Sashe 59
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka Widad ta kwanta akan katifar, Yusuf ya ɗau bargo ɗaya ya koma bakin ƙofa ya shimfiɗa ya kwanta, shiru Widad ta kasa bacci, tana tunanin wai itace zata kwana a gurin nan, ga sauro se kururuwa yake mata a kunne, ga zafi ga jikinta da yake ciwo, ga rashin lafiya tana fama.
Æangaren Yusuf ma shiru Yayi yana saÆ™e saÆ™e, yana tunanin wani hali Ummansa take ciki, yasan duk inda take hankalin ta a tashe yake, dan tun tasowarsa be taÉ“a nesa da ita ba, wani É“angare na zuciyar sa yana tunanin Alhaji Nasir yasan tabbas shima yana cikin damuwa, ko wani haki yake ciki Allah masani, ga zamansa da Widad a É—aki É—aya baze yuwu ba, tunda ba muharramarsa bace, gashi ba ta yadda da kowa se shi, ga wasu abubuwan se anyi mata saboda bata da lafiya, dole idan Saleh yazo yayi masa magana asama masa wani É—akin, dan gudun afkawa tarkon sheÉ—an.
Yana nan kwancw sauro yana cizonsa, yana masa hada hada aka, ga cinnaka da yake ta gasa masa cizo a gurin nan, tunani yake Allah yasa kae cinnakan ya ciji Widad.
Katsam ya jiyo sheshsheƙar Widad tana kuka, da yayi kamar ya basar amma ya dinga jin kukan nata a zuciyar sa, tabbas yakamata a tausaya mata.
Ɗakin baƙiƙirin da duhu, ko tafin hannu ba'a iya gani saboda duhu, haka yaja jikinsa cikin lalube yaje gefen katifar ta yace "uwa ɗakina kukan me kike?"
Maimakon tayi magana seta sake fashewa da kuka, Yusuf yace "Am sorry, i feel your pain kiyi haƙuri ki karɓi hakan a matsayin ƙaddarar mu, yakamata ki gode Allah da yasa muka tsira daga hannun mutanen nan, kuma insha Allah zamu koma gida ki dena kuka, kiyi bacci zaki ji daɗin jikin ki"
"I can't sleep, sauro ya dameni zafi nake ji, kuma ina tunanin Daddy na"
Tai maganar tana sake fashewa da kuka.
"kiyi hakuri, Insha Allah Daddy yana nan lafiya, komai ze wuce kamar be faru ba, ki dena kuka kinga baki da lafiya"
Ajiyar zuciya kawai tayi, ta lumshe idinta tana jin yadda zuciyarta ke raÉ—aÉ—i.
Da Asuba yayi Alwala yazo ya tada Salla, bacci take dan sam bata samu bacci ba da daddare, seda ya idar sannan ya tashe ta ya kaita tayi alwala tazo ta tada salla.
Da gari ya fara haske me gari da kansa yayi sallama a ƙofar ɗakin su Yusuf, Yusuf ya fita ya durƙusa ya gaishe shi.
Ya amsa cikin mutuntawa yace "Ya me jikin kuwa?"
Yusuf yace "Jikinta da sauƙi Alhamdilillah"
"Masha Allah, Allah ya ƙara afuwa ya bata lafiya, karkaji komai ku saki jikinku duk abunda kuke buƙata kuyi magana insha Allah baze gagara ba"
Yusuf yace "Masha Allah, mungode sosai da wannan karamcin naku"
"Karka damu, ai shi É—a na kowa ne"
Wajejen ƙarfe tara na Safe aka aiko yaro ya kawowa Su Yusuf Koko me zafi da ɗumamen tuwo, Yusuf ya karɓa yace sun gode.
Ya kalli Widad dake zaune tayi shiru, gwanin ban tausayi yace "ga Abinci an kawo, ki daure kici se Kisha magani"
Kallon kwanon tuwon tayi, sannan ta kalli kwanon da'aka zubo kokon, har ɗan gara kwanon kokon, amma na tuwon dai se a hankali ga warin daddawar nan ji tayi kamar tayi amai, miyar nan baƙa wuluk ga uban tuwo a ido in ka kalli Tuwon nan kasan ze azabar tauri.
