← Book details Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 112

Sashe 18

Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kmr daga sama ta hango motar man tafe ya zo gab dasu ya tsaya kmr mai shirin taka musu qafafu don tsirif ya rage har sae da sukayi saurin ja da baya.
Dukkan su da mugun kallo ya fito yana binsu dashi,yace da Rynt shiga mota"kallon sa ta tsaya yayi ya daka mata tsawa yace"shiga mota nace!cikin 6acin rai taje ta shiga motar ya zagaya ya shiga yaja motar a tsiyace had'e da bazawa munir qura.

Tafiya yayi da ita mai nisa snn ya samu guri ya parker ya kalli Rynt da tun lokacinda yaja motar gabanta ke dukan tara tara kaddai ace ya gane ko ita wace ce,yace"oya cire wnn baqin abun dake kan fuskar ki magana nake son zanyi dake"
Ba musu ta yaye niqab d'inta ba tare da ta kalle sa ba.
Sae da yakai hannu ya d'ago fuskarta yana kallonta shaye da toka snn yace"abu zan nema agunki wanda ban ta6a nema agun kowa ba wato alfarma, alfarmar itace ina son dan Allah idan Abbana ya kiraki ya tambaye ki ko kina sona kice masa A'a shine kawai ni kuma idan kika min haka nayi miki alqawarin duk wani abu da kike so a rayuwa ki tambaye ni zan miki shi koma mene ne kuwa"amma wlh kar ganin na had'aki da Allah ki raina min da wayo dmn duk kika yi gigin amincewa buqatar Abbana sae dai a nemi wata bake ba!
Manyan idanuwanta farare tas take ci gaba da kallon shi dasu snn ta ta6e baki tace"ai sae ka fayyace min komai ta yanda zan fhmta"
Mugun kallo ya watsa mata yace"daqiqiyar inace ke da bazaki fhmta ba ,da Allah ni ftr min daga mota kuma wlh ki tabbatar kinyi abinda na saki!
Ba musu kuwa ta fita motar don yanda taga yanayinsa ko tura ta zai iya yi ta fad'i, sae dai da gani akwai mgnr da takeyi a ranta haka kuma akwai nazarin da takeyi shi kuma mohd har lokacin kallon takaici yake mata snn yaja motarsa a tsiyace ya bar gurin.

Da qyar Rynt taga ta sami napep sbd yanayin anguwar da ba kwaramniya bare abin hawa ya yawaita.
Nazari take yi kam har ta isa gida ko kuma nace har akayi sllr isha'i bata daina nazarin ba yayinda tuni zuciyarta ta ganar da ita abinda ke shirin faruwa sae dai taqi bawa kanta damar amincewa da hkn har sae Abba ya kirata tukun taji koma mene ne.

Tana gama cin abinci Abba ya aiko Ameera yana son ganin ta.
Taje ta same shi shi kadai zaune a falo.
Ta nemi guri a qasa ta zauna ta kuma gaida shi cikin ladabi kmr koyaushe.
Cikin sakin fuska ya amsa snn yayi gyran murya yace"Rynt haqiqa duk mutumin da ya zauna dake zai yi sha'awar kyawawan halayenki da kuma d'abiunki,a dalilin hakane ma yasa nayi sha'awar had'aki aure da mohd,amma kuma ba dole sae idan kina ra'ayi kuma dan Allah kar ki 6oye komai a ranki,dmn ita rayuwar aure wata sabuwar rayuwace da ta banbanta da kowace rayuwa wacce dad'inta ka auri wanda kake so yake sonka, shiyasa nake son ki snr dani gskyr abinda ke ranki ma'ana idan ba kya ra'ayin auren ki da mohd kar kiji shayin komai ki snr dani idan kuma kina ra'ayi sae dai nace Alhmdh dmn zanfi kowa farin ciki da haka.
Tun farkon fara zancen sa ba qaramin girgiza Rynt tayi da jin zancen ba amma sae ta dake bata yarda ya fhmci halinda take ciki ba.
Bata son mohd bata kuma jin zata soshi har abada!amma kuma ko don ta d'auki fansarta a sauqaqe zaisa ta amince da aurensa to kuma ya zata ce da yaya munir dake matuqar son ya aureta.
Duk a cikin ranta take wnn tunanin ,Abba ya katse ta da cewa ke nake saurare Rynt ,sae da ta qara sadda kanta qasa snn tace"na Amince Abba zan aure shi"Abba yace "kin tabbatar Rynt ba cutar kanki kikayi ba? eh wlh Abba har raina na amince.
Wani irin dad'i Abba yaji har ransa, yace"Allah yayi miki albarka Rynt, ya kuma sa ki gama lfy da duniya"da qyar ta iya cewa amin kan kukan da ke qoqarin zo mata sbd tuna baffanta da tayi da kusan kullum sae yayi mata irin addu'ar nn.

Koda ta koma d'aki ba kowa sae tayi kwance abinta tana ta kukan tuna Baffanta har sae da tayi mai isarta snn ta tashi tana tunanin me zai faru idan mohd yaji ta amince da buqatar abbanshi ko ita ma kasheta zai yi kmr yanda ya kashe mata Abbanta.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2:43PM, 5/2/2017] Billy giro😊: [ 1/8/2017]
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

🔮🔮🔮
_*page*_ *```22```*
Don tasan a rashin imaninsa zai iya aiwatar da abinda ma yafi haka in akwai, amma kuma bari taga shin me yake nufi da sae dai wata ba ita ba.
Abba kuwa da mohd har umma ba wanda ya kira cikin su bare ya snr dasu yanda sukayi shi da Rynt kawai ya yanke hukunci sae inna ta dawo su yanke shawara shi da ita asa rnr aure.

washe gari hnklinta a kwance tayi shirinta na islamiyya ta fita.

Ko minti 5 batayi da fita ba inna ta dawo daga qauye kuma a nn gidan ta sauka sae murna ake da dawowar ta yayinda ita kuma ta matsu taga Rynt nn Abba ke snr da ita ai ta tafi islamiyya.

Bayan inna taci abinci ta d'an huta Abba ya shiga snr da ita shawarar da ya yanke kan zancen had'a mohd aure da Rynt har yanda sukayi da Abban malika duk sae da ya snr da ita.
Sosai inna tayi murna ba kad'an ba haka kuma itama bata bada goyon bayan mohd ya auri malika ba wanda duk zancen nn da suke yana kunnen hjyrsu mohd wacce tana gama sauraren kaf abinda suka tsara ta koma d'aki cike da masifa ta kira mohd a waya ta snr dashi tace"ga irinta nn sae da nace kbr ni da yarinyar nn ni nasan yanda zanyi da ita wanda ko da kuskure baza ta yarda ta amince da zancen Abbanka ba wlh, amma kace a'a wae kar ta rainani ,raini duk ya wuce ace kmrta baqauya er matsiyata ta had'a surukuta dani,mohd yace"yanzu umma kina nufin duk yanda nayi da ita ta amince da buqatar Abba? Hm!na nawa kuma gashi har sun tsara anjima da dare iyayenka zasu tafi gidan inna asa ranar aurenku!ai wlh kayi wa kanka!don yanzu sae kasan yanda zakayi ka ftr da kanka ko kuma ka nemi wata uwar don muddin ka rasa mafita har takai ga an aura ma ita tofa bani ba kai tunda tun farko sae da nace kabarni da ita kaqi.
Daga haka ta katse wayar sae huci take
tace"in shi mai hnkli ne ko islamiyya baxata dawo ba sae dai wata ba ita ba amma bari nasa ido naga ko dabara ta tayi!in yaso ni kuma na tayasa da wani aikin ta yanda baza ace dasa hannun mu kan 6acewar ta ba.

Mohd kuwa hjyrsa na kashe waya ya rasa ta inda zai sa kansa kan baqin ciki da kuma tunanin hukuncin da zai yiwa Rynt.
Ya zama dole yaje ya jirata kan hnyrsu ta islamiya don yau sae ta fad'i wanda ya aiketa .

Yana fita da motar sa yayi kici6is da Malika ta parker motar ta ta fito, dole ya tsaida tasa motar ya fito yaje gab da ita ya tsaya yana mata wani irin kallo,ita kuwa ta wani langwa6ar da kanta snn tace"my man wai ya ake ciki ne tun jiya da mukayi waya naji shiru har yau "
yace"to shine zaki wani biyo ni har gida da kuma wnn banzan dressing d'inki salon Abbana ya ganki yace bakida kamun kai kuma,in yaso Komai ya qara cakud'e mana! Kayi haquri my man wlh banda wasu kaya sae ire iren su kuma ka sani,to me ya hana ki kirani a waya muyi magana? Ina mgnr zata yiyu a waya nida kwata kwata daren jiya ban samu nayi bacci ba,amma malika kinsan bana son damuwa koma mene ne ai zanje na sameki har gida,kayi haquri na damu ne sosai ,tayi mgnr cike da qwallah tap a idonta, yayi saurin cewa"shikenan kar kiyi kuka gaya min me kike so yanzu?so nake ka gaya min abinda ake ciki ,ajiyar zuciya ya sauke snn yace"wnn yrnyr ta lalata mana komai don ta amince da buqatar Abba snn kuma Abbana har yanzu dai yana kan bakarsa na bazan aureki ba,amma kar ki damu zan shawo kan matsalar komai inshaAllah ,matsalata d'aya yanzu shine anjima za'a sa rnr aurena da wnn yrnr shiyasa at all kaina ya kunce bansan ma wane hukunci zan yanke ba, ga umma ta sani cikin wata chakwakiyar wae bani ba ita idan ban nemo mafita ba har akayi aurena da wnn yrnyr.... Wae da kana nufin zaka yarda ayi auren ne to! Malika uba ba abin wasa bane idan kuma ya yanke hukunci ba yanda za'ayi kuma ya rantse cewa in ta amince tofa shikenan ba fashi aurena da ita, but my man be wise mana,idan ba yrnyr ai ba auren shike nn dole Abba ya haqura, aikin hnkli dai malika ina mai gaya miki 6atar wnn yrnyr tmkr tsinuwace na jawa kaina don dole Abba yasan nine, kawai dai zan aureta amma na d'an wani lokaci .....Wlh! my man bari kaji in gaya ma ba maccen da ta isa ta aure ka bayan ni don ka ma daina wnn sa6on!daga haka taja motar ta a tsiyace ta bar gurin.
Har zai shiga mota sae ga kiran Abba yana son ganin shi,dole ya juya ya tafi ga kiran Abba.
Chapter 18 · 0% Book details