Sashe 43
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yusuf ka fara ƙoƙarin tsallake iyaka, Yusuf meyasa baka tsoron Allah ka dinga nuna kai na Allah ne amma baka kyautawa rayuwarka, Yusuf kai mugune mara tausayi baka da tausayi baka tausayina, ko kaɗan soyayyata bata da daraja a idonka, na rasa meye a tsakaninka da Widad, wallahi akan Son da nake maka banƙi komai ze faru ya faru ba, wallahi akanka koni ko Widad "
Girgiza kai Yusuf yayi yace " keya dace a nemawa maganin mahaukata ai, nayi iya ƙoƙarina in ganar dake amma kin kasa ganewa, bana Soyayya bani da ra'ayinki, ba abunda ya kawoni nan kenan ba, ki ƙyale rayuwar Yusuf ta huta, tun kafin in nuna miki ainihin kalata na gaya miki"
"Haka kace?"
"Eh haka nace, ko baki da kunne ne?"
"bayan ƙalubalen dake gabanka saboda Kasancewar ka da wannan mahaukaciyar, ka shirya ƙalubalen da zaka fuskanta daga gareni"
"duk wanda ya dogara da Allah, to ya isar masa"
Yusuf ya bata amsa yasa kai ya fice, ya barta tana mamakin wannan taurin kai irin na Yusuf.
Bayan Suleiman ya gama nazarin abunda Yusuf ya tura masa, yayi mamakin jajircewa da kuma ƙoƙarin da yayi, tabbas Yusuf jajirtacce ne me kuma hikima da iya aiki, amma meye dalilin da yasa Abbas yakeson lallai a ƙwace aiki a bashi? Lallai akwai wata a ƙasa Abbas yana da fuska biyu.
Yusuf yana nan zaune yana ganin yadda aketa aiken su Murtalah, anata shirye shirye da alama akwai baƙon da gidan zasu tara yau, shi dai yana guri ɗaya nasa ido.
Ƙarfe biyu na rana Yusuf ya dawo daga masallaci sallar Azahar, wata dalleliyar mota ta shigo gidan, wani matashi ne ya fito daga motar, jikinsa sanye da ƙananan kaya kallo ɗaya zaka masa kasan ɗan hutune, ya ɗaga kai ya ƙarewa gidan kallo tsaf, su Isa mai gadi suna gaisheshi yana ɗaga musu hannu ba tare da ya amsa ba.
Shidai Yusuf be kula shi ba, sema É—auke kai da yayi kamar bega Matashin ba, ba zato suka jiyo muryar Ramla ta taho da gudu tana faÉ—in "Oyoyo my heart beat"
Ba kunya suka rungume juna a gurin.
Fahad yace "I miss you so much Baby"
"I miss you too mine" Fahad yayi kissing É—inta a forehead yaceÂ
"kin ƙara kyau my Ramlat"
"Kyau ai kaine ka ƙara kyau, mutanen Amurka muje daga ciki ko"
Suka shige hannunsu saƙale da juna.
Nura direba yayi tsaki yace "ƙaryar banza burodi a lefe, waisu a dole turawa ba kunya taje ta rungume ƙasurgumin gaddi tana ce masa Baby tir da wannan hali"
Shidai Yusuf bece musu komai ba suka ci gaba da gulmarsu.
A babban falon dake ɓangaren Hajiya Halima aka sauki Fahad, suka dinga hira yana basu labarin Anwar shima ya kusa dawowa.
Fahad ya ɗan ɓata fuska yace "Hajiya wai ina Yarinyar take ne? Ance inzo in ganta karta ƙullamin wani sharrin a gurin father ta jamin magana, danni sam ba'a kyautamin ba da'akace zan Aureta"
Æata rai Ramla tayi ta miÆ™e ta bar falon, Hajiya Halima tace "Aikuwa dai an gama da kai, dan yarinya ce ba tarbiyya ga kuma uwa uba hauka"
"wallahi Hajiya na rasa wani irin tunani Daddy yayi haka, da yasa yake son illata rayuwa ta, nazo ne dai kar'ace banzoba amma sena tabattar da na mata rashin mutunci yadda ko ganina tayi ba zata nuna ta sanni ba"
Amal ta kalleshi a yatsine, sam Fahad haushi yake bata yana ta wani iyayi shi lallai ya dawo daga Turai, indai Widad ce ze gane kurensa ne.
Ba kunya Fahad ya miƙe yace "Hajiya bari inje gurin Ramla, naga tayi fushi"
"Shikenan kunfi kusa ai"
A ɗakinta ya sameta tayi kicin kicin da rai, ta haɗe fuska, ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa yace "haba Baby, meye abun damuwa nifa danke nazo gidan nan, ba dan wata banza ba meye na ɓata rai, ki tsaya kiga matakin da zan ɗauka yau akanta"
"Fahad inajin tsaro fa, su Daddy suna san Auren nan naku, zasu iya tursasa maka fa"
"waye ya gaya miki? Kamarni aina wuce ajin amin auren dole, calm down Baby" ya faÉ—a yana jan hancinta
Murmushi Tayi tace "bari in shirya maka Abinci a dining, na maka girki"
Kafin yayi magana wayarsa ta fara ringing yace "excuse me Daddy ne"
Ya ɗaga wayar yasa a kunnensa yace "hello Daddy"
"Fahad kaje gurin nata kuwa?"
"Amm.. Eh ina gidan amma ban ganta ba"
"to ka tsaya ku gaisa, sannan yarinyar nan ka bita a hankali bata da cikakkiyar lafiya, kabi a sannu ka kwantar mata da hankali"
Tura baki Fahada yayi yace "Haba Daddy sekace uwata, yarinyar ma ashe mahaukaciya ce"
"ba zakayi ba kenan?
" Naji zanyi "
" idan naji wani abu na rashin kyautawa daga ɓangarenka sena saɓa maka, shashasha wanda be san halacci ba, aiko wani kaga ze Wulaƙanta 'yar Nasir Daula kai me tare matane"
Bulama yayiwa Fahad tatas sannan ya kashe wayar
Fahad yace "kar wannan abun ya ɗaga miki hankali kinji babyna, ina tare dake, nasan matakin da zan ɗauka"
Ta jinjina masa kai suka fito babban falo, Fahad yace "kiramin ita".
Ramla ta nufi part ɗin Widad, a falonta ta tarar da ita tana kwance a ƙasa ta ɗora ƙafafunta akan kujera, mageneta na kan cikinta a kwance, itakuma tana danna waya.
Ramlah tace "Fahad yazo, yana falo yana jiranki"
Ai kamar da kujerun gurin Ramla ke magana ba da Widad ba, dan ko motsi ba tayi ba.
"Magana fa nake miki"
"And then? Ko bayan hauka kuma inada larurar kurmanta ne? Kinyi magan na jiki kin cigaba da tsayawa a kaina, ki matsa daga kaina"
"Amma se ki bani amsa ai, tunda keba kurma bace"
Miƙewa Zaune Widad tayi tace barmin falo.
"Amma...
" ki fice nace, ko Bulama ne yazo da kansa be isa ya tursasani in saurare shiba, kije ki gaya masa ya cigaba da jira idan ze iya daga nan zuwa lokacin da zan fito, idan baze iyaba ze iya komawa ya tambayi Bulama tsarukana, idan ya shirya É—auka ya sake dawowa, fita ki barmin É—akina"
Buɗe baki Ramla tayi tabi Widad da kallo, wato ita kullum rashin mutuncinta ƙara ta'azzara yake, ina ita ina zuwa ta Sanarwa da Fahad wannan baƙin saƙo, mussman shi dabe san kan Gimbiyar ba.
Ramla ta juya ta fice ta koma main falo tace "Baby naje yanzu ta tashi daga bacci zata shirya ta fito"
Ramla ta zauna a kusa da Fahad suka shiga hirarsu, tun Fahad yana tsammanin fitowar Widad harya fara ƙulewa.
"Ramlah wai yarinyar nan ba zata fito bane?"
