta fita.
Rynt ta biyota tana fad'in "saliha kimin bayani mana"
sam saliha bata saurara mata ba tayi ficewarta.
Ita kuwa Rynt tana kawowa bakin qofa tayi kici6is da mohd da qarfi ya turata ta koma ciki ya kuma rufe qofar da key.
Inda kai tsaye ya yakai hannu kan wuyan hijabinta ya rabashi biyu, a firgice Rynt tayi saurin kama hijabin ta riqe tace"malam meye haka dan Allah!
bai kulata ba sae hijabin ya fizge ya yar ,ta koma d'auka ta rufe jikinta.
Sai kawai yaje yayi zaune abinsa kan sofa ya d'aura qafa kan qafa yana juya belt d'in hannunsa a hnkli snn ya kalli Rynt da taje jikin wardrobe zata nemo wani hijabin yace"ki ma daina wahaladar da kanki don kaf kayan jikin ki ne zan raba ki dasu sbd ni sam bana dukan mutum da kaya a jikin shi, ta fiddo ido waje cike da tsoro tace"kenan kai d'an iska ne"yace"eh sosai yanzu kuwa zan nuna miki"ya taso gadan gadan zai zo gurinta.
Tace"Aa dan Allah kayi haquri wlh zanje na gyra ma d'akin ka indan shine "
Idan na gama dukan ki ba ya fad'i hankane tare da fizge hijabinta ya jefar ya kamo wyn rgrta zai yaga...tace"wayyo dan Allah kayi hqr"ta qarashe mgnr tare da fashe masa da kuka tana roqon shi yace"shin saliha bata gaya miki horon da nake musu bane da suna en yara"cikin kuka sosai had'e da girgiza kanta tace"wlh Aa bata gaya min ba"yace"to kiji kaf qannai na duk wanda yamin laifin duka se ya cire tufafin sa nake dukan sa sbd ni ba sakaran mutum bane da zan daki mutum da kaya a jikin shi, kuma duk na daki mutum sau d'aya to ko da kuskure bazai qara min laifin da zan sake dukan shi ba, amma ke sbd a iya qafafun ki kad'ai na daka shine kika sake min wani laifin duka wae har ni zaki duba ki kira qaton banza,yana kawo nn sae jin tayi bata tare da rgr jikinta don zama d'aya ya yage ta ya jefar ,ya zamo vest kad'ai ke jikinta sae kuma zani ,wani irin kuka ta fashe dashi mai cin rai had'e da saurin durqushewa qasa,tana girgiza mai kai tana ja baya sbd yanda yake matsowa kusa da ita, cikin zafin nama ya miqar da ita tsaye tayi saurin sa hannayenta ta kare qirjinta tace"idan kai musulmi ne na roqe ka da girman Allahn da muke bauta ma kar ka rabani da kayan jikina"hannu yakai ya jaye tsorayen kalabarda suka soma rufe mata fuska snn ya d'ora hannayensa kan kumatun ta da hawaye keta fmn sintiri yace"na barki sbd girman fiyayyen halitta amma ki sani bake ba boko har abada!
Nn ya juya ya fita ,ita kuwa taje kan bed cikin tsananin kuka taja blanket ta rufe jikinta har wuya nn ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukan da duk wanda ya gani zai d'auka ko kaf duniya an mutu ita kad'ai aka bari a raye sbd baqin cikin yanda ya rabata da hijabinta har rgrta sae duk taji duk duniya ba wanda ta tsana kmr shi,sbd still cikin su ukun nn tafi yarda a ranta cewa shine dai makashin babanta.
Qofa taji an turo tayi saurin d'agowa don ta d'auka ko shine ya dawo, sae taga malika ce wacce ke d'auke da shu'umin murmushi a fuskar ta tace"kad'an kenan daga cikin sharrin na,dmn ni ba'a taka ni a zauna dai dai,inace yanzu kin fara ganin kuskuren ki na auren mijin da ba naki ba,wanda kwata kwata ba'a halitto shi wa kowa ba sae ni kad'ai,amma sbd kwad'ayin duniya irin naki kika shigo sabgar da ba taki ba,kika lalata min tsarin rayuwata gabad'aya, to bari kiji wlh idan har bakiyi gaggawar rabuwa da mijina ba nice zan zamo ajalinki.
Kmr bada Rynt take zancen ba don tun lokacinda Rynt ta d'ago taga wace ce ta maida kanta kawai taci gaba da kukanta,har kuwa ta fita.

Har kusan kwana biyu Rynt bata bar kukan abinda mohd ya mata ba sbd taji ciwo sosai fiye da zaton mai karatu,dmn idan aka cire mutuwar mahaifinta to shine abu na farko da tafi jin ciwon sa a duniya.

Duk kwana biyun nn mohd na shigowa d'akin Rynt da safe kafin ya tafi asibiti,wanda duk shigowar da yake ganin ta yake zaune kan bed ta had'e kai da guiwa kuma har ya fita bata d'agowa bare zancen gaida shi.

Sallar zuhur ta gama snn ta tashi tayi shirin islamiyya ta fita.
Bayan sun tashi da qarfe hud'u a maimakon ta koma gida sae napep ta nema ta tafi gidan inna.

