Sashe 36
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sosai Yusuf yake ƙara samun haske akan lamarin binciken da yake yi, Sam babu specific lokacin da Widad take bawa Yusuf albashi, duk lokacin da ta bushi Iska sedai yaga alert ɗin kuɗi, kuma kuɗi masu yawa, sannan be isa yayi magana ba.
Yana ta tattara bayananan daze gabatar a gurin aiki na sakamakon binciken da yake yi.
Tunda Yusuf ya tafi Nurat take tunanin, ko ta gayawa Mahaifiyarta yadda suka yi da Yusuf, wata zuciyar ta gargaÉ—e ta akan hakan.
********************************
Gaba É—aya Widad ta takura kanta, sam ko Babban falo bata fitowa, tana iya sashin ta daga ita se magenta, duk da haka Yusuf kullum se yaje koda baze ganta ba kuwa.
Lambar wani abokinsa likita ya dubo a wayarsa ya kirashi, se da ta kusa katsewa sannan ya É—auka.
"Yusuf kana da kirki kuwa? Ace ka ɓata ko neman mutane baka yi?"
Yusuf yace "Amma ka tsaya mu fara gaisawa, sarkin ƙorafi"
Nan suka gaisa suka taɓa hirar yaushe rabo, sannan Yusuf yace "dama doctor Hamza ina da wata 'yar tambaya ne, dukda nasan tambayar da zan maka ba a fannin daka karanta kenan ba, amma na sanka da shige shige"
Hamza yace "shikenan ina jinka, Allah yasa nasan amsar tambayar taka, in babu amsar ma se'a nemo"
'Masha Allah, dan Allah Hamza wace irin larurar ƙwaƙwalwa ce take sa mutum ya dinga gudun mutane? "
Doctor Hamza yace
"Anthropophobia kenan, is a mental disorder, masu irin wannan larurar suna jin tsoron taron mutane, idan abun ya tsananta ma ko ahalinsu basa son su raɓe su, sedai wasu tsirari daga mutane, basu fiye son taron jama'a ba, ko shiga cikin mutane basa so"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "to me yake haddasa ciwon"
Hamza yace "eh to, abun da yake haddassa wannan larurar ga wasu, idan an taɓa cin amanarsu, mussaman wanda suka yadda da shi, ko kuma wani abu da ya taɓa faruwa dasu mara daɗi a rayuwarsu, wasu kuma hormones ne suke haddasa musu excessive fear ya danganta dai, zakaga wataran suna lafiya ƙalau ga wanda ciwon be tsananta a gare su ba, amma idan ya tashi zaka ga basa son haɗa ido da mutane, basa son suga ana kallonsu, kosu kasa bacci, ko yawan ciwon kai, bugun zuciyar su ya canza, wasu numfashinsu har ɗaukewa yake, ko su dinga karkarwa in sunga baƙo, ko wanda basu yadda dashi ba, ko kuma su dinga wrong perception akan abubuwa, ko su dinga ganin duk wanda ya raɓesu ze cutar da sune"
"Ok magana, nagode sosai Hamza amma meye maganin ciwon?"
"gaskiya babu wani sahihin maganin ciwon gaskiya, rehabilitation ne a dinga kwantar musu da hankali tare da ƙoƙarin canza musu tunani daga mummuna zuwa kyakkyawa, dan wasu in damuwar tayi musu yawa suna fara shaye2, ko dinga wasu tunani wanda ya saɓa da abunda yake a zahiri, ayi ƙoƙarin samar da wani abu daze dinga ɗebe musu kewa, koya ɗauke musu hankali daga damuwarsu, in kaga an basu magani mafi akasari sedai a basu magani akan sauran matsala, kamar bugun zuciyar, ko daidaituwar hormones ɗin ko makamancin hakan...
Shiru Yusuf yayi yana tunani, meye alaƙar ƙwayar daya gani a ƙasan kofin shayin da za'a bawa Widad da ciwon nata, Doctor Hamza Yana cikin yiwa Yusuf bayanin ne ya hango Widad ta fito, tana nufo inda yake zaune, gaba ɗaya fuskarta a haɗe kamar kullum, yauma shigar tata da ta saba ita tayi, jikin nan a tsuke a cikin ƙananan kaya.
Da sauri Yusuf yace "shikenan nagode sosai doctor, nagane Allah ya saka da alkhairi" ya katse wayar
Ya shiga wani tunanin, "to wace irin Allura akewa Widad haka? Amal tace masa ana mata wata Allura, ga kuma abunda likita yace"
Ta ƙaraso ta kalle shi a yamutse tace
"É—akko mota, zamu airport ne yanzu"
Ya kalle ta yace
"me zamuje yi a Airport?"
"ban sani ba" ta bashi amsa
Ƙasa yai da idonsa yayi mata wani irin kallo sannan ya miƙe yai gaba, gaba ɗaya kasa gane kalar kallon tayi meya ke nufi da haka?
Ya É—akko mota ya kunna suka fara tafiya, suna tafiya yana satar kallonta yana tunanin, me zeyi wa Widad wanda ze temaka gurin canza tunanin ta mara kyau zuwa me kyau, kamar yadda doctor Hamza ya gaya masa.
Yana cikin tunanin wayarsa ta fara ringing, sedai lambar ba suna, kuma yana tsoron ya ɗaga yaje a cikin abokan aikinsa ne, wani yayi masa kwaɓa, sekuma ya tuna halinta, yanzu yana ƙin ɗaga wayar zata masa wata fassarar, haka ya basar ya ɗaga wayar yasa a kunnen sa tare da yin sallama.
Siririyar muryar mace ce ta amsa tace
"Aboki ya kake?" se yanzu ya gane muryar Nurat, murmushi yayi yace "lafiya ƙalau, light ya kike?"
Wani murmushi ne ya suɓuce mata tace "lafiya ƙalau friend, dama cewa nayi bari in kiraka mu gaisa"
"Amma gaskiya kin kyauta Light, ina fatan kina lafiya ba kya cikin kowace irin damuwa? Kin san damuwa da yawan haɗe rai yana sa mutum ɓacin rai da saurin tsufa, kuma duk kyansa ya koma kamar wani abun tsoro"
Da sauri Widad ta juyo ta kalle shi, amma ya basar ya cigaba da wayar, yayin da Nurat tayi murmushi tace "Ni lafiya ƙalau nake, bani da wata damuwa ko matsala ina Widad?"
"tana gidansu, ko ince kina gaishe ta ne?"
Kamar Yusuf yana ganinta ta girgiza kai tace "Kamanta kace kar in gaya mata muna abota? Na tambayane kawai dan inji ko tana lafiya"
"Eh kuma fa hakane? Amma yaushe zakizo ki ganta?"
"Ai ban san wane irin kallo za tayi min ba idan nazo gidansu, inajin tsoror"
Tsaki Widad tayi ba tare da ta kalli Yusuf ba tace
"Malam ka isheni, ka cikamin kunne"
Murmushi Yusuf yayi yace
"light, se anjima Madam tace na cika mata kunne"
Jiki a sanyaye Nurat tace "Madam kuma? Dama kana da Aurene?"
Yusuf yace "Babba dani kice bani da Aure, ina da Aure mana muna tare da ita ma, munɗan fita ne, se anjima kar in sake ɓata mata rai"
Wani irin wulaƙantaccen kallo Widad tayi masa, dama yasan a rina
"ni kake cewa matarka? Baka da hankaline, ni ka kalleni ka cemin matarka"
"waye cemiki dake nake ne? Am just kidding idan ba haka nayi mata ba zata ga kamar na mata wulaƙanci ne, kuma babu daɗi ka Wulaƙanta mutum it hurts a lot, Yusuf baya Wulaƙanta mutane"
Wani tsakin ta kuma ja ta ɗauke kanta, yayin da shi kuma yayi murmushi, a ransa yace 'Insha Allah, sena canza miki dukkanin wannan gurɓatattun tunanin naki kafin in kammala bincike na"
Gurin wani restaurant sukabi, tace masa ya tsaya ai kuwa yayi parking, tana yi tana duba agogon hannunta, ta buÉ—e motar ta fita, shima ya fito yabi bayanta.
Cikin restaurant É—in ta shiga ta samu guri ta zauna, Yusuf be jira unarninta ba shima yaja kujera ya zauna.
Aka kawo musu menu
(jadawalin Abincin da suke available)
Ta karɓa tana jujjuya menu ɗin, ɗan ɓata fuska tayi ta zaɓi Abunda take so,
Aka bawa Yusuf ma, ya kalli Menu É—in ya girgiza kai yace
"Ni ban iya cin irin wannan Abincin ba gaskiya, Umma ta cika min ciki da É—umamen tuwo dan haka ni ba abunda zanci"
Kallonsa tayi ta ɗauke kanta, yayin da waiter ɗin tayi murmushi ta karɓi menu ɗin ta tafi.
Karon Farko da Yusuf yaga Widad tana cin normal Abinci, sam bata damu da Abinci ba, sedai yaga tana 'yan ciye ciye, ta yaya mutum zeyi lafiya ba tare da cin cikakken Abincin da ze gina masa jiki ba, ko duk cikin rashin yardar ne oho mata.
Yanzun ma ba wani cin Abincin take ba, ɗan cakala take a jikin spoon, kamar wata ƙaramar Yarinya kamar me wasa da Abincin tana kaiwa bakin ta .
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido yace "Madam are you really Hungry?"
Cigaba da cakalar Abincin ta tayi ba tare da ta kula shi ba.
Ko ɗaya bisa ukun Abincin bata ci ba, ko naman kai bata taɓa ba, ta ture Abincin ta ɗau tissue tana goge bakin ta, 'Iko se Allah, Abincin naira dubu huɗu akayi wa wannan cakalar aka barshi, wani yana nan yana fama da Yunwa'
"wai Harkin ƙoshi?"
"wai ina ruwanka dani ne? Ta yaya zan iya cinye wannan Abincin duka?"
"Amma kin san bazaki iya cinyewa ba kika sa aka kawo miki? Akwai dubban marasa ƙarfi da Abincin naira ɗari ma gagarar su yake a rana, kalli uban Abincin da kika bari, wataƙila yanzu wannan da kika rage sedai a zubar, ba kyau Wulaƙanta Abinci, wataran kema ze iya Wulaƙanta ki"
Ko kallonsa ba tayi ba, ta É—auke kanta tana kallon wani gurin, amma tayi shiru tana saurarensa, gefe guda kuma ta shiga tunanin maganar sa, dagaske akwai wanda suke rasa Abincin naira É—ari ya gagare su? To wani irin Abinci ma mutum zeci da naira É—ari, se a samu mutum yace bashi da naira É—ari?.
Yusuf Yaja plate É—in Abincin gabansa ya É—au spoon ya fara cin Abincin da Widad ta rage.
Kallon Yusuf take, sosai mamaki yake bata shi sam be É—au komai da zafi ba, Abincin data rage yake ci, ko dan dai shi talaka ne oho.
Yusuf ba ƙaramin mamaki yake ba yadda take ɗaga masa ƙafa, dan shi kansa yasan wasu lokutan yana wuce gona da iri, tana ƙyaleshi ne kawai
"ya naga kina kallona ko nayi wani abun ne na rashin yadda?"
ÆŠauke idonta tayi daga kallonsa zuwa wani gurin daban.
Yusuf ya ciko spoon yace
"Kinga yadda ake cin Abinci a ciko cokali da Abinci, se mutum ya ƙoshi ba yadda kike yi ba, kamar kina wasan yara, koda yake yarinyar ce ai"
Ɗago ido tayi ta kalle shi, amma ya cigaba da cin Abincin yaƙi kallonta, lallai Yusuf ya samu dama a kanta ya fara rainata, tunda harya samu damar gaya mata maganganun da yaga dama, ita kanta Widad tana mamakin yadda take ƙyale Yusuf, ba yadda za tayi dashi wata ƙaddara me ƙarfi ta shigo dashi cikin rayuwarta, wanda ko dan albarkacin hakan yaci ta dinga ɗaga masa.
Yana ta tattara bayananan daze gabatar a gurin aiki na sakamakon binciken da yake yi.
Tunda Yusuf ya tafi Nurat take tunanin, ko ta gayawa Mahaifiyarta yadda suka yi da Yusuf, wata zuciyar ta gargaÉ—e ta akan hakan.
********************************
Gaba É—aya Widad ta takura kanta, sam ko Babban falo bata fitowa, tana iya sashin ta daga ita se magenta, duk da haka Yusuf kullum se yaje koda baze ganta ba kuwa.
Lambar wani abokinsa likita ya dubo a wayarsa ya kirashi, se da ta kusa katsewa sannan ya É—auka.
"Yusuf kana da kirki kuwa? Ace ka ɓata ko neman mutane baka yi?"
Yusuf yace "Amma ka tsaya mu fara gaisawa, sarkin ƙorafi"
Nan suka gaisa suka taɓa hirar yaushe rabo, sannan Yusuf yace "dama doctor Hamza ina da wata 'yar tambaya ne, dukda nasan tambayar da zan maka ba a fannin daka karanta kenan ba, amma na sanka da shige shige"
Hamza yace "shikenan ina jinka, Allah yasa nasan amsar tambayar taka, in babu amsar ma se'a nemo"
'Masha Allah, dan Allah Hamza wace irin larurar ƙwaƙwalwa ce take sa mutum ya dinga gudun mutane? "
Doctor Hamza yace
"Anthropophobia kenan, is a mental disorder, masu irin wannan larurar suna jin tsoron taron mutane, idan abun ya tsananta ma ko ahalinsu basa son su raɓe su, sedai wasu tsirari daga mutane, basu fiye son taron jama'a ba, ko shiga cikin mutane basa so"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "to me yake haddasa ciwon"
Hamza yace "eh to, abun da yake haddassa wannan larurar ga wasu, idan an taɓa cin amanarsu, mussaman wanda suka yadda da shi, ko kuma wani abu da ya taɓa faruwa dasu mara daɗi a rayuwarsu, wasu kuma hormones ne suke haddasa musu excessive fear ya danganta dai, zakaga wataran suna lafiya ƙalau ga wanda ciwon be tsananta a gare su ba, amma idan ya tashi zaka ga basa son haɗa ido da mutane, basa son suga ana kallonsu, kosu kasa bacci, ko yawan ciwon kai, bugun zuciyar su ya canza, wasu numfashinsu har ɗaukewa yake, ko su dinga karkarwa in sunga baƙo, ko wanda basu yadda dashi ba, ko kuma su dinga wrong perception akan abubuwa, ko su dinga ganin duk wanda ya raɓesu ze cutar da sune"
"Ok magana, nagode sosai Hamza amma meye maganin ciwon?"
"gaskiya babu wani sahihin maganin ciwon gaskiya, rehabilitation ne a dinga kwantar musu da hankali tare da ƙoƙarin canza musu tunani daga mummuna zuwa kyakkyawa, dan wasu in damuwar tayi musu yawa suna fara shaye2, ko dinga wasu tunani wanda ya saɓa da abunda yake a zahiri, ayi ƙoƙarin samar da wani abu daze dinga ɗebe musu kewa, koya ɗauke musu hankali daga damuwarsu, in kaga an basu magani mafi akasari sedai a basu magani akan sauran matsala, kamar bugun zuciyar, ko daidaituwar hormones ɗin ko makamancin hakan...
Shiru Yusuf yayi yana tunani, meye alaƙar ƙwayar daya gani a ƙasan kofin shayin da za'a bawa Widad da ciwon nata, Doctor Hamza Yana cikin yiwa Yusuf bayanin ne ya hango Widad ta fito, tana nufo inda yake zaune, gaba ɗaya fuskarta a haɗe kamar kullum, yauma shigar tata da ta saba ita tayi, jikin nan a tsuke a cikin ƙananan kaya.
Da sauri Yusuf yace "shikenan nagode sosai doctor, nagane Allah ya saka da alkhairi" ya katse wayar
Ya shiga wani tunanin, "to wace irin Allura akewa Widad haka? Amal tace masa ana mata wata Allura, ga kuma abunda likita yace"
Ta ƙaraso ta kalle shi a yamutse tace
"É—akko mota, zamu airport ne yanzu"
Ya kalle ta yace
"me zamuje yi a Airport?"
"ban sani ba" ta bashi amsa
Ƙasa yai da idonsa yayi mata wani irin kallo sannan ya miƙe yai gaba, gaba ɗaya kasa gane kalar kallon tayi meya ke nufi da haka?
Ya É—akko mota ya kunna suka fara tafiya, suna tafiya yana satar kallonta yana tunanin, me zeyi wa Widad wanda ze temaka gurin canza tunanin ta mara kyau zuwa me kyau, kamar yadda doctor Hamza ya gaya masa.
Yana cikin tunanin wayarsa ta fara ringing, sedai lambar ba suna, kuma yana tsoron ya ɗaga yaje a cikin abokan aikinsa ne, wani yayi masa kwaɓa, sekuma ya tuna halinta, yanzu yana ƙin ɗaga wayar zata masa wata fassarar, haka ya basar ya ɗaga wayar yasa a kunnen sa tare da yin sallama.
Siririyar muryar mace ce ta amsa tace
"Aboki ya kake?" se yanzu ya gane muryar Nurat, murmushi yayi yace "lafiya ƙalau, light ya kike?"
Wani murmushi ne ya suɓuce mata tace "lafiya ƙalau friend, dama cewa nayi bari in kiraka mu gaisa"
"Amma gaskiya kin kyauta Light, ina fatan kina lafiya ba kya cikin kowace irin damuwa? Kin san damuwa da yawan haɗe rai yana sa mutum ɓacin rai da saurin tsufa, kuma duk kyansa ya koma kamar wani abun tsoro"
Da sauri Widad ta juyo ta kalle shi, amma ya basar ya cigaba da wayar, yayin da Nurat tayi murmushi tace "Ni lafiya ƙalau nake, bani da wata damuwa ko matsala ina Widad?"
"tana gidansu, ko ince kina gaishe ta ne?"
Kamar Yusuf yana ganinta ta girgiza kai tace "Kamanta kace kar in gaya mata muna abota? Na tambayane kawai dan inji ko tana lafiya"
"Eh kuma fa hakane? Amma yaushe zakizo ki ganta?"
"Ai ban san wane irin kallo za tayi min ba idan nazo gidansu, inajin tsoror"
Tsaki Widad tayi ba tare da ta kalli Yusuf ba tace
"Malam ka isheni, ka cikamin kunne"
Murmushi Yusuf yayi yace
"light, se anjima Madam tace na cika mata kunne"
Jiki a sanyaye Nurat tace "Madam kuma? Dama kana da Aurene?"
Yusuf yace "Babba dani kice bani da Aure, ina da Aure mana muna tare da ita ma, munɗan fita ne, se anjima kar in sake ɓata mata rai"
Wani irin wulaƙantaccen kallo Widad tayi masa, dama yasan a rina
"ni kake cewa matarka? Baka da hankaline, ni ka kalleni ka cemin matarka"
"waye cemiki dake nake ne? Am just kidding idan ba haka nayi mata ba zata ga kamar na mata wulaƙanci ne, kuma babu daɗi ka Wulaƙanta mutum it hurts a lot, Yusuf baya Wulaƙanta mutane"
Wani tsakin ta kuma ja ta ɗauke kanta, yayin da shi kuma yayi murmushi, a ransa yace 'Insha Allah, sena canza miki dukkanin wannan gurɓatattun tunanin naki kafin in kammala bincike na"
Gurin wani restaurant sukabi, tace masa ya tsaya ai kuwa yayi parking, tana yi tana duba agogon hannunta, ta buÉ—e motar ta fita, shima ya fito yabi bayanta.
Cikin restaurant É—in ta shiga ta samu guri ta zauna, Yusuf be jira unarninta ba shima yaja kujera ya zauna.
Aka kawo musu menu
(jadawalin Abincin da suke available)
Ta karɓa tana jujjuya menu ɗin, ɗan ɓata fuska tayi ta zaɓi Abunda take so,
Aka bawa Yusuf ma, ya kalli Menu É—in ya girgiza kai yace
"Ni ban iya cin irin wannan Abincin ba gaskiya, Umma ta cika min ciki da É—umamen tuwo dan haka ni ba abunda zanci"
Kallonsa tayi ta ɗauke kanta, yayin da waiter ɗin tayi murmushi ta karɓi menu ɗin ta tafi.
Karon Farko da Yusuf yaga Widad tana cin normal Abinci, sam bata damu da Abinci ba, sedai yaga tana 'yan ciye ciye, ta yaya mutum zeyi lafiya ba tare da cin cikakken Abincin da ze gina masa jiki ba, ko duk cikin rashin yardar ne oho mata.
Yanzun ma ba wani cin Abincin take ba, ɗan cakala take a jikin spoon, kamar wata ƙaramar Yarinya kamar me wasa da Abincin tana kaiwa bakin ta .
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido yace "Madam are you really Hungry?"
Cigaba da cakalar Abincin ta tayi ba tare da ta kula shi ba.
Ko ɗaya bisa ukun Abincin bata ci ba, ko naman kai bata taɓa ba, ta ture Abincin ta ɗau tissue tana goge bakin ta, 'Iko se Allah, Abincin naira dubu huɗu akayi wa wannan cakalar aka barshi, wani yana nan yana fama da Yunwa'
"wai Harkin ƙoshi?"
"wai ina ruwanka dani ne? Ta yaya zan iya cinye wannan Abincin duka?"
"Amma kin san bazaki iya cinyewa ba kika sa aka kawo miki? Akwai dubban marasa ƙarfi da Abincin naira ɗari ma gagarar su yake a rana, kalli uban Abincin da kika bari, wataƙila yanzu wannan da kika rage sedai a zubar, ba kyau Wulaƙanta Abinci, wataran kema ze iya Wulaƙanta ki"
Ko kallonsa ba tayi ba, ta É—auke kanta tana kallon wani gurin, amma tayi shiru tana saurarensa, gefe guda kuma ta shiga tunanin maganar sa, dagaske akwai wanda suke rasa Abincin naira É—ari ya gagare su? To wani irin Abinci ma mutum zeci da naira É—ari, se a samu mutum yace bashi da naira É—ari?.
Yusuf Yaja plate É—in Abincin gabansa ya É—au spoon ya fara cin Abincin da Widad ta rage.
Kallon Yusuf take, sosai mamaki yake bata shi sam be É—au komai da zafi ba, Abincin data rage yake ci, ko dan dai shi talaka ne oho.
Yusuf ba ƙaramin mamaki yake ba yadda take ɗaga masa ƙafa, dan shi kansa yasan wasu lokutan yana wuce gona da iri, tana ƙyaleshi ne kawai
"ya naga kina kallona ko nayi wani abun ne na rashin yadda?"
ÆŠauke idonta tayi daga kallonsa zuwa wani gurin daban.
Yusuf ya ciko spoon yace
"Kinga yadda ake cin Abinci a ciko cokali da Abinci, se mutum ya ƙoshi ba yadda kike yi ba, kamar kina wasan yara, koda yake yarinyar ce ai"
Ɗago ido tayi ta kalle shi, amma ya cigaba da cin Abincin yaƙi kallonta, lallai Yusuf ya samu dama a kanta ya fara rainata, tunda harya samu damar gaya mata maganganun da yaga dama, ita kanta Widad tana mamakin yadda take ƙyale Yusuf, ba yadda za tayi dashi wata ƙaddara me ƙarfi ta shigo dashi cikin rayuwarta, wanda ko dan albarkacin hakan yaci ta dinga ɗaga masa.