"Fahad baka ga komai ba, indai akan wannan Yarinyar ne, idan ka kuskura ka aureta taka ta ƙare wallahi"
"zan saita mata zama kuwa, dan nafi ƙarfin wata banza ta Wulaƙanta ni, bari inje akwai wani friend ɗina a quarters ɗin nan, inaso mu gaisa ina dawowa"
"to ka fara cin Abincin mana"
"karki damu yanzu zanje in dawo"
Ramlah ta rakashi har gaban motarsa, kallo ɗaya Yusuf yayi musu ya ɗauke kai, Fahad yace "Baby wai waye wannan ne?"
Yai maganar yana nuna Yusuf, yamutsa fuska tayi tace "Direban wannan sakaryar ce"
"yanzu wannan ne direba?"
"direba ne, sedai ya samu gindin zama fiye da duk wani me aiki a gidan nan, shiyasa har wani jin kansa yake"
"ku kuka ƙyaleshi baku saita masa zama ba"
"ni yanzu ba shine a gabana ba, kaje kayi sauri ka dawo kaci Abinci"
Suka yi sallama Fahad ya tafi, se bayan ƙarfe huɗu Yusuf yaga message ɗin Widad, ya miƙe ya shiga part ɗinta.
Yau dogon skirt ne a jikinta baƙi, da wata riga me dogon hannu ta ɗora ɗan ƙaramin veil akanta, tayi kyau sosai kayan sun zauna cif a jikinta sedai ana ganin duk wani shape na jikinta.
Tunda Yusuf ya shigo ba tayi magana ba, se sabgar gabanta take yi.
"Ya jikin magenki?" ya tambaye ta
Abunda Yusuf ya faɗa ne yasa ta ɗagowa da sauri tace "i think she got better now, she's able to play"
"Allah ya bata lafiya, na É—auka mutuwa zata yi ashe da sauran kwananta a gaba"
Harar Yusuf tayi ta ɗau jakarta tayi waje, binta yake a hankali baya sauri yana tafiya kamsr kazar da ƙwai ya fashewa a ciki , ta juyo ta kalle shi tace "wannan wace irin tafiya ce kuma?"
"Nifa gaskiya Yunwa nake ji, tun safe ban kuma cin komai ba, kuma kince kar inje ko ina ban samu na fita naci Abinci ba"
Hararasa tayi tai gaba abunta, suna fitowa falo taga an shaƙe kan dining da Kulolin Abinci, wani murmushi tayi ta kalli Yusuf tace "jirani anan"
Ta juya ta koma part É—inta, fitowa tayi hannunta É—auke da magenta ta nufi dining.
Alama ta yiwa Yusuf da hannu yaje, ya nufi kan haɗaɗɗen dining ɗin da'aka shaƙe da kayan Abinci.
Tai masa alama da ya zauna, yaja kujera ya zauna tace "buɗe duk abunda kake so a gurin nan kaci"
Kallonta yay yace "Amma ranki ya daɗe, naga kamar baƙo aka shiryawa teburin
" bana son musu ko jayayya, umarni na baka ba shawararka nake nema ba" ta faÉ—a cikin faÉ—a da bada umarni.
Yusuf ya shiga buÉ—e Kulolin, Abinci ne kala kala kamar ba'asan zafin nema ba, yasan duk tsiya wanda aka shiryawa Abincin baze iya cinyewa ba.
Widad ta zuba kifi akan plate ta miƙawa magenta, Taja plate itama ta ɗiba ta zuba, dama Yusuf yunwa yake ji ga Abinci yayi daɗi nan ya dinga zurawa
(samun guri direba a dining 🤣🤣🤣)
Ramla ce ta fito itada Amal suna magana, me zasu gani Widad da mage ga direbanta suna cin Abincin da'aka shirya karɓar baƙon Ramla sannan baƙon Widad, Amal tayi saroro tana kallon Ramla.
