Sashe 69
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
             PART1
                Page 36_37
Riƙeta gam Yusuf yayi, yayin da ta cigaba da fizge fizge tana kuka, a hankali Yusuf ya zame ya zauna da ita a jikinsa, ya toshe mata baki, saboda dare ne nan da nan sautinta ze iya cika ko'ina.
Yusuf yace "Widad, ki nutsu mana darene yanzu karkisa hankalin mutane ya dawo kanmu, mafarki kikayi fa"
Girgiza masa kai ta shiga yi, cikin kuka tace "is not just a dream, wani abu na shirin faruwa da Daddyna, ka ƙyaleni inje in ganshi, wani abu ze sameshi"
"yanzu idan kika tafi ina zaki? Daddy Addu'ar mu yake buƙata, tun ɗazu nan salla nake ina mana addu'a muda iyayen mu, Insha Allah babu wanda ze iya cutar dasu, kuma Saleh ya cemin ya gaya masa muna nan tare, kidena kuka"
Girgiza kai take tana kuka tace "Daddy na, shikaɗai ya ragemin bani da kowa, bana son in rasa Daddyna, idan na rasa Daddy babu sauran me ƙaunata sedai dukiyar daze bari, wayyo Allah Daddyna, ya Allah secure my Dad, Allah yasa in koma in tarad da kai a raye"
Gaban Yusuf ne ya faÉ—i, ya tuna abunda Saleh ya gaya masa game da mahaifin Widad.
Kuka take sosai jikinta har rawa yake, ga wani irin gumi daya rufe ta, ɗora hannunsa yayi a saman ƙirjinta, se bugawa zuciyarta take da ƙarfin gaske.
Yusuf ya shiga karanta mata dukkan Addu'ar da tazo bakinsa, a hankali zuciyarta ta rage bugawa da sauri da sauri, can kuma bacci ya É—auketa, ta shiga sauke Ajiyar zuciya.
Yusuf ya miƙe a hankali da ita, ya kaita kan katifarta ya rufe ta da bargo, ya koma ya sake alwala ya cigaba da sallar sa.
Alhaji Musane keta sintiri a cikin É—akinsa, se safa da marwa yake ya kai gwauro ya kai mari, ya rasa abunda yake masa daÉ—i, sosai maganganun Saleh sunyi tasiri a zuciyarsa, sosai zargi ya É—arsu a ransa cewar a cikinsu akwai wanda ya zame yake shirin cin amanarsu, kamar yadda ya zame a baya yaso ya haÉ—a kai shida Alhaji Bukar.
A fili ya furta dole "inyi wani abu akai"
Juyowa yayi yaga Nurat a tsaye a ƙofar ɗakinsa da tray ɗauke da kayan marmari a ciki, a fusace yace "dan uwarki laɓe kika koma Yimin ko?"
Cikin dakewa tace "meyasa zan maka laɓe kuma Daddy, tun ɗazu nake sallama amma baka amsa ba"
"Kuma shine seki tsaya ki laɓe?"
"Daddy bafa laɓewa nayi ba"
"zoki ajiye kayan nan ki fita ki ban guri"
Nurat taje ta ajiye masa tray ɗin ta fita, gaba ɗaya Nurat ta lura mahaifinta a kamar a ruɗe yake, akwai abunda yake damunsa, zata so sanin abunda yake damunsa, dan wataƙila yana da alaƙa da harƙallar da suke ƙullawa akan Alhaji Nasir da iyalansa.
Bayan sallar Asuba yau a masallaci, Yusuf ne ya tsaya ya ɗanyi wa mutanen ƙauyen Nasiha akan neman ilimin Addini, ta hanyar janyo musu ayoyi da hadisan manzon Allah salallahu alaihi wassalam, be fito yace musu basu da ilimi ba, amma a cikin bayanin da yake musu ya kawo musu misalin yadda mutum ze kawo raka'oin daya rasa idan yazo bin jam'i, nan suka dinga gano irin tafka tafka da kwaɓar da suke yi.