Ta kalli kokon tana tunanin ta ina zata sha abun sha a cikin kwano, ta kalli Yusuf tace "janye min wannan baƙin Abincin kar inyi amai"
Kallonta yayi da mamaki, tuwon ne bata sani ba ko kuma tsabar rainin hankali ne? Ta miƙa hannu ta ɗau kwanon kokon, ta dinga juya kwanon sannan ta kai bakin ta, karɓa ɗaya tayi ta dire kwanon ta yamutsa fuska kamar zata yi kuka.
Yusuf yace "ya dai?"
"Ba daÉ—i" ta bashi amsa
"to ai badan daÉ—i zaki sha ba, kinga nan ba kamar gida bane da zakici abunda kike so, ki daure kisha"
Banza tayi masa taƙi kallonsa, ya ɗau kwanon ya zuƙi kokon, kokon dawane kuma gasarar tayi tsami dan ta ɗan fara wari ma, gashi babu ko ɗigon sugar a ciki.
Yusuf yace "kinga babu wani Abincin da zan baki, idan baki sha ba babu wani Abincin da zaki samu kici, ki daure ki É—auke numfashi kawai kisha"
Da ƙyar ya lallaɓata ta sha kokon nan shima kaɗan ta sha tace ita ta ƙoshi, sannan ya bata magungunanta.
Yusuf yace "Inaga yakamata inyi musu magana, idan da hali a bani ɗakin da zan dinga kwana, kinga be dace mudinga kwana a ɗaki ɗaya nida ke ba, sannan dole kiyi haƙuri su ɗan dinga temaka miki ko gurin wankan ne da canza kaya, nida nake miki be dace ba, tunda ba muharrama tace keba"
Da sauri ta kalle shi tace "NikaÉ—ai zan dinga kwana a É—akin nan? Ni gaskiya bazan iya ba"
"to se a samu a yaran gidan wasu su dinga ta yaki kwana"
Ai tuni ta fara kuka tace "Ni wallahi ba wanda nasani a gurin nan ba zaka tafi ka barni a ɗakin nan ba, kuma wallahi niba zasu dinga taɓani ba, wannan matar me haƙora tsoro take bani, in ba haka ba kawai ka maida ni gida"
Yusuf ya ƙara kwantar da murya yace "Widad mufa musulmi ne, mun san illar zaman mu a guri ɗaya, bekamata yadda nake kula dake ba bayan ga 'yan uwanki mata a gidan nan ba"
"to ni ka maida ni gida mana, kkme ze faru ya faru amma wallahi ba inda zaka tafi ka barni".
"so kike mu koma gida wani abu
ya sameki?
" Idan ba zamu koma gida ba, to bazaka bar É—akin nan ba, in ba haka ba ni zan tafi gidan nikaÉ—ai "
"Amma kin san zamana dake a ɗaki ɗaya ya saɓawa shari'ar musulunci?"
Shiru tayi bata ce komai ba, Yusuf yace "kiyi haƙuri, mutan gidan nan suna da kirki kuma duk mutane ne, babu wanda ze cutar dake, kiyi haƙuri zanje in samu me garin muyi magana"
Riƙo rigar Yusuf tayi ta fashe da kuka tace "Wallahi bazan dinga zama a ɗakin nan nikaɗai ba, sedai duk inda zaka in bika"
Shiru yayi yana Kallonta, kuka take sosai har cikin ranta, tabbas yasan halinta da ƙyanƙyami da rashin yadda, ba zata yadda ta zauna da kowa a ɗaki ɗaya ba in bashi ba, kuma gashi hakan ya haramta.
Jiki a sanyaye yace "shikenan is ok kidena kuka, idan har kina son mu cigaba da zama tare a ɗakin nan inyi jinyarki bisa shari'a mafita ɗaya ce, kuma mafitar nasan me tsaurin gaske ce a gurinki ba lallai ki yadda ba"
Widad ta É—ago idonta tace "Meye mafitar?"