A fusace Ramla ta ƙarasa dining ɗin kamarta fashe da kuka tace "Widad wane irin wulaƙanci ne wannan, ta yaya za'ayiwa baƙo girki ki zauna kina ci naga dai idan munyi Abinci ba ci kike ba, dan kawai ki muzgunamin kika yi haka? Saboda wulaƙanci kuma ace harda direbanki saboda tsabar tozarci"
Girgiza kai Yusuf yayi yace " keya dace a nemawa maganin mahaukata ai, nayi iya ƙoƙarina in ganar dake amma kin kasa ganewa, bana Soyayya bani da ra'ayinki, ba abunda ya kawoni nan kenan ba, ki ƙyale rayuwar Yusuf ta huta, tun kafin in nuna miki ainihin kalata na gaya miki"
"Haka kace?"
"Eh haka nace, ko baki da kunne ne?"
"bayan ƙalubalen dake gabanka saboda Kasancewar ka da wannan mahaukaciyar, ka shirya ƙalubalen da zaka fuskanta daga gareni"
"duk wanda ya dogara da Allah, to ya isar masa"
Yusuf ya bata amsa yasa kai ya fice, ya barta tana mamakin wannan taurin kai irin na Yusuf.
Bayan Suleiman ya gama nazarin abunda Yusuf ya tura masa, yayi mamakin jajircewa da kuma ƙoƙarin da yayi, tabbas Yusuf jajirtacce ne me kuma hikima da iya aiki, amma meye dalilin da yasa Abbas yakeson lallai a ƙwace aiki a bashi? Lallai akwai wata a ƙasa Abbas yana da fuska biyu.
Yusuf yana nan zaune yana ganin yadda aketa aiken su Murtalah, anata shirye shirye da alama akwai baƙon da gidan zasu tara yau, shi dai yana guri ɗaya nasa ido.
Ƙarfe biyu na rana Yusuf ya dawo daga masallaci sallar Azahar, wata dalleliyar mota ta shigo gidan, wani matashi ne ya fito daga motar, jikinsa sanye da ƙananan kaya kallo ɗaya zaka masa kasan ɗan hutune, ya ɗaga kai ya ƙarewa gidan kallo tsaf, su Isa mai gadi suna gaisheshi yana ɗaga musu hannu ba tare da ya amsa ba.
Shidai Yusuf be kula shi ba, sema É—auke kai da yayi kamar bega Matashin ba, ba zato suka jiyo muryar Ramla ta taho da gudu tana faÉ—in "Oyoyo my heart beat"
Ba kunya suka rungume juna a gurin.
Fahad yace "I miss you so much Baby"
"I miss you too mine" Fahad yayi kissing É—inta a forehead yaceÂ
"kin ƙara kyau my Ramlat"
"Kyau ai kaine ka ƙara kyau, mutanen Amurka muje daga ciki ko"
Suka shige hannunsu saƙale da juna.
Nura direba yayi tsaki yace "ƙaryar banza burodi a lefe, waisu a dole turawa ba kunya taje ta rungume ƙasurgumin gaddi tana ce masa Baby tir da wannan hali"
Shidai Yusuf bece musu komai ba suka ci gaba da gulmarsu.
A babban falon dake ɓangaren Hajiya Halima aka sauki Fahad, suka dinga hira yana basu labarin Anwar shima ya kusa dawowa.
Fahad ya ɗan ɓata fuska yace "Hajiya wai ina Yarinyar take ne? Ance inzo in ganta karta ƙullamin wani sharrin a gurin father ta jamin magana, danni sam ba'a kyautamin ba da'akace zan Aureta"
Æata rai Ramla tayi ta miÆ™e ta bar falon, Hajiya Halima tace "Aikuwa dai an gama da kai, dan yarinya ce ba tarbiyya ga kuma uwa uba hauka"
"wallahi Hajiya na rasa wani irin tunani Daddy yayi haka, da yasa yake son illata rayuwa ta, nazo ne dai kar'ace banzoba amma sena tabattar da na mata rashin mutunci yadda ko ganina tayi ba zata nuna ta sanni ba"
Amal ta kalleshi a yatsine, sam Fahad haushi yake bata yana ta wani iyayi shi lallai ya dawo daga Turai, indai Widad ce ze gane kurensa ne.
