Sashe 81
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Widad ta fita tsakar gida, ta ƙarasa inda Gwaggo take tana murmushi, Hari tace "ohh ni Harira, se wangale baki kike miji ya dawo, kin ware"
Widad tace "Toke ya kika gani? A garin nan banda Allah se shi na sani, idan lafiyarsa ta taɓu akwai damuwa sosai"
Gwaggo tace "ƙyaleta Amarya, zolayarki take"
Widad tace "Mama, dan Allah abun nan na É—akinki sunmin kyau sosai"
Gwaggo tace "me fa?"
Widad tace "kwanukan nan da kika shirya a É—akinki, sunyi kyau sosai fa"
Gwaggo tayi murmushi tace "Widad kenan, kayan Su Samira da fanteka kenan, mu dasu mukeyin adon É—aki"
Widad tace "Masha Allah, gaskiya sunmin kyau sosai Mama"
Can ta hango bulugari, a gefen Gwaggo zata kaÉ—a miya.
Widad tace "ya sunan wannan Mama? Wanda kike juya miya dashi"
Gwaggo tace "Bulugari kenan, dashi muke kaÉ—a miya"
"Mama wannan tunkunyar naganta baƙa sosai"
Gwaggo tayi murmushi tace "wannan itace Talle Amarya, tukunya ce ta ƙasa, muna girki a cikinta, miya tafi zaƙi da daɗi Sosai"
Widad tayi murmushi tace "taɓ Mama duk ban san wannan abubuwan ba, ban taɓa ganinsu ba"
Gwaggo tace "hakane dama, tunda ba kuyi rayuwar karkara ba ba lallai ki sansu ba, bari inje É—aki in É—akko abun kaÉ—i"
Gwaggo ta tashi ta tafi, tana tafiya
Hanne tayi tsaki tace "Aikin banza mutum ya zauna yaita ƙarya, mtseww aikin banza dana wofi, wai bata san bulugari da fanteka ba"
Widad ko waigawa ba tayi ba, tai shiru abunta, Hari tace "wato Wudas kinfi jin tsoron Hanne, ta gayamiki duk abunda data ga dama, kiyi ƙus amma da nice da tuni kim hayayyaƙomin"
Wani irin kallo Widad tayi wa Hari, nan take cikin Hari ya kaÉ—a, ganin wani irin kallo da Widad tayi mata, se taga kamar ta canza gaba É—aya daga kamaninta, ba shiri Hari taja bakinta ta tsuke.
Saleh ya kalli Yusuf yace "Sannu Yusuf, gaskiya kana fama, yanzu haka kuke zaune? Tana maka wannan gadarar da jin kan, bayan taimakonta kake"
Yusuf yayi murmushi yace "lafiya ƙalau muke zaune da ita, duk wannan abubuwan bata Yimin, ƙalau muke zaune Alhamdilillah"
Saleh yace "kaga nifa bana son wannan kawaicin naka, kalli yadda take wani bintsire bintsire, tana cin magani, na zata tuni ta dena wannan halin nata?"
Yusuf yace "Kai da ita ta baka amsar wannan tambayar, Amma nan ma shigo ka tarar tana bani Abinci ai"
Saleh yace "kuma fa hakane, lallai kai ɗan baiwa ne kuma na musamman Yusuf, wannan yarinyar me Azabar taurin kai, amma take kula da kai haka, ta yadda ka shiga jikimta gaskiya abun da mamaki, kayi namijin ƙoƙari fa"
Yusuf yayi murmushi yace "Haka lamarin ubangiji yake, yanzu ya jikin mahaifinta?"
Saleh yayi shiru da alama jikinsa yayi sanyi yace "labari mara daɗi Yusuf, yanzu ma badan ka tambaya ba bazan gaya maka ba"
A rikice Yusuf yace "Subhanallah, meyafaru kuma?"
Saleh ya gyara zama ya waiga yaji babu motsin kowa sannan ya waigo ya kalli Yusuf yace "An sace Daula akan gadon Asibiti"
Dafe ƙirji Yusuf yayi yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, kamar yaya?"