Yusuf yace " Sedai ki amince muyi Aure zuwa lokacin da zaki warke, mu koma gida semu rabu"
Gaban Widad ne ya faÉ—i ta tsaya tana masa wani irin kallo
Duk yadda me Adda yake tunanin lamarin ya wuce tunaninsa, dan babu wata alama ko sheda da zata nuna maka inda su Yusuf sukabi, suka yi sintiri da neman duniya a dajin nan basu sami su Yusuf ba, me Adda yace "gaskiya ina mamakin guduwar mutanen nan, tabbas akwai munafiki a cikinmu, wanda ya kuɓutar dasu banda haka yaza'ayi mutanen da ko tashi basa iyawa ace sun gudu?"
"Oga nima dai nayi wannan tunanin, dan tabbas maganar ka haka take, da saka hannun wani a kuɓutar tasu"
Me Adda yace "Ni yanzu tunanina yadda zanwa wannan mutanen bayanin sun ɓata, dan wallahi babu lallai su ƙyalemu"
"To Oga ko muma sanfewa za muyi muyi ta kanmu"
Me Adda yace "ƙwarai kuwa, Amma zamu fara kiransu mu gaya musu su san meya dace suyi, sannan muma muyi ta kanmu da ba mutunci mutanen nan suka cika ba"
Suleiman shike zuwa ya rarrashi Maman Yusuf, dan ko Abinci bata iya ci, sedai wataran inzeje yayi mata Nasiha ya sai wani abun ya kai mata.
Yauma bayan Azahar da ya taso daga gurin aiki gidan su Yusuf yaje, yatarar da Umman Yusuf akan dadduma taci kuka ta ƙoshi, idanunta duk sunyi jawur.
Suka gaisa Suleiman yace "Umma har yanzu baki dena kukan ba? Ki sani wannan carbin da kike ja kina masa Addu'a yafi wannan kukan da kike yi, dan Allah ki kwantar da hankalinki, kar wani ciwon ya shige ki"
Umman Yusuf tace "To Suleiman dangana ta zama dole, yau da gawar Yusuf na gani seta fiyemin kwanciyar hankali akan ɓatansa, ban san a ina yake ba, yaci Abinci? Yayi wanka? Me yake ciki? Yana samun Abincin da yake so duk ban sani ba, Allah ne kawai ya barwa kansa sani, dole in shiga damuwa inyi kuka"
Suleiman yace "hakane Umma, amma ki kwantar da hankalinki, muna nan muna bincike akan mu gano inda Yusuf yake, very soon zakiji labari me daɗi, kuma kisawa zuciyarki addu'ar nan da kike tana isa ga Yusuf insha Allah muna sa ran jin labari me daɗi akan Yusuf"
Umman Yusuf tace "Nagode Suleiman, Allah ya saka da alkhairi tunda abun nan ya faru kai kaÉ—ai kake zuwa inda nake ka rarrashenin, Nagode Allah yayi Albarka"
Suleiman yace "Ameen Umma, kin san mahaifin yarinyar ma yana can a gadon Asibiti, sedai fatan Allah ya bayyanasu"
Umma ta amsa da Ameen.
Nurat ta kuma satar jiki, mahaifiyarta bata sani ba ta tafi Asibiti duba jikin Baban Widad, koda taje Anwar kawai ta gani a gurinsa, sedai abun mamaki har yana zaune yana cin Abinci da kansa.
Nurat tace "Alhamdilillah lafiya ta fara samuwa, ya ƙarfin jiki kuwa Daddy?"
Daula yayi murmushi yace "Alhamdilillah, yau gani a zaune ina cin Abinci ma"
Nurat tace "Alhamdilillah"
Ta kalli Anwar tace "Yaya Anwar ina kwana"
Anwar yace "lafiya ƙalau, ya mutan gidan?"
"duk suna lafiya Alhamdilillah, Amma ina su Anty Ramlah ne?"
Ɗan kame kame Anwar ya fara yace "kin san da yake tunda Daddy ya kwanta itama taƙi lafiya, tana can tana jinya su Amal ke kula da ita"
Nurat tace "Allah sarki, Allah ya sawwake naje in duba ta"
Saleh ne yayi sallama ya shigo, yana ganin Daula a zaune yace "Alhamdilillah Alhajin Allah, kaine a zaune haka kake cin Abinci?"