Ba kunya Fahad ya miƙe yace "Hajiya bari inje gurin Ramla, naga tayi fushi"
"Shikenan kunfi kusa ai"
A ɗakinta ya sameta tayi kicin kicin da rai, ta haɗe fuska, ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa yace "haba Baby, meye abun damuwa nifa danke nazo gidan nan, ba dan wata banza ba meye na ɓata rai, ki tsaya kiga matakin da zan ɗauka yau akanta"
"Fahad inajin tsaro fa, su Daddy suna san Auren nan naku, zasu iya tursasa maka fa"
"waye ya gaya miki? Kamarni aina wuce ajin amin auren dole, calm down Baby" ya faÉ—a yana jan hancinta
Murmushi Tayi tace "bari in shirya maka Abinci a dining, na maka girki"
Kafin yayi magana wayarsa ta fara ringing yace "excuse me Daddy ne"
Ya ɗaga wayar yasa a kunnensa yace "hello Daddy"
"Fahad kaje gurin nata kuwa?"
"Amm.. Eh ina gidan amma ban ganta ba"
"to ka tsaya ku gaisa, sannan yarinyar nan ka bita a hankali bata da cikakkiyar lafiya, kabi a sannu ka kwantar mata da hankali"
Tura baki Fahada yayi yace "Haba Daddy sekace uwata, yarinyar ma ashe mahaukaciya ce"
"ba zakayi ba kenan?
" Naji zanyi "
" idan naji wani abu na rashin kyautawa daga ɓangarenka sena saɓa maka, shashasha wanda be san halacci ba, aiko wani kaga ze Wulaƙanta 'yar Nasir Daula kai me tare matane"
Bulama yayiwa Fahad tatas sannan ya kashe wayar
Fahad yace "kar wannan abun ya ɗaga miki hankali kinji babyna, ina tare dake, nasan matakin da zan ɗauka"
Ta jinjina masa kai suka fito babban falo, Fahad yace "kiramin ita".
Ramla ta nufi part ɗin Widad, a falonta ta tarar da ita tana kwance a ƙasa ta ɗora ƙafafunta akan kujera, mageneta na kan cikinta a kwance, itakuma tana danna waya.
Ramlah tace "Fahad yazo, yana falo yana jiranki"
Ai kamar da kujerun gurin Ramla ke magana ba da Widad ba, dan ko motsi ba tayi ba.
"Magana fa nake miki"
"And then? Ko bayan hauka kuma inada larurar kurmanta ne? Kinyi magan na jiki kin cigaba da tsayawa a kaina, ki matsa daga kaina"
"Amma se ki bani amsa ai, tunda keba kurma bace"
Miƙewa Zaune Widad tayi tace barmin falo.
"Amma...
" ki fice nace, ko Bulama ne yazo da kansa be isa ya tursasani in saurare shiba, kije ki gaya masa ya cigaba da jira idan ze iya daga nan zuwa lokacin da zan fito, idan baze iyaba ze iya komawa ya tambayi Bulama tsarukana, idan ya shirya É—auka ya sake dawowa, fita ki barmin É—akina"
Buɗe baki Ramla tayi tabi Widad da kallo, wato ita kullum rashin mutuncinta ƙara ta'azzara yake, ina ita ina zuwa ta Sanarwa da Fahad wannan baƙin saƙo, mussman shi dabe san kan Gimbiyar ba.
Ramla ta juya ta fice ta koma main falo tace "Baby naje yanzu ta tashi daga bacci zata shirya ta fito"
Ramla ta zauna a kusa da Fahad suka shiga hirarsu, tun Fahad yana tsammanin fitowar Widad harya fara ƙulewa.
"Ramlah wai yarinyar nan ba zata fito bane?"
