Sashe 70
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anwar ya É—aga waya ya kira 'yan sanda, ya kira ya sanar da Bulama abunda ake ciki.
Widad ta gaji da zaman ɗaki, ta fito tsakar gida ƙarƙashin bishiya ta zauna, yaron gurin hansai ne da baze wuce shekaru uku ba, yake ta kallon Widad yana leƙa gashin kanta, murmushi Widad tayi tace "Naga kana son gashin nan, zo in baka ka taɓa"
Tsayawa yaron yayi yana murmushi, a hankali ya ƙaraso inda Widad take, ta riƙe hannunsa ta ɗora akan gashinta, nan yaron ya shiga wasa da gashin nata yana dariya.
Hansai data fito taga abunda yake faruwa, tunda suka dawo suka tarar dasu Widad, ko sannu bata taɓa haɗasu ba, ko murmurewa bata taɓa ganin tayi ba, Hausawa sukace me ɗa wawa se taji daɗin yadda Widad take wasa da ɗan nata.
Hindu data fito tsakar gidanma, tana ganin haka ta ƙaraso tace "kai Sani sakar mata gashi mana, ya takura miki ko?"
Widad tace "A'a nibe takura min ba, naga yana son kamawa ne shiyasa nace yazo ya taɓa"
Hindu tace "Abunka daba'a saba ganiba shiyasa yazo ya saki gaba"
Widad tayi murmushi har haƙoranta suka fito tace "gashin ne ba'a saba gani ba, bayan duk kanku ba'a aske yake ba"
Hindu tace "to ai ganin gashi me yawan naki dai basu saba gani ba, kuma dan Allah ke 'yar ƙasar nan ce?"
Hansai dake ƙoƙarin haɗa wuta tace "wallahi nima abunda ke bani mamaki kenan, dan Allah' yar ƙasar nan ce ke?"
Widad tace "taɓ 'yar ƙasar nan ceni mana, banyi kama da Hausawa bane"
Hindu tace "gaskiya ko bahaushiya ce ke, to sedai ko ruwa biyu"
Widad tace "ruwa biyu kamar yaya?"
Hansai tace "kamar ace mamanki bahaushiya mahaifinki wani yaren, ko mahaifinki bahaushe mamanki wata yaren"
Widad ta É—anyi jim sannan ta murmusa tace "dukkansu Hausawa ne, mazauna Kano"
Hindu tace "kano, dan Allah a kano kike?"
Widad tace "kin taɓa zuwa ne?"
"Ni waze kaini kano? Muna dai jin labarin kano, ance garin yana da kyau sosai, kuma mutanen kano suna da kirki"
Widad tace "Insha Allah wataran zaki kano, ba laifi kam kano tana da kyau, nikam ya sunanki ne"
Hindu tace "sunana Hindu"
Widad tace "Masha Allah, Hindatu"
Gwaggo ce ta fito hannunta ɗauke da ƙwarya da rariya tace "Amarya yau hira ake haka? Badan da kaina naga kina surutu ba, da zance bake bace"
Widad tace "Wallahi gwaggo bani da surutu, amma ina magana sosai ai"
Hanne kuwa dake bakin rijiya tana wanke wanke ko kulasu ba tayi ba.
Itakuwa Hari fitowa tayi da gero, ta zuba a turmi ta fara daka tana habaice habaicenta, basu kulata ba suka cigaba da hira.
Gwaggo tace "Ai Amarya mutum rahama ne, ko yaya idan kina É—an fitowa ana hira zaki rage kaÉ—aici, amma ace ke mijinki kawai kika sani"
Widad tace "Mama kenan, to ai shikaÉ—ai É—in kawai na sani, kawo in tayaki tankaÉ—awa"
Gwaggo tace "A'a kar in takura miki"
Widad tace "ni baki takuramin ba"
Ta ɗaga kai ta kalli Hari tace "dan Allah malama kiyi ɗaya, ko dakan kokuma waƙe waƙen haba dan Allah, da wanne za muji ƙarar daka ko kuma na wannan hayaniyar da kike yi"
Hari tace "Allah ya haɗani da Baƙar Jaraba ni Hari jikar Hama, na kulaki ne ko tsabar jan bala'i ne? Wallahi ki fita a sabgata, tun kafin in miki wulaƙanci"
Widad ta sunkuyar da kai tana dariya, dama abunda take so kenan, ta zungurota taita masifa, dan ita yanzu ta maida Hari comedy.
Widad ta karɓi tankaɗe kamar abun Arziki, ta riƙe rariyar da hannu ɗaya, ta ɗaga hannun sama tana girgiza rariyar, garin kuwa se kama gabansa yake, dan haka iska ta dinga kwashe shi, gwaggo kuma takasa yi mata magana saboda kawaici.
Yusuf ne yayi sallama hannunsa ɗauke da ledar viva, hango Widad yayi tayi buɗu buɗu a cikin gari, gashi a ƙarƙashin bishiya take tankaɗen, iska duk ta kwashe garin.
Hanne na ganinsa ta wani fara mutsu mutsu da gyare2, tace "sannu da zuwa" Yusuf be kula da ita ba
Da sauri ya ƙarasa inda Widad take yace 'Subhanallah Widad waye ya saki wannan aikin "
Gwaggo tace "seda nace base tayi ba, tace in bata tayi"
Yusuf yace "wa yace ki bata, Mama bata iya bafa, kalli yadda tayi miki Asarar gari"
Murmushi gwaggo tayi, ta É—auke kai daga kallonsu.
Widad tace "Na iya, ba gashi inayi ba, kai komai nayi seka gwalemin"
Yusuf yace "Ni na isa kiyi abu in gwale, amma kalli yadda kika ɓata gurin"
"Ni dai ka ƙyaleni in cigaba da aikina"
Yace "Naji, amma kawo in nuna miki yadda akeyi"
"A'a ni naga yadda akeyi ai, shine nima nake gwadawa"
Gwaggo kam gaba ɗaya kunya suka bata, dan haka ta miƙe ta bar musu gurin gaba ɗaya.
Yusuf yayi ƙasa da murya yace "dan Allah kiyi haƙuri ki kawo, wallahi baki iya ba kawaici kawai tayi miki, amma wannan aika aika kike mata"
Sakar masa rariyar tayi, ya shiga gwada mata yadda ake yi, kawai ta kwashe da dariya, ya kalle ta yace "lafiya kuwa?"
"A'a gani nayi ka iya sosai"
Ba ƙaramin kyau tayi ba dariyar da tayi, karon farko da tayi fara'a haka sosai ya gani.
Kawai ya shagala da kallonta, ya É—anyi murmushi ya cigaba da nuna mata yadda akeyi.
Hanne kuwa ji tayi ta tsani Widad gaba ɗaya, ko ganinta bata son yi ganin Yadda Yusuf ke wani ƙure Widad da ido se taji kamar tayi kuka.
Megari ne yayi sallama ya shigo, yace "Malam Yusuf ka dawo kenan?"
Yusuf yace "eh Baba na dawo" Megari yana jin daÉ—in yadda Yusuf yake girmamashi
Yace "ya kasuwar kuwa?"
Yusuf yace "Alