← Book details Akidata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 82

Sashe 47

Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Karki kuma yi masa tsawa, na kuma gayamiki ba zamanki yake ba, idan kika ƙara hukuncin daze biyo baya ka iya ɓatawa kowa rai"  Widad tayi maganar ba tare da kallon Ramla ba.

Anwar yace  "Ramla baki kyauta ba, babu daɗi abunda kikayi fa"

A fusace Mummy tace  "dalla tashi ka wuce ciki, ina magana harda neman guri ka zauna"

Anwar ya miƙe yace  "Widad idan na fito zanzo mu gaisa sosai ki bani sirrin wannan girman naki"

"No need Anwar, yanzu ma mun gaisa yawan shiga harkata ka iya baka matsala da kai da Ahalinka, ina taya ka murnar kammala karatunka, Allah yasa al'umma su amfana"

Tai maganar tana miƙa masa hannu suka gaisa, from no where Yusuf yaji wani takaici ya tokare masa zuciya ganin abunda ya faru.

Mummy ta tasa ahalinta suka shige sashinta, aka bar Yusuf da Widad a falon har ya juya ze fita ya bar falon ya waiwayo, ba zato suka haɗa ido tai saurin ɗauke nata idon daga nasa, a hankali ya dawo ya kalleta yace  "Madam ko baki da lafiya ne?"

Girgiza masa kai tayi tace  "jirani a waje gani nan zamu fita" ya jinjina mata kai ya fita.

Cike da damuwa Anwar yace "Mumsy meyasa bakya son Widad ne? Me tayi mikine haka?"

Ramla tace  "yanzu daka dawo idonka ze gane maka ai"

"kar in sake magana ki samun baki, in bahaka ba sena tattakaki na gaya miki"

Ya maida hankalinsa kan Hajiya Halima yace  "Rayuwar ta abun tausayi ce, tana buƙatar kulawa meyw a ciki dan ki haɗemu gaba ɗaya kin nuna mata kamar ke kika haifeta"

Amal tace  "Taɓɗijan lallai baka san yarinyar nan da taurin kai kamar arnan farko ba, ba mutunci a lamuranta balle tausasawa bata ganin kowa da gashi waye za janyo ta a jiki?"

"Amla yaushe kika koma hakane? Gaba É—aya kun zama fitsararru"

"karka ƙara ce musu fitsararru na gaya maka, bazan riƙe yarinyar da zata nemi ta halakani da baƙinciki ba, bata da tarbiyya sam bata da ɗa'a, shikansa mahaifin nata bata ƙyaleshi ba, weekends ɗin nan Fahad yazo ganin ta za'a haɗasu Aure da shi da ubansa ta haɗa ta wanke su da rashin mutunci tsaf, ubanta ya kirata yayi mata faɗa nan ma ta sake kunyata shi a gaban mutane ta hanyar nuna masa be isa ba"

Cike da ɗimuwa Anwar yace  "wait ji nayi kamar kince za'a haɗata Aurw da Fahad, wani Fahad ɗin wai?"

"Fahad É—in Bulama mana" ta bashi amsa

A diririce yace "Mummy ta yaya haka zata farune? Ita tace tana sonshi? A zatona ai Ramla yake so"

Amla tace  "Ramla yake so, amma babansa da Babanta sukayi ƙarfa ƙarfa sukace zasu aura masa ita, tayi masa rashin mutunci amma yace ba gudu ba ja da baya seya aure ta"

Anwar yace  "Impossible wallahi sedai ayi biyu babu, Fahad yafi kowa sanin yadda nake son yarinyar nan danme zemin haka? Na tabbata da nine bazan masa haka ba, wallahi indai da raina Fahad be isa ba, sedai zumuncin namu ya watse"

"haka nima indai da raina baka isa ka aureta ba, sedai ka canza wata uwar bani ba, dan da hankalina É—ana baze auri dangin mahaukata gadon rashin tarbiyya ba"

Bin mahaifiyar tasa yayi da ido, tare da mamakin wannan magana data fito daga bakinta, be kuma cewa komai ba ya fice cikin hanzari.

Wata katafariyar ma'aikata sukaje, Yusuf yayi mamakin haɗuwa gami da tsaruwar ma'aikatar kamar ba'a ƙasa Nigeria ba, Widad ta dinga ratsawa Yusuf na binta kamar inuwa haka suka isa wani makeken Office.

Kai tsaye ba neman izina ta bankaÉ—a ofishin ta shiga, Bulama ne zaune da É—ansa Fahad suna dudsuba wasu file, Widad ta kallesu tana huci kamar mayuwanciyar Mesa.

"daughter lafiya kuwa?" Bulama ya tambayeta.

"Dole ka tambayi lafiya mana tunda kayi nasarar cusawa mahaifina ra'ayinka wansa yake barazana ga ratuwata, be taɓa fushi dani kamar wannan karon ba yana kallon hawaye akan fuskata amma ya kasa share min hawayen, ya barni tsawon kwanaki ina fama da ƙuncin zuciya "

Bulama yace " Calm down daughter, wannan fa duk ba abun zafi bane, ke kika kambama abun kika maida shi babba, meye laifin Fahad dan an Aure shi? Kuma daba'a aure a haifeki? "

" kai baka ga laifin ɗanka ba ni na gani, bashi da nagartar daze iya zama miji a gare ni, na tsane shi bana sonsa kuma bazan aure shi ba, sannan ka gaggauta zuwa ka janye wannan maganar daga gurin mahaifina ya dena fushi dani, fushinsa yana daga abunda ke jefa zuciyata cikin tashin hankali, be taɓa fushibdanibba se a dalikin wannan gurguwar shawarar taka, bazanyi aure ba ka janye wannan maganar idan ba haka ba Wallahi sena baka mamaki daga kai har ɗan naka"

"Ke jahila!" Fahad ya faɗa tare da yunƙurin kai mata mari, ganin yadda take wa mahaifinsa shouting, sedai ba zato yaji an riƙe hannunsa anyi gefe dashi.

"karka kuskura koda wasa ka kuma yunƙurin ɗaga hannu akanta, koda mafarki kake kaga hakan zata faru kayi duk me yuwuwa kaga ka farka da baccin dan mummunan mafarkine balle a gaske, sannan kasan da kalmomin da zakayi amfani gurin yi mata magana"

Yusuf yayi maganar cikin fushi da harzuƙa, wani irin kwarjini Yusuf yayiwa Fahad, dan a doke tsaf Yusuf ze bazar dashi a gurin.

Bulama yace  "ɗan samari kamar kana zaƙewa fa wasu lokutan"

Yusuf ya saki hannun Fahad cikin ladabi yace  "bahaka bane ranka ya dade, nayi ƙoƙarin hana faruwar tsamin alaƙar daze biyo baya idan har Alhaji Nasir yaji ɗanka ya dakar masa 'ya me"

Bulama yace "koda baka yi hakan ba ni zan É—au mataki Yusuf, bazan bari hakan ta faru ba sam"

Widad tace  "naso ka bari ya dakeni, in sa a nuna masa shi ba komai bane, in nunawa duniya da bazata yake rawa, duk wannan fuffukar da yake da sena nuna masa in ba Widad babu shi, kuma Auren nan dole a fasashi, nazo ne dama dan in muku gargaɗi na ƙarshe a janye maganar nan kafin rugujewar duk wata alaƙa dake tsakaninka da mahaifina"

Sosai Fahad ya dinga huci, a gabansa yarinya ƙarama take cim zarafin mahaifinsa.
Bayan fitarsu Widad, Bulama yayi shiru yana tunani, Fahad yace  "Daddy wannan wace irin dabbar yarinya ce me kyan ɗan maciji, bata da tarbiyya bata da ta ido Sam, ta dubi mutum kamar kai ta dinga gaya masa wannan maganganun, kana kallonta kuma Daddy"

Bulama yayi ajiyar zuciya yace  "daka sake ka daki yarinyar nan da tabbas yanzu wani zancen ake ba wannan ba, koda wasa karka kuskura kayi gangancin cewar zaka dake ta, ta wuce yadda kake tunani, tabbas ba dan inajin nauyin Daula ba da se an fasa Auren nan, dan ina ganin ƙiyayyarka a idonta wanda har hakan yake son ya shafeni"