Saleh yace "kaima dai ka tambaya, abun kamar almara, Kasan tunda yake rashin lafiya Anwar ne kawai yake sintirin jinyarsa, matarsa da sauran yaran ba ruwansu dashi, daga ya É—an fito daga É—akin, ya koma aka nemi Daula aka rasa, yanzu haka an kama Anwar da me Asibitin ana tuhumarsu, yau sati uku kenan sun tsare "
Dafe kai Yusuf yayi ya shiga murza goshi, wannan wane irin bala'i ne? Duk yadda yake zaton lamarin ya wuce tunaninsa, wane irin tashin hankali ne haka?
Saleh yace " ka kwantar da hankslinka fa, ban gaya maka dan ka É—aga hankalinka ba, sedai ka tayata da Addu'a, sannan karka bari ta sani"
Yusuf yace "kuma ana bincike akan lamarin, ba'a gano inda yake ba?"
Saleh yace "kai dai ayi sha'ani, har yanzu babu Labari"
"Amma naji kamar kace kasan suwaye ke wannan abubuwan"
Saleh yayi murmushi yace "kaifa jami'in tsarone, kuma kai aka bawa wannan aikin na binciken, zuwa yanzu ai nasan ka samu haske akan binciken da kayi"
Yusuf yace "kamar yaya kenan?"
"Kana nufin baka gane me nake nufi ba? Ai shikenan mu bar zancen, kar tazo ta same mu muna maganar"
Yusuf yace "Ya Ummana kuwa Saleh?"
"tana nan lafiya, Suleiman yana kula maka da ita"
"Amma Saleh, Akwai wani abokin aikina Abbas, babban Abokina nane, yana Ibadan akan aiki, ko Suleiman yayi maka maganrsa, nasan idan yasan ina nan Abbas ze shiga damuwa ina da tabbacim se yazo nan"
Ƙura masa ido Saleh yayi, ya ɗanyi shiru sannan yace "gaskiya ba muyi maganar wani da shi ba, kai dai kunci gaba da haƙuri, komai ze wuce kamar ba'ayi ba Insha Allah"
Yusuf yace "Allah yasa"
Saleh yace "bari in ɗan fita waje, in zaga gari"
Yusuf yace "bari in bika bana son zaman gidan ne, gara in fita in É—an tattaka"
Saleh yace "kar kasa matarka tamin tijara fa"
Yusuf yai murmushi yace "bakomai"
Suka fito shida Yusuf, Can Saleh ya hango Widad a kusa da Gwaggo suna hira, Widad ta maida hankalinta sosai akan Abunda Gwaggon take yi.
Saleh yace "iko se Allah, da a mafarki aka haskomin wannan abun ze faru, zance sharrin mafarki ne"
Widad ta É—aga ido ta hango Yusuf, ya fito da alama fita za suyi, Widad tace "ya dai, naga ka fito, ina zaka haka?"
"You leave alone in the room, am so boring, Saleh is going out, so i feel like to follow him"
Widad tace "gaskiya ban yadda ba, ka koma ka huta in kuma ka faÉ—i fa?".
"Bazan faÉ—i ba insha Allah, ina son in ga gari ne kawai"
Widad tace "Shikenan, kar kayi nisa dai"
"As you wish your majesty"
Saleh jinjina kai kawai yayi, yayin da Yusuf yake jin wani irin matsanancin tausayinta, ko ya zataji idan taji labarin mahaifinta ya ɓata shima?.
Haka yabi Saleh suka fice.
A harabar gidan su Nurat kuwa, Nurat ce zaune a É—aya daga fararen kujerun dake harabar gidan, ita da Barrister Khalil cousin É—inta, teburin gabansu É—auke da lemu ka da kuma kofunan glass.
Barrister Khalil yace "kince kina son ganina, gashi nazo amma kin kasa cemin komai"
"Brother, aini sam ban san ta ina zan fara maka bama, na rasa me ya kamata ince maka"
"Ki nutsu, ki gayamin komai a hankali, an fahimceki Insha Allah"
Ta ɗanyi ajiyar zuciya sannan tace "brother, game da maganar da mukayi da kaine na belin Anwar" Se kuma tayi shiru.
Khalil yace "Mhmm ina jinki, gayamin ke nake sauraro"
"Barrister, kai ɗan uwana ne, kona ɓoyewa kowa wani abun, kai bazan ɓoye maka ba, amma ina son maganar ta tsaya iya nida kai, ko Kasan akwai hannun mahaifina a cikin abubuwan da suke faruwa da Alhaji Daula?"
A hankali Khalil ya zare glashin fuskarsa, ya kalle ta yace " kamar yaya? Ban gane me kike nufi ba"
'Nasan abun ze baka mamaki, amma kasan Alhaji Daula me silar ɓacin siyasar Mahaifina? "
"Eh na sani, nasan da wannan"
"Mahaifina yayi alwashin ko ze mutu se ya rama abunda Alhaji Daula yayi masa, ya haɗa kai da wasu manyan abokan kasuwancin Alhaji Daula, suna ƙoƙarin ganin bayansa, zancen da nake maka, da saninsa aka sace 'yar gidan Daula da direbanta"
Hankici ya É—akko a aljihunsa ya share gumin fuskarsa yace "wani tabbaci kike dashi, akan wannan maganar da kike yi"
"Brother, nikaɗai ce sheda, se Mummy amma kasan halin Mummy da tsoro, ba zata taɓa bamu goyon baya ba, yanzun kaima ma gaya maka ne, saboda yadda abun ke cin zuciyata, na rasa wa zan gayawa inji daɗi a raina"
Khalil yayi shiru sannan yace "am sorry to say, Nurat mahaifinki gaba É—ayansa zuciyarsa babu Allah a cikinta, yanzu muddin ya gano mum sam me yake yi to tabbas ze É—au mataki a kanmj, nasan shi ba tun yanzu ba"
"Nasani brother, nikaina tunda naje na duba Daula a Asibiti ya samun takunkumi, ya hanani fita, rannan dana fita baka ga yadda ya shaƙeni ba kamar ze kasheni"
Khalil ya jinjina kai yace "yanzu Addu'a zamu ci gaba dayi, mahaifinki yana da goyon bayan manya sosai, dan haka babu wanda ze tsaya ya É—au mataki, sedai muyi ta addu'a"
Nurat tace "hakane Brother, but am so much disturbed wallahi"
"Kakri damu, ki kwantar da hankalinki, Dukda haka zan duba inga me zan iyayi akai"
"Shikenan nagode sosai brother, Allah ya ƙara ɗaukaka"
"Ameen ya Allah karki damu kinji, ki kwantar da hankalinki, komai zezo da sauƙi"
Haka sukka cigaba da tattaunawa.
"Alhaji Musa wai yanzu duk kuna kallo haka É—ana ze cigaba da zama a prison? Ba zakuyi komai akai ba? Na gaji da yawon da kukemin da hankali fa"
Alhaji Musa yace "Ni yanzu me kike son inyine? Nifa bani na sa aka kama É—anki ba, me kike so inyi?"
"Idan ba ku kuka sa aka kamashi ba, amma kuna da ƙarfin da zaku sa a sakarmin shi aiko? Wane irin abune haka, se zarya nake a tsakanin ku, amma kowa da kalar rainin hankalin daze mun"
"Kinga saurara, ni babu abunda zan iyayi akan wannan al'amarin, wannan babban case ne da yake buƙatar bincike, idan bashi da laifi zasu sake shi fa"
Hajiya Halima tace "Shikenan nagode sosai da abunda kukayi min, wato na gama yi muku amfani, zaku watsamin ƙasa a ido, zaku ga abunda zanyi"
Ta juya fuuu tayi waje kamar zata tashi sama, tana tafe tana banbami, ofishin Bulama ta tafi, ta tarar yana shirin fita, ya kalle ta yace "Halima lafiya kuwa?"
"karka ƙara tambaya ta ko lafiya, lafiyar kenan kana nan hankalinka kwance, ni kuma nawa a tashe ko baccin kirki bana samu, na zama kamar mahaukaciya, ɗana yana can a tsare, kun nunamin halin ko in kula, kun nuna baku damu da halin da nake ciki ba"
Bulama yace "Nikam Halima kina bani mamaki, ɗanki fa ɗana ne, nima nawa hankalin ba'a kwance yake ba, muna iya ƙoƙarin mu, amma abunda ake gayamana shine, ana zargin da sa hannun Anwar a wannan abu daya faru, kuma duniya ta kasa kunne taji wani mataki za'a ɗauka, me kike tsammani idan aka ji da sa hannuna aka saki Anwar? "
Widad tace "Toke ya kika gani? A garin nan banda Allah se shi na sani, idan lafiyarsa ta taɓu akwai damuwa sosai"
Gwaggo tace "ƙyaleta Amarya, zolayarki take"
Widad tace "Mama, dan Allah abun nan na É—akinki sunmin kyau sosai"
Gwaggo tace "me fa?"
Widad tace "kwanukan nan da kika shirya a É—akinki, sunyi kyau sosai fa"
Gwaggo tayi murmushi tace "Widad kenan, kayan Su Samira da fanteka kenan, mu dasu mukeyin adon É—aki"
Widad tace "Masha Allah, gaskiya sunmin kyau sosai Mama"
Can ta hango bulugari, a gefen Gwaggo zata kaÉ—a miya.
Widad tace "ya sunan wannan Mama? Wanda kike juya miya dashi"
Gwaggo tace "Bulugari kenan, dashi muke kaÉ—a miya"
"Mama wannan tunkunyar naganta baƙa sosai"
Gwaggo tayi murmushi tace "wannan itace Talle Amarya, tukunya ce ta ƙasa, muna girki a cikinta, miya tafi zaƙi da daɗi Sosai"
Widad tayi murmushi tace "taɓ Mama duk ban san wannan abubuwan ba, ban taɓa ganinsu ba"
Gwaggo tace "hakane dama, tunda ba kuyi rayuwar karkara ba ba lallai ki sansu ba, bari inje É—aki in É—akko abun kaÉ—i"
Gwaggo ta tashi ta tafi, tana tafiya
Hanne tayi tsaki tace "Aikin banza mutum ya zauna yaita ƙarya, mtseww aikin banza dana wofi, wai bata san bulugari da fanteka ba"
Widad ko waigawa ba tayi ba, tai shiru abunta, Hari tace "wato Wudas kinfi jin tsoron Hanne, ta gayamiki duk abunda data ga dama, kiyi ƙus amma da nice da tuni kim hayayyaƙomin"
Wani irin kallo Widad tayi wa Hari, nan take cikin Hari ya kaÉ—a, ganin wani irin kallo da Widad tayi mata, se taga kamar ta canza gaba É—aya daga kamaninta, ba shiri Hari taja bakinta ta tsuke.
Saleh ya kalli Yusuf yace "Sannu Yusuf, gaskiya kana fama, yanzu haka kuke zaune? Tana maka wannan gadarar da jin kan, bayan taimakonta kake"
Yusuf yayi murmushi yace "lafiya ƙalau muke zaune da ita, duk wannan abubuwan bata Yimin, ƙalau muke zaune Alhamdilillah"
Saleh yace "kaga nifa bana son wannan kawaicin naka, kalli yadda take wani bintsire bintsire, tana cin magani, na zata tuni ta dena wannan halin nata?"
Yusuf yace "Kai da ita ta baka amsar wannan tambayar, Amma nan ma shigo ka tarar tana bani Abinci ai"
Saleh yace "kuma fa hakane, lallai kai ɗan baiwa ne kuma na musamman Yusuf, wannan yarinyar me Azabar taurin kai, amma take kula da kai haka, ta yadda ka shiga jikimta gaskiya abun da mamaki, kayi namijin ƙoƙari fa"
Yusuf yayi murmushi yace "Haka lamarin ubangiji yake, yanzu ya jikin mahaifinta?"
Saleh yayi shiru da alama jikinsa yayi sanyi yace "labari mara daɗi Yusuf, yanzu ma badan ka tambaya ba bazan gaya maka ba"
A rikice Yusuf yace "Subhanallah, meyafaru kuma?"
Saleh ya gyara zama ya waiga yaji babu motsin kowa sannan ya waigo ya kalli Yusuf yace "An sace Daula akan gadon Asibiti"
Dafe ƙirji Yusuf yayi yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, kamar yaya?"
Saleh yace "kaima dai ka tambaya, abun kamar almara, Kasan tunda yake rashin lafiya Anwar ne kawai yake sintirin jinyarsa, matarsa da sauran yaran ba ruwansu dashi, daga ya É—an fito daga É—akin, ya koma aka nemi Daula aka rasa, yanzu haka an kama Anwar da me Asibitin ana tuhumarsu, yau sati uku kenan sun tsare "
Dafe kai Yusuf yayi ya shiga murza goshi, wannan wane irin bala'i ne? Duk yadda yake zaton lamarin ya wuce tunaninsa, wane irin tashin hankali ne haka?
Saleh yace " ka kwantar da hankslinka fa, ban gaya maka dan ka É—aga hankalinka ba, sedai ka tayata da Addu'a, sannan karka bari ta sani"
Yusuf yace "kuma ana bincike akan lamarin, ba'a gano inda yake ba?"
Saleh yace "kai dai ayi sha'ani, har yanzu babu Labari"
"Amma naji kamar kace kasan suwaye ke wannan abubuwan"
Saleh yayi murmushi yace "kaifa jami'in tsarone, kuma kai aka bawa wannan aikin na binciken, zuwa yanzu ai nasan ka samu haske akan binciken da kayi"
Yusuf yace "kamar yaya kenan?"
"Kana nufin baka gane me nake nufi ba? Ai shikenan mu bar zancen, kar tazo ta same mu muna maganar"
Yusuf yace "Ya Ummana kuwa Saleh?"
"tana nan lafiya, Suleiman yana kula maka da ita"
"Amma Saleh, Akwai wani abokin aikina Abbas, babban Abokina nane, yana Ibadan akan aiki, ko Suleiman yayi maka maganrsa, nasan idan yasan ina nan Abbas ze shiga damuwa ina da tabbacim se yazo nan"
Ƙura masa ido Saleh yayi, ya ɗanyi shiru sannan yace "gaskiya ba muyi maganar wani da shi ba, kai dai kunci gaba da haƙuri, komai ze wuce kamar ba'ayi ba Insha Allah"
Yusuf yace "Allah yasa"
Saleh yace "bari in ɗan fita waje, in zaga gari"
Yusuf yace "bari in bika bana son zaman gidan ne, gara in fita in É—an tattaka"
Saleh yace "kar kasa matarka tamin tijara fa"
Yusuf yai murmushi yace "bakomai"
Suka fito shida Yusuf, Can Saleh ya hango Widad a kusa da Gwaggo suna hira, Widad ta maida hankalinta sosai akan Abunda Gwaggon take yi.
Saleh yace "iko se Allah, da a mafarki aka haskomin wannan abun ze faru, zance sharrin mafarki ne"
Widad ta É—aga ido ta hango Yusuf, ya fito da alama fita za suyi, Widad tace "ya dai, naga ka fito, ina zaka haka?"
"You leave alone in the room, am so boring, Saleh is going out, so i feel like to follow him"
Widad tace "gaskiya ban yadda ba, ka koma ka huta in kuma ka faÉ—i fa?".
"Bazan faÉ—i ba insha Allah, ina son in ga gari ne kawai"
Widad tace "Shikenan, kar kayi nisa dai"
"As you wish your majesty"
Saleh jinjina kai kawai yayi, yayin da Yusuf yake jin wani irin matsanancin tausayinta, ko ya zataji idan taji labarin mahaifinta ya ɓata shima?.
Haka yabi Saleh suka fice.
A harabar gidan su Nurat kuwa, Nurat ce zaune a É—aya daga fararen kujerun dake harabar gidan, ita da Barrister Khalil cousin É—inta, teburin gabansu É—auke da lemu ka da kuma kofunan glass.
Barrister Khalil yace "kince kina son ganina, gashi nazo amma kin kasa cemin komai"
"Brother, aini sam ban san ta ina zan fara maka bama, na rasa me ya kamata ince maka"
"Ki nutsu, ki gayamin komai a hankali, an fahimceki Insha Allah"
Ta ɗanyi ajiyar zuciya sannan tace "brother, game da maganar da mukayi da kaine na belin Anwar" Se kuma tayi shiru.
Khalil yace "Mhmm ina jinki, gayamin ke nake sauraro"
"Barrister, kai ɗan uwana ne, kona ɓoyewa kowa wani abun, kai bazan ɓoye maka ba, amma ina son maganar ta tsaya iya nida kai, ko Kasan akwai hannun mahaifina a cikin abubuwan da suke faruwa da Alhaji Daula?"