Æangaren Yusuf ma shiru Yayi yana saÆ™e saÆ™e, yana tunanin wani hali Ummansa take ciki, yasan duk inda take hankalin ta a tashe yake, dan tun tasowarsa be taÉ“a nesa da ita ba, wani É“angare na zuciyar sa yana tunanin Alhaji Nasir yasan tabbas shima yana cikin damuwa, ko wani haki yake ciki Allah masani, ga zamansa da Widad a É—aki É—aya baze yuwu ba, tunda ba muharramarsa bace, gashi ba ta yadda da kowa se shi, ga wasu abubuwan se anyi mata saboda bata da lafiya, dole idan Saleh yazo yayi masa magana asama masa wani É—akin, dan gudun afkawa tarkon sheÉ—an.
Yana nan kwancw sauro yana cizonsa, yana masa hada hada aka, ga cinnaka da yake ta gasa masa cizo a gurin nan, tunani yake Allah yasa kae cinnakan ya ciji Widad.
Katsam ya jiyo sheshsheƙar Widad tana kuka, da yayi kamar ya basar amma ya dinga jin kukan nata a zuciyar sa, tabbas yakamata a tausaya mata.
Ɗakin baƙiƙirin da duhu, ko tafin hannu ba'a iya gani saboda duhu, haka yaja jikinsa cikin lalube yaje gefen katifar ta yace "uwa ɗakina kukan me kike?"
Maimakon tayi magana seta sake fashewa da kuka, Yusuf yace "Am sorry, i feel your pain kiyi haƙuri ki karɓi hakan a matsayin ƙaddarar mu, yakamata ki gode Allah da yasa muka tsira daga hannun mutanen nan, kuma insha Allah zamu koma gida ki dena kuka, kiyi bacci zaki ji daɗin jikin ki"
"I can't sleep, sauro ya dameni zafi nake ji, kuma ina tunanin Daddy na"
Tai maganar tana sake fashewa da kuka.
"kiyi hakuri, Insha Allah Daddy yana nan lafiya, komai ze wuce kamar be faru ba, ki dena kuka kinga baki da lafiya"
Ajiyar zuciya kawai tayi, ta lumshe idinta tana jin yadda zuciyarta ke raÉ—aÉ—i.
Da Asuba yayi Alwala yazo ya tada Salla, bacci take dan sam bata samu bacci ba da daddare, seda ya idar sannan ya tashe ta ya kaita tayi alwala tazo ta tada salla.
Da gari ya fara haske me gari da kansa yayi sallama a ƙofar ɗakin su Yusuf, Yusuf ya fita ya durƙusa ya gaishe shi.
Ya amsa cikin mutuntawa yace "Ya me jikin kuwa?"
Yusuf yace "Jikinta da sauƙi Alhamdilillah"
"Masha Allah, Allah ya ƙara afuwa ya bata lafiya, karkaji komai ku saki jikinku duk abunda kuke buƙata kuyi magana insha Allah baze gagara ba"
Yusuf yace "Masha Allah, mungode sosai da wannan karamcin naku"
"Karka damu, ai shi É—a na kowa ne"
Wajejen ƙarfe tara na Safe aka aiko yaro ya kawowa Su Yusuf Koko me zafi da ɗumamen tuwo, Yusuf ya karɓa yace sun gode.
Ya kalli Widad dake zaune tayi shiru, gwanin ban tausayi yace "ga Abinci an kawo, ki daure kici se Kisha magani"
Kallon kwanon tuwon tayi, sannan ta kalli kwanon da'aka zubo kokon, har ɗan gara kwanon kokon, amma na tuwon dai se a hankali ga warin daddawar nan ji tayi kamar tayi amai, miyar nan baƙa wuluk ga uban tuwo a ido in ka kalli Tuwon nan kasan ze azabar tauri.