"Fahad baka ga komai ba, indai akan wannan Yarinyar ne, idan ka kuskura ka aureta taka ta ƙare wallahi"
"zan saita mata zama kuwa, dan nafi ƙarfin wata banza ta Wulaƙanta ni, bari inje akwai wani friend ɗina a quarters ɗin nan, inaso mu gaisa ina dawowa"
"to ka fara cin Abincin mana"
"karki damu yanzu zanje in dawo"
Ramlah ta rakashi har gaban motarsa, kallo ɗaya Yusuf yayi musu ya ɗauke kai, Fahad yace "Baby wai waye wannan ne?"
Yai maganar yana nuna Yusuf, yamutsa fuska tayi tace "Direban wannan sakaryar ce"
"yanzu wannan ne direba?"
"direba ne, sedai ya samu gindin zama fiye da duk wani me aiki a gidan nan, shiyasa har wani jin kansa yake"
"ku kuka ƙyaleshi baku saita masa zama ba"
"ni yanzu ba shine a gabana ba, kaje kayi sauri ka dawo kaci Abinci"
Suka yi sallama Fahad ya tafi, se bayan ƙarfe huɗu Yusuf yaga message ɗin Widad, ya miƙe ya shiga part ɗinta.
Yau dogon skirt ne a jikinta baƙi, da wata riga me dogon hannu ta ɗora ɗan ƙaramin veil akanta, tayi kyau sosai kayan sun zauna cif a jikinta sedai ana ganin duk wani shape na jikinta.
Tunda Yusuf ya shigo ba tayi magana ba, se sabgar gabanta take yi.
"Ya jikin magenki?" ya tambaye ta
Abunda Yusuf ya faɗa ne yasa ta ɗagowa da sauri tace "i think she got better now, she's able to play"
"Allah ya bata lafiya, na É—auka mutuwa zata yi ashe da sauran kwananta a gaba"
Harar Yusuf tayi ta ɗau jakarta tayi waje, binta yake a hankali baya sauri yana tafiya kamsr kazar da ƙwai ya fashewa a ciki , ta juyo ta kalle shi tace "wannan wace irin tafiya ce kuma?"
"Nifa gaskiya Yunwa nake ji, tun safe ban kuma cin komai ba, kuma kince kar inje ko ina ban samu na fita naci Abinci ba"
Hararasa tayi tai gaba abunta, suna fitowa falo taga an shaƙe kan dining da Kulolin Abinci, wani murmushi tayi ta kalli Yusuf tace "jirani anan"
Ta juya ta koma part É—inta, fitowa tayi hannunta É—auke da magenta ta nufi dining.
Alama ta yiwa Yusuf da hannu yaje, ya nufi kan haɗaɗɗen dining ɗin da'aka shaƙe da kayan Abinci.
Tai masa alama da ya zauna, yaja kujera ya zauna tace "buɗe duk abunda kake so a gurin nan kaci"
Kallonta yay yace "Amma ranki ya daɗe, naga kamar baƙo aka shiryawa teburin
" bana son musu ko jayayya, umarni na baka ba shawararka nake nema ba" ta faÉ—a cikin faÉ—a da bada umarni.
Yusuf ya shiga buÉ—e Kulolin, Abinci ne kala kala kamar ba'asan zafin nema ba, yasan duk tsiya wanda aka shiryawa Abincin baze iya cinyewa ba.
Widad ta zuba kifi akan plate ta miƙawa magenta, Taja plate itama ta ɗiba ta zuba, dama Yusuf yunwa yake ji ga Abinci yayi daɗi nan ya dinga zurawa
(samun guri direba a dining 🤣🤣🤣)
Ramla ce ta fito itada Amal suna magana, me zasu gani Widad da mage ga direbanta suna cin Abincin da'aka shirya karɓar baƙon Ramla sannan baƙon Widad, Amal tayi saroro tana kallon Ramla.
A fusace Ramla ta ƙarasa dining ɗin kamarta fashe da kuka tace "Widad wane irin wulaƙanci ne wannan, ta yaya za'ayiwa baƙo girki ki zauna kina ci naga dai idan munyi Abinci ba ci kike ba, dan kawai ki muzgunamin kika yi haka? Saboda wulaƙanci kuma ace harda direbanki saboda tsabar tozarci"