Wani mutum yace "gaskiya Malam Yusufa munji daɗin wannan bayanin naka, danni harga Allah na ƙaru da abubuwa da dama, danni wallahi na zata idan mutum yayi alwala in yayi tusa indai ba tayi ƙara ba to bata karye ba"
Na kusa dashi yace "Nikuma wallahi na zata ko sujjada ka samu in ana salla shikenan ka samu salla, dan Allah yakamata ka cigaba da yi mana wannan bayanin idan anyi sallar Asuba ko kuma da daddare mudinga taruwa anan kana ƙara fahimtar damu abubuwa"
Megari yace "hakane kam, Yusufa idan bamu takura maka ba, muna buƙatar hakan"
Yusuf yace "Ai babu batun takura ranka ya daÉ—e, mafi alkairin mutane shine wanda yasan ilimi kuma ya sanar dashi"
Seda gari yayi haske tukuna suka watse, suna mamakin kurakuran da suke aikatawa a sha'anin addininsu.
Yana shiga gidan yayi karo da wata budurwa tana koro dabbobi daga turke zasu fita kiwo, tana ganin Yusuf tayi turus tana kallonsa, har Yusuf ze wuce tace masa "Ina kwana"
Yusuf yace "Yawwa lafiya ƙalau sannunki"
Yai gaba abunsa, ƙura masa ido tayi harya wuce ya shige ɗakinsu, anan ta tabattar da cewa shine mijin wannan farar matar me gashi.
Da sauri ta koma É—akinsu, tana kiran "Hindu, Hindu"
Hindu dake sharar ɗaki tace "lafiya kikemin wannan kiran?"
Hanne tace "kinga mijin wannan farar matar nan ta jiya kuwa?"
"me yayi?" hindu ta tambaya
"innalillahi, wallahi ban taɓa ganin namiji me kyau kamarsa ba"
Hindu tace "har LamiÉ—on rigarsu gwaggo?"
Hanne tace "wallahi harshi, taɓ bakiga kyau ba masha Allah, ban taɓa ganin namiji me kyansa ba"
Hindu tace "bakiga matarsa bama, fara me kyau"
Hanne tace "dalla wannan da gani bata da mutunci, kinga kallon da tayi mana jiya kamar taga kashi, da gani bata da mutunci"
Hindu tace "ke Hanne karkice haka, aikinga bata sanmu ba"
Hanne tace "ke dallacan Allah yasa in kuma ganinsa"
Yusuf ya shiga ɗaki ya tarar da Widad a zaune, ya kalleta yace "ina kwana?"
Kallonsa tayi kawai ba tace komai ba, Yusuf yace "Munyi magana da ɗan megari na bashi kuɗi, zeje cikin gari ze siyo miki kayan tea da sauran abun buƙata"
Ita dai ba tace komai ba, sema lumshe idanunta da tayi.
"wai meke damunki ne kuma?"
"Bakomai"
"zakiyi wanka ne? Ina son zan fita"
Tace "kaje kawai, zanyi komai da kaina"
Yusuf yace "Aini tsoron fitarma nakeji, jiya da daddare ki tsoratani sosai, kar in fitane kema kice zaki tafi"
Shiru tayi masa ta ƙara rufe idonta, "Widad" ya kira sunanta, a ɗan hasale tace "meye ne?"
"Inaga bari in haƙura da fitar nan, bari inje inyiwa abokin tafiyar tawa magana se in dawo"
"Nifa ban hanaka tafiya ba, ba inda zani jiyanma na tsorata ne mafarkin da nayi"
Yusuf yace "dagaske idan na fita bazaki tafi ki barni ba"?
ÆŠagowa tayi tana kallon cikin Æ™wayar idonsa, ta jinjina masa kai alamar eh, yayi murmushi yaceÂ
"to bari inje in wanke mana kwanuka, in wanke miki banÉ—aki se in tafi, sena dawo, in a kawo abun karyawa kiyi breakfast É—inki kawai, base kin ragemin ba"
Yai maganar tare da miƙewa ya fice, ya kwashi kwanukan ya zuba ruwa, Hanne ce ta hango Yusuf da kwanuka, ta taho da sauri tace
"kawo in wanke maka"
Yusuf yace "A'a bakomai nagode, yanzu zan wanke in gama"
"dan Allah ka kawo, ai be kamata kayi wanke wanke da kanka ba, idan Baffa ya gani ma ze iyayi mana faÉ—a"
Yusuf yace "kema 'yarsa ce ne?"