Ta kalli kokon tana tunanin ta ina zata sha abun sha a cikin kwano, ta kalli Yusuf tace "janye min wannan baƙin Abincin kar inyi amai"
Kallonta yayi da mamaki, tuwon ne bata sani ba ko kuma tsabar rainin hankali ne? Ta miƙa hannu ta ɗau kwanon kokon, ta dinga juya kwanon sannan ta kai bakin ta, karɓa ɗaya tayi ta dire kwanon ta yamutsa fuska kamar zata yi kuka.
Yusuf yace "ya dai?"
"Ba daÉ—i" ta bashi amsa
"to ai badan daÉ—i zaki sha ba, kinga nan ba kamar gida bane da zakici abunda kike so, ki daure kisha"
Banza tayi masa taƙi kallonsa, ya ɗau kwanon ya zuƙi kokon, kokon dawane kuma gasarar tayi tsami dan ta ɗan fara wari ma, gashi babu ko ɗigon sugar a ciki.
Yusuf yace "kinga babu wani Abincin da zan baki, idan baki sha ba babu wani Abincin da zaki samu kici, ki daure ki É—auke numfashi kawai kisha"
Da ƙyar ya lallaɓata ta sha kokon nan shima kaɗan ta sha tace ita ta ƙoshi, sannan ya bata magungunanta.
Yusuf yace "Inaga yakamata inyi musu magana, idan da hali a bani ɗakin da zan dinga kwana, kinga be dace mudinga kwana a ɗaki ɗaya nida ke ba, sannan dole kiyi haƙuri su ɗan dinga temaka miki ko gurin wankan ne da canza kaya, nida nake miki be dace ba, tunda ba muharrama tace keba"
Da sauri ta kalle shi tace "NikaÉ—ai zan dinga kwana a É—akin nan? Ni gaskiya bazan iya ba"
"to se a samu a yaran gidan wasu su dinga ta yaki kwana"
Ai tuni ta fara kuka tace "Ni wallahi ba wanda nasani a gurin nan ba zaka tafi ka barni a ɗakin nan ba, kuma wallahi niba zasu dinga taɓani ba, wannan matar me haƙora tsoro take bani, in ba haka ba kawai ka maida ni gida"
Yusuf ya ƙara kwantar da murya yace "Widad mufa musulmi ne, mun san illar zaman mu a guri ɗaya, bekamata yadda nake kula dake ba bayan ga 'yan uwanki mata a gidan nan ba"
"to ni ka maida ni gida mana, kkme ze faru ya faru amma wallahi ba inda zaka tafi ka barni".
"so kike mu koma gida wani abu
ya sameki?
" Idan ba zamu koma gida ba, to bazaka bar É—akin nan ba, in ba haka ba ni zan tafi gidan nikaÉ—ai "
"Amma kin san zamana dake a ɗaki ɗaya ya saɓawa shari'ar musulunci?"
Shiru tayi bata ce komai ba, Yusuf yace "kiyi haƙuri, mutan gidan nan suna da kirki kuma duk mutane ne, babu wanda ze cutar dake, kiyi haƙuri zanje in samu me garin muyi magana"
Riƙo rigar Yusuf tayi ta fashe da kuka tace "Wallahi bazan dinga zama a ɗakin nan nikaɗai ba, sedai duk inda zaka in bika"
Shiru yayi yana Kallonta, kuka take sosai har cikin ranta, tabbas yasan halinta da ƙyanƙyami da rashin yadda, ba zata yadda ta zauna da kowa a ɗaki ɗaya ba in bashi ba, kuma gashi hakan ya haramta.
Jiki a sanyaye yace "shikenan is ok kidena kuka, idan har kina son mu cigaba da zama tare a ɗakin nan inyi jinyarki bisa shari'a mafita ɗaya ce, kuma mafitar nasan me tsaurin gaske ce a gurinki ba lallai ki yadda ba"
Widad ta É—ago idonta tace "Meye mafitar?"