Mohd na zaune shida malika kan dining inna ta kirashi a waya sae masifa take mai,
kan dole ya ajiye zancen cin abinci ya tafi gidan inna.
Inna tasa shi d'aki shida Rynt tace"sae naji Rynt tazo min da wani zance wae ba zaka barta tayi boko ba,yace"bata snr da ke laifin da tamin bane inna.....Yo dan bata je ta gyara ma d'aki ba har shine wani laifin da za kace ba za tayi boko ba,to bari kaji ubanka kabiru ma bai isa ya hanata bokon nn ba bare kai,boko kam sae Rynh tayi shi kmr kowa don ba za'a barta a baya ba,kuma dolenka ka d'auki nauyin krtn tunda mtrka ce,yace"gsky inna kiyi hqr don na riga da yanke hukunci.....inna ta dunqule yatsu ta watsa mai tace"ubanka! nace ubanka kabiru! yo har ni zaka duba kace ka rigada ka yanke hknci sbd ban haifeka ba ko,ko d'aya ba hk bane inna sae fa da na gaya mata duk bata je ta gyara min d'aki ba bokon ta ne haka wae shine don ta raina ni ta saka saliha wai ita ta gaji da gyrawa qaton banza d'aki har ni zata kira qaton banza !Rynt tace"wlh Allah inna bance masa qaton banxa ba..... A fusace mohd ya taso xai bugewa Rynt baki, tayi saurin tashi ta koma bayan inna ta la6e ,inna ta tashi tace"yo da dukanta zakayi to"cikin yanayi na 6acin rai yace"to inna ni sa'anta ne da zata qaryata"
inna tace" lallai Muhammadu sam albasa bata biyo hln ruwa ba indai kace dukan mace kake, don ubanka kabiru duk iya shegenda uwarka take mai bai ta6a sa hannu ya dake ta ba, kai kaf ubannanka ba mai dukan matar sa, sae kai zaka ce ka fara sbd baqin zuciya irin taka,
nn ta maidà dubanta gun Rynt da ta soma kuka tace" zo zauna abinki ya dake inga inshi shashan yaro ne.
Sae da ya koma ya zauna snn Rynt ta iya zama yace"inna ki barni kawai da yrnyr dan Allah ki ftr da bakin ki a cikin zancen nn......naqi na ftr d'in shashan yaro ai kwanaki kafin aurenka zowa kayi nn ka nemi na roqa maka alfarma agun mahaifinka don ka samu kaga ka auri wnn yrnyr er marasa mutunci ,shine yanzu tunda burinka ya gama cika har ni kake cewa na daina sako bakina a cikin zancen ka ,iye lallai Muhammadu yau ka nuna min ban isa dakai ba.
Ta qarashe mgnr ne cikin muryar kuka irin nasu na tsafi d'in nn.
Cikin nuna damuwa mohd yace"inna ba haka bane wlh yrnyr nn tafa ranani sosai wanda dole ya kamata ace na d'auki mataki akai......yo muhammadu ita Rynh d'ince ta rainaka yrnyr er albarka wacce ba ruwanta da kowa, kuma ai tunda na sako bakina a ciki ya kamata ka haqura koma mene ne idan kuma banda wani matsayi a gurinka shikenan sae ka tashi ka tafi ai inada kud'in da zan sata mkrntr ba wai rasawa nayi ba.
Kauda kansa yayi gefe cike da takaici yace"ki barshi kawai zan sata d'in"
inna tace"bama so! kuma idan kaje gidan naka ka aiko min da duk kayan Rynh don a nn zata zauna tayi bokon ta"
Nan Mohd ya shiga ba inna hqr ba don yaso ba har ya samu ta haqura.

A tare suka fito shida Rynt wacce har takai hannu zata bud'e murfin mota ta shiga ya daka mata tsawa yace"bana son raini tare mukazo ne!
Kallon sa kawai Rynt tayi snn ta juyawarta ta kama hnyr fita riqe da er ledar ta da inna ta bata mai d'auke da kular d'an wanke a ciki.

Tana fitowa gate d'in gidan sae mota ta gani a gabanta ta faka, snn aka zuge glass d'in motar a hnkli
qoqarin kaucewa take sae taji muryar munir yana cewa"Rynt ina yini"kallon sa tayi sae kuma tayi saurin sadda kanta qasa tace "yaya munir barka da wuni"yace"lfy lau yasu inna da mohd tace"suna lafiya"

Dukkan su sukayi shiru can munir yace" Rynt sae kuma naji.... yayi shiru sbd hawayenda suka cika mai ido, Rynt ma hkn ce ta kasance a gurinta,kmr daga sama taji muryar mohd yana cewa"ke je shiga mota gani nn zuwa.
Ba musu ta wuce sbd kar kukan da take ji ya qwace mata mohd kuwa ba yabo ba fallasa ya ba munir hannu suka gaisa har ma yana tmbyrsa mutanen gida.

Sai da suka gama gaisawa snn munir yaja motarsa shi ma mohd yaje ya shiga tasa motar,
Da shigar sa ya kalli Rynt wacce tayi saurin sa hannu tana share hawayenta,kauda kansa yayi had'e da tsaki snn yace"da kina sonsa meyasa baki aure sa ba sae ni kika cutar"komai dae Rynt bata ce mai ba sae kauda kanta tayi gefe tana kallon titi.
Chapter 29 · 0% Book details