Hanne tace "eh nima' yarsa ce nida Hindu, muje wani ƙauyene suna, se jiya muka dawo"
Yusuf yace "Allah sarki, Allah yayiwa rayuwar ku Albarka"
Cike da jin daɗi Hanne tace "Ameen" ta karɓi kwanukan, yace "in kin gama, seki kai mata ɗakin"
Hanne tace "to" tana mamakin ace yana da mata amma shize wanke wanke, Yusuf ya janyo ruwa a rijiya ya wanke banɗakinsu, yayi wanka ya fice.
Hanne ta gama wanke wanke, ta tafi ƙofar ɗakinsu Widad, ta tsaya tana sallama, ƙasa ƙasa Hanne ta shiga ɗakin ta cewa Widad "ga kwanuka inji mijinki"
"Ajiye anan"
Hanne ta ajiye, ta juya ta fita tana mamakin wannan irin nuna isa na Widad.
Anwar ya gayarawa Daula jikinsa, ya canza masa kaya ya bashi Abinci da sirinji, ta cikin robar dake hancin Daula, ya gyara É—akin ya tattara kayansa marasa kyau ya fita ze bayar akai gida su Nura su wanke.
Sufyan ne ya tinkari ɗakin da Alhaji Nasir yake, gaban sa se faɗuwa yake, ji yake kamar kowa kallonsa yake a baranda ya haɗu da Anwar, suka gaisa da Anwar, doctor Sufyan yace "ina zaka haka Anwar? Kasan bama san ana barinsa shi kaɗai"
Anwar yace "yanzu zan koma, kayan nan na fito dashi zan kaiwa direba ya kai gida a wanke"
Sufyan yace "to masha Allah, ga wasu magunguna na rubuta, idan ka kai kayan wankin seka biya pharmacy ka siyo"
Suna nan tsaye aka fito da wani mutum ya mutu an turo shi a gado za'a fita dashi.
Anwar yace "doctor, dan Allah nasan lafiyar Alhaji ba a hannunka take ba tana hannun Allah, dan Allah ka ƙara ƙoƙari, bawan Allah nan kullum jikinsa ƙara rikicewa yake"
Sufyan ya dafa kafaɗar Anwar yace "karka damu Anwar, kamar yadda ka faɗa sauƙi na Allah ne, Amma muna fatan Allah ya bawa Daula lafiya"
Anwar yace "shikenan nagode, bari inje"
Anwar yayi gaba, Sufyan ya tsaya a gurin yayi shiru, sannan yayi gaba jikinsa gaba ɗaya babu ƙwari, a haka ya taka har yaje ƙofar ɗakin da Daula yake, yasa hannu ya murɗa ƙofar ya shiga, sedai me yana shiga yaga wayam ba kowa akan gadon, ya ƙarasa gaban gadon da sauri ya yaye bargon kai, ba Daula babu alamarsa, ya buɗe banɗaki ya duba nan ma kowa, ya duba bayan ƙofa zuwa ƙarƙashin gado, amma be ganshi ba ƙarewa har fridge ya buɗe amma bega alamar Daula ba.
Cire gilashin dake idonsa yayi yana zazzare ido, yana waige waige kamar Æarawo
Fitowa yayi da sauri daga É—akin, aikuwa yayi karo da Anwar, Anwar yace "doctor Sufyan ya dai? Naganka a haka? Na kawo maganin"
Doctor Sufyan yace "Amm... Mmm.. Nace ina Mara lafiyar ne?"
Anwar yace "kamarya? Yana ciki mana"
Sufyan yace "Baya nan na duba ko ina ban ganshi ba"
Anwar yace "kamar yaya? Ya za'ayi in fita barshi, daga zuwa siyo magani kace baka gasnhi ba? Sekace wata eiga, mutumin da komai sena masa ta yaya ze iya fita?"
Sufyan yace  "Nima abunda ya bani mamaki kenan, na duba ko'ina ban ganshi ba, har banɗaki na duba baya nan"
Kallon tuhuma Anwar yayiwa Sufyan yace "Amma gaskiya ni ina tantama, babu wanda ya shiga É—akin bayan fita ta sekai"
Sufyan yace "Wallahi ban tarar dashi a É—akin nan ba kaji na rantse"
                Page 36_37
Riƙeta gam Yusuf yayi, yayin da ta cigaba da fizge fizge tana kuka, a hankali Yusuf ya zame ya zauna da ita a jikinsa, ya toshe mata baki, saboda dare ne nan da nan sautinta ze iya cika ko'ina.
Yusuf yace "Widad, ki nutsu mana darene yanzu karkisa hankalin mutane ya dawo kanmu, mafarki kikayi fa"
Girgiza masa kai ta shiga yi, cikin kuka tace "is not just a dream, wani abu na shirin faruwa da Daddyna, ka ƙyaleni inje in ganshi, wani abu ze sameshi"
"yanzu idan kika tafi ina zaki? Daddy Addu'ar mu yake buƙata, tun ɗazu nan salla nake ina mana addu'a muda iyayen mu, Insha Allah babu wanda ze iya cutar dasu, kuma Saleh ya cemin ya gaya masa muna nan tare, kidena kuka"
Girgiza kai take tana kuka tace "Daddy na, shikaɗai ya ragemin bani da kowa, bana son in rasa Daddyna, idan na rasa Daddy babu sauran me ƙaunata sedai dukiyar daze bari, wayyo Allah Daddyna, ya Allah secure my Dad, Allah yasa in koma in tarad da kai a raye"
Gaban Yusuf ne ya faÉ—i, ya tuna abunda Saleh ya gaya masa game da mahaifin Widad.
Kuka take sosai jikinta har rawa yake, ga wani irin gumi daya rufe ta, ɗora hannunsa yayi a saman ƙirjinta, se bugawa zuciyarta take da ƙarfin gaske.
Yusuf ya shiga karanta mata dukkan Addu'ar da tazo bakinsa, a hankali zuciyarta ta rage bugawa da sauri da sauri, can kuma bacci ya É—auketa, ta shiga sauke Ajiyar zuciya.
Yusuf ya miƙe a hankali da ita, ya kaita kan katifarta ya rufe ta da bargo, ya koma ya sake alwala ya cigaba da sallar sa.
Alhaji Musane keta sintiri a cikin É—akinsa, se safa da marwa yake ya kai gwauro ya kai mari, ya rasa abunda yake masa daÉ—i, sosai maganganun Saleh sunyi tasiri a zuciyarsa, sosai zargi ya É—arsu a ransa cewar a cikinsu akwai wanda ya zame yake shirin cin amanarsu, kamar yadda ya zame a baya yaso ya haÉ—a kai shida Alhaji Bukar.
A fili ya furta dole "inyi wani abu akai"
Juyowa yayi yaga Nurat a tsaye a ƙofar ɗakinsa da tray ɗauke da kayan marmari a ciki, a fusace yace "dan uwarki laɓe kika koma Yimin ko?"
Cikin dakewa tace "meyasa zan maka laɓe kuma Daddy, tun ɗazu nake sallama amma baka amsa ba"
"Kuma shine seki tsaya ki laɓe?"
"Daddy bafa laɓewa nayi ba"
"zoki ajiye kayan nan ki fita ki ban guri"
Nurat taje ta ajiye masa tray ɗin ta fita, gaba ɗaya Nurat ta lura mahaifinta a kamar a ruɗe yake, akwai abunda yake damunsa, zata so sanin abunda yake damunsa, dan wataƙila yana da alaƙa da harƙallar da suke ƙullawa akan Alhaji Nasir da iyalansa.
Bayan sallar Asuba yau a masallaci, Yusuf ne ya tsaya ya ɗanyi wa mutanen ƙauyen Nasiha akan neman ilimin Addini, ta hanyar janyo musu ayoyi da hadisan manzon Allah salallahu alaihi wassalam, be fito yace musu basu da ilimi ba, amma a cikin bayanin da yake musu ya kawo musu misalin yadda mutum ze kawo raka'oin daya rasa idan yazo bin jam'i, nan suka dinga gano irin tafka tafka da kwaɓar da suke yi.