Fahad ya daki teburi yace  "Nikuma ina sonta a hakan, zan Aure ta koda zata kashe kanta sena Aureta na wulaƙantata na nuna mata ita bakomai bace zanga wanda ze Nasara tsakanin ni da ita"

Bulama ya girgiza kai yace  "Fahad kenan kai kana tunanin zaka iya Wulaƙanta ta idan ka Aureta, dole kayi haƙuri da duk abunda zata aikata maka, zamuyi mata aurene dan samun nutsuwar ta ba dan a muzguna mata ba, shiyasa tun da fari bamu nemi wani bare sekai"

Gajeren tsaki Fahad yayi yaja kujera ya zauna tare da dafe kansa.

Kallonsa take yana tuƙi fuskarsa ɗauke da ɓacin rai, tunani take a duk lokacin da yaga wani na shirin cin zarafinta ko ɓata mata rai se yayi duk me yuwa ya hana faruwar hakan, a duk lokacin da take cikin damuwa zataga damuwa a fuskarsa, wanda ko ɓata masa rai tayi be fiye nuna damuwa haka ba.
Ajiyar zuciya ta sauke seda Yusuf ya juyo ya kalleta yace "lafiya kuwa?"

Ta jinjina masa kai alamar eh, haka suka koma gida ranta a matuƙar ɓace.

Anwar suka gani a harabar gidan, ya ƙaraso da sauri inda take yace  "Widad ina kika jene? Tun ɗazu nake dubaki a gidan nan ban ganki ba" yai maganar cike da damuwa.

Widad tace  "Anwar bana son daga dawowarka ka fara shiga cikin matsalolin gidan nan, zaka fuskanci fushin mahaifiyarka idan haraka cigaba da shiga harkata, am sorry amma kayi harkokinka inyi nawa please"

Ze sake yin magana tayi gaba ta shige ta barshi a gurin, ya kalli Yusuf yace  "ɗan uwa dan Allah meke wakana a gidan nan ne? Ni gaba ɗaya abubuwan mamaki suke bani"

Yusuf yace  "gaskiya nima ban sani ba, tunda nima banfi watanni huɗu da fara aiki a gidan nan ba, bakomai nasani ba, sedai damuwa na damunta sakamakon Auren da za'ayi mata, bata fiye son a shiga harkar ta ba idan tana cikin damuwa shine kawai abunda nasani"

"dan Allah wai dama maganar Auren nan dagaske ne?"

"Eh gaskene" Yusuf ya bashi amsa

"Impossible" Anwar ya faɗa da ɗan ƙarfi

"Ni Fahad zeyi wa haka? Saboda cin amana da wulaƙanci" Anwar ya girgiza kai ya koma cikin gida fuskarsa ɗauke da ɓacin rai.

Washegari da safe Yusuf ya shirya ya fita, seda ya fara biyawa gidan Abbas amma ya tarar baya nan, kamar yaje office amma ya fasa ya wuce gidansu Widad.

"Yusuf gimbiyar masu gida da kanta ta fito nemanka, da alama ka makara fa"

Yusuf yace  "wani abune ya ɗan tsareni, bari inje in ganta"

Murtalah yace  "tana lambu ita da tsuntsayenta da ƙanwarta wato kyanwarta"

Yusuf yayi murmushi ya nufi lambun, kamar yadda Murtalah ya gaya masa tana lambun ita da magenta Roux, magana takewa magen nata kamar da mutum take magana tana cewa

"Roux har yanzu Daddy yana fushi dani, gaba ɗaya duniya tamin zafi, ba wanda ya goyi bayana ko ya tausayawa halin da nake ciki, ba zan iyayiwa Daddy biyayya in Auri Fahad ba, ji nake kamar zuciyata zata tsaya saboda ɓacin rai, amma dole in san hujjar da zan gabatarwa Daddy da zesa a fasa Auren nan, am so much disturbed Roux"

Tana maganar tana shafa jikin magen, yayinda magen tayi luf a jikin Widad kamar tasan me take gaya mata, lokuta da dama Yusuf yana jin Widad tana hira da Mage, hirar da be taɓa jin tana yi da ɗan adam cikin mutuntawa da nutsuwa haka ba.
Chapter 47 · 0% Book details