Yusuf yace " Sedai ki amince muyi Aure zuwa lokacin da zaki warke, mu koma gida semu rabu"
Gaban Widad ne ya faÉ—i ta tsaya tana masa wani irin kallo
Duk yadda me Adda yake tunanin lamarin ya wuce tunaninsa, dan babu wata alama ko sheda da zata nuna maka inda su Yusuf sukabi, suka yi sintiri da neman duniya a dajin nan basu sami su Yusuf ba, me Adda yace "gaskiya ina mamakin guduwar mutanen nan, tabbas akwai munafiki a cikinmu, wanda ya kuɓutar dasu banda haka yaza'ayi mutanen da ko tashi basa iyawa ace sun gudu?"
"Oga nima dai nayi wannan tunanin, dan tabbas maganar ka haka take, da saka hannun wani a kuɓutar tasu"
Me Adda yace "Ni yanzu tunanina yadda zanwa wannan mutanen bayanin sun ɓata, dan wallahi babu lallai su ƙyalemu"
"To Oga ko muma sanfewa za muyi muyi ta kanmu"
Me Adda yace "ƙwarai kuwa, Amma zamu fara kiransu mu gaya musu su san meya dace suyi, sannan muma muyi ta kanmu da ba mutunci mutanen nan suka cika ba"
Suleiman shike zuwa ya rarrashi Maman Yusuf, dan ko Abinci bata iya ci, sedai wataran inzeje yayi mata Nasiha ya sai wani abun ya kai mata.
Yauma bayan Azahar da ya taso daga gurin aiki gidan su Yusuf yaje, yatarar da Umman Yusuf akan dadduma taci kuka ta ƙoshi, idanunta duk sunyi jawur.
Suka gaisa Suleiman yace "Umma har yanzu baki dena kukan ba? Ki sani wannan carbin da kike ja kina masa Addu'a yafi wannan kukan da kike yi, dan Allah ki kwantar da hankalinki, kar wani ciwon ya shige ki"
Umman Yusuf tace "To Suleiman dangana ta zama dole, yau da gawar Yusuf na gani seta fiyemin kwanciyar hankali akan ɓatansa, ban san a ina yake ba, yaci Abinci? Yayi wanka? Me yake ciki? Yana samun Abincin da yake so duk ban sani ba, Allah ne kawai ya barwa kansa sani, dole in shiga damuwa inyi kuka"
Suleiman yace "hakane Umma, amma ki kwantar da hankalinki, muna nan muna bincike akan mu gano inda Yusuf yake, very soon zakiji labari me daɗi, kuma kisawa zuciyarki addu'ar nan da kike tana isa ga Yusuf insha Allah muna sa ran jin labari me daɗi akan Yusuf"
Umman Yusuf tace "Nagode Suleiman, Allah ya saka da alkhairi tunda abun nan ya faru kai kaÉ—ai kake zuwa inda nake ka rarrashenin, Nagode Allah yayi Albarka"
Suleiman yace "Ameen Umma, kin san mahaifin yarinyar ma yana can a gadon Asibiti, sedai fatan Allah ya bayyanasu"
Umma ta amsa da Ameen.
Nurat ta kuma satar jiki, mahaifiyarta bata sani ba ta tafi Asibiti duba jikin Baban Widad, koda taje Anwar kawai ta gani a gurinsa, sedai abun mamaki har yana zaune yana cin Abinci da kansa.
Nurat tace "Alhamdilillah lafiya ta fara samuwa, ya ƙarfin jiki kuwa Daddy?"
Daula yayi murmushi yace "Alhamdilillah, yau gani a zaune ina cin Abinci ma"
Nurat tace "Alhamdilillah"
Ta kalli Anwar tace "Yaya Anwar ina kwana"
Anwar yace "lafiya ƙalau, ya mutan gidan?"
"duk suna lafiya Alhamdilillah, Amma ina su Anty Ramlah ne?"
Ɗan kame kame Anwar ya fara yace "kin san da yake tunda Daddy ya kwanta itama taƙi lafiya, tana can tana jinya su Amal ke kula da ita"
Nurat tace "Allah sarki, Allah ya sawwake naje in duba ta"
Saleh ne yayi sallama ya shigo, yana ganin Daula a zaune yace "Alhamdilillah Alhajin Allah, kaine a zaune haka kake cin Abinci?"