Wani mutum yace "gaskiya Malam Yusufa munji daɗin wannan bayanin naka, danni harga Allah na ƙaru da abubuwa da dama, danni wallahi na zata idan mutum yayi alwala in yayi tusa indai ba tayi ƙara ba to bata karye ba"
Na kusa dashi yace "Nikuma wallahi na zata ko sujjada ka samu in ana salla shikenan ka samu salla, dan Allah yakamata ka cigaba da yi mana wannan bayanin idan anyi sallar Asuba ko kuma da daddare mudinga taruwa anan kana ƙara fahimtar damu abubuwa"
Megari yace "hakane kam, Yusufa idan bamu takura maka ba, muna buƙatar hakan"
Yusuf yace "Ai babu batun takura ranka ya daÉ—e, mafi alkairin mutane shine wanda yasan ilimi kuma ya sanar dashi"
Seda gari yayi haske tukuna suka watse, suna mamakin kurakuran da suke aikatawa a sha'anin addininsu.
Yana shiga gidan yayi karo da wata budurwa tana koro dabbobi daga turke zasu fita kiwo, tana ganin Yusuf tayi turus tana kallonsa, har Yusuf ze wuce tace masa "Ina kwana"
Yusuf yace "Yawwa lafiya ƙalau sannunki"
Yai gaba abunsa, ƙura masa ido tayi harya wuce ya shige ɗakinsu, anan ta tabattar da cewa shine mijin wannan farar matar me gashi.
Da sauri ta koma É—akinsu, tana kiran "Hindu, Hindu"
Hindu dake sharar ɗaki tace "lafiya kikemin wannan kiran?"
Hanne tace "kinga mijin wannan farar matar nan ta jiya kuwa?"
"me yayi?" hindu ta tambaya
"innalillahi, wallahi ban taɓa ganin namiji me kyau kamarsa ba"
Hindu tace "har LamiÉ—on rigarsu gwaggo?"
Hanne tace "wallahi harshi, taɓ bakiga kyau ba masha Allah, ban taɓa ganin namiji me kyansa ba"
Hindu tace "bakiga matarsa bama, fara me kyau"
Hanne tace "dalla wannan da gani bata da mutunci, kinga kallon da tayi mana jiya kamar taga kashi, da gani bata da mutunci"
Hindu tace "ke Hanne karkice haka, aikinga bata sanmu ba"
Hanne tace "ke dallacan Allah yasa in kuma ganinsa"
Yusuf ya shiga ɗaki ya tarar da Widad a zaune, ya kalleta yace "ina kwana?"
Kallonsa tayi kawai ba tace komai ba, Yusuf yace "Munyi magana da ɗan megari na bashi kuɗi, zeje cikin gari ze siyo miki kayan tea da sauran abun buƙata"
Ita dai ba tace komai ba, sema lumshe idanunta da tayi.
"wai meke damunki ne kuma?"
"Bakomai"
"zakiyi wanka ne? Ina son zan fita"
Tace "kaje kawai, zanyi komai da kaina"
Yusuf yace "Aini tsoron fitarma nakeji, jiya da daddare ki tsoratani sosai, kar in fitane kema kice zaki tafi"
Shiru tayi masa ta ƙara rufe idonta, "Widad" ya kira sunanta, a ɗan hasale tace "meye ne?"
"Inaga bari in haƙura da fitar nan, bari inje inyiwa abokin tafiyar tawa magana se in dawo"
"Nifa ban hanaka tafiya ba, ba inda zani jiyanma na tsorata ne mafarkin da nayi"
Yusuf yace "dagaske idan na fita bazaki tafi ki barni ba"?
ÆŠagowa tayi tana kallon cikin Æ™wayar idonsa, ta jinjina masa kai alamar eh, yayi murmushi yaceÂ
"to bari inje in wanke mana kwanuka, in wanke miki banÉ—aki se in tafi, sena dawo, in a kawo abun karyawa kiyi breakfast É—inki kawai, base kin ragemin ba"
Yai maganar tare da miƙewa ya fice, ya kwashi kwanukan ya zuba ruwa, Hanne ce ta hango Yusuf da kwanuka, ta taho da sauri tace
"kawo in wanke maka"
Yusuf yace "A'a bakomai nagode, yanzu zan wanke in gama"
"dan Allah ka kawo, ai be kamata kayi wanke wanke da kanka ba, idan Baffa ya gani ma ze iyayi mana faÉ—a"
Yusuf yace "kema 'yarsa ce ne?"
Hanne tace "eh nima' yarsa ce nida Hindu, muje wani ƙauyene suna, se jiya muka dawo"
Yusuf yace "Allah sarki, Allah yayiwa rayuwar ku Albarka"
Cike da jin daɗi Hanne tace "Ameen" ta karɓi kwanukan, yace "in kin gama, seki kai mata ɗakin"
Hanne tace "to" tana mamakin ace yana da mata amma shize wanke wanke, Yusuf ya janyo ruwa a rijiya ya wanke banɗakinsu, yayi wanka ya fice.
Hanne ta gama wanke wanke, ta tafi ƙofar ɗakinsu Widad, ta tsaya tana sallama, ƙasa ƙasa Hanne ta shiga ɗakin ta cewa Widad "ga kwanuka inji mijinki"
"Ajiye anan"
Hanne ta ajiye, ta juya ta fita tana mamakin wannan irin nuna isa na Widad.
Anwar ya gayarawa Daula jikinsa, ya canza masa kaya ya bashi Abinci da sirinji, ta cikin robar dake hancin Daula, ya gyara É—akin ya tattara kayansa marasa kyau ya fita ze bayar akai gida su Nura su wanke.
Sufyan ne ya tinkari ɗakin da Alhaji Nasir yake, gaban sa se faɗuwa yake, ji yake kamar kowa kallonsa yake a baranda ya haɗu da Anwar, suka gaisa da Anwar, doctor Sufyan yace "ina zaka haka Anwar? Kasan bama san ana barinsa shi kaɗai"
Anwar yace "yanzu zan koma, kayan nan na fito dashi zan kaiwa direba ya kai gida a wanke"
Sufyan yace "to masha Allah, ga wasu magunguna na rubuta, idan ka kai kayan wankin seka biya pharmacy ka siyo"
Suna nan tsaye aka fito da wani mutum ya mutu an turo shi a gado za'a fita dashi.
Anwar yace "doctor, dan Allah nasan lafiyar Alhaji ba a hannunka take ba tana hannun Allah, dan Allah ka ƙara ƙoƙari, bawan Allah nan kullum jikinsa ƙara rikicewa yake"
Sufyan ya dafa kafaɗar Anwar yace "karka damu Anwar, kamar yadda ka faɗa sauƙi na Allah ne, Amma muna fatan Allah ya bawa Daula lafiya"
Anwar yace "shikenan nagode, bari inje"
Anwar yayi gaba, Sufyan ya tsaya a gurin yayi shiru, sannan yayi gaba jikinsa gaba ɗaya babu ƙwari, a haka ya taka har yaje ƙofar ɗakin da Daula yake, yasa hannu ya murɗa ƙofar ya shiga, sedai me yana shiga yaga wayam ba kowa akan gadon, ya ƙarasa gaban gadon da sauri ya yaye bargon kai, ba Daula babu alamarsa, ya buɗe banɗaki ya duba nan ma kowa, ya duba bayan ƙofa zuwa ƙarƙashin gado, amma be ganshi ba ƙarewa har fridge ya buɗe amma bega alamar Daula ba.
Cire gilashin dake idonsa yayi yana zazzare ido, yana waige waige kamar Æarawo
Fitowa yayi da sauri daga É—akin, aikuwa yayi karo da Anwar, Anwar yace "doctor Sufyan ya dai? Naganka a haka? Na kawo maganin"
Doctor Sufyan yace "Amm... Mmm.. Nace ina Mara lafiyar ne?"
Anwar yace "kamarya? Yana ciki mana"
Sufyan yace "Baya nan na duba ko ina ban ganshi ba"
Anwar yace "kamar yaya? Ya za'ayi in fita barshi, daga zuwa siyo magani kace baka gasnhi ba? Sekace wata eiga, mutumin da komai sena masa ta yaya ze iya fita?"
Sufyan yace  "Nima abunda ya bani mamaki kenan, na duba ko'ina ban ganshi ba, har banɗaki na duba baya nan"
Kallon tuhuma Anwar yayiwa Sufyan yace "Amma gaskiya ni ina tantama, babu wanda ya shiga É—akin bayan fita ta sekai"
Sufyan yace "Wallahi ban tarar dashi a É—akin nan ba kaji na rantse"