A hankali Khalil ya zare glashin fuskarsa, ya kalle ta yace " kamar yaya? Ban gane me kike nufi ba"
'Nasan abun ze baka mamaki, amma kasan Alhaji Daula me silar ɓacin siyasar Mahaifina? "
"Eh na sani, nasan da wannan"
"Mahaifina yayi alwashin ko ze mutu se ya rama abunda Alhaji Daula yayi masa, ya haɗa kai da wasu manyan abokan kasuwancin Alhaji Daula, suna ƙoƙarin ganin bayansa, zancen da nake maka, da saninsa aka sace 'yar gidan Daula da direbanta"
Hankici ya É—akko a aljihunsa ya share gumin fuskarsa yace "wani tabbaci kike dashi, akan wannan maganar da kike yi"
"Brother, nikaɗai ce sheda, se Mummy amma kasan halin Mummy da tsoro, ba zata taɓa bamu goyon baya ba, yanzun kaima ma gaya maka ne, saboda yadda abun ke cin zuciyata, na rasa wa zan gayawa inji daɗi a raina"
Khalil yayi shiru sannan yace "am sorry to say, Nurat mahaifinki gaba É—ayansa zuciyarsa babu Allah a cikinta, yanzu muddin ya gano mum sam me yake yi to tabbas ze É—au mataki a kanmj, nasan shi ba tun yanzu ba"
"Nasani brother, nikaina tunda naje na duba Daula a Asibiti ya samun takunkumi, ya hanani fita, rannan dana fita baka ga yadda ya shaƙeni ba kamar ze kasheni"
Khalil ya jinjina kai yace "yanzu Addu'a zamu ci gaba dayi, mahaifinki yana da goyon bayan manya sosai, dan haka babu wanda ze tsaya ya É—au mataki, sedai muyi ta addu'a"
Nurat tace "hakane Brother, but am so much disturbed wallahi"
"Kakri damu, ki kwantar da hankalinki, Dukda haka zan duba inga me zan iyayi akai"
"Shikenan nagode sosai brother, Allah ya ƙara ɗaukaka"
"Ameen ya Allah karki damu kinji, ki kwantar da hankalinki, komai zezo da sauƙi"
Haka sukka cigaba da tattaunawa.
"Alhaji Musa wai yanzu duk kuna kallo haka É—ana ze cigaba da zama a prison? Ba zakuyi komai akai ba? Na gaji da yawon da kukemin da hankali fa"
Alhaji Musa yace "Ni yanzu me kike son inyine? Nifa bani na sa aka kama É—anki ba, me kike so inyi?"
"Idan ba ku kuka sa aka kamashi ba, amma kuna da ƙarfin da zaku sa a sakarmin shi aiko? Wane irin abune haka, se zarya nake a tsakanin ku, amma kowa da kalar rainin hankalin daze mun"
"Kinga saurara, ni babu abunda zan iyayi akan wannan al'amarin, wannan babban case ne da yake buƙatar bincike, idan bashi da laifi zasu sake shi fa"
Hajiya Halima tace "Shikenan nagode sosai da abunda kukayi min, wato na gama yi muku amfani, zaku watsamin ƙasa a ido, zaku ga abunda zanyi"
Ta juya fuuu tayi waje kamar zata tashi sama, tana tafe tana banbami, ofishin Bulama ta tafi, ta tarar yana shirin fita, ya kalle ta yace "Halima lafiya kuwa?"
"karka ƙara tambaya ta ko lafiya, lafiyar kenan kana nan hankalinka kwance, ni kuma nawa a tashe ko baccin kirki bana samu, na zama kamar mahaukaciya, ɗana yana can a tsare, kun nunamin halin ko in kula, kun nuna baku damu da halin da nake ciki ba"
Bulama yace "Nikam Halima kina bani mamaki, ɗanki fa ɗana ne, nima nawa hankalin ba'a kwance yake ba, muna iya ƙoƙarin mu, amma abunda ake gayamana shine, ana zargin da sa hannun Anwar a wannan abu daya faru, kuma duniya ta kasa kunne taji wani mataki za'a ɗauka, me kike tsammani idan aka ji da sa hannuna aka saki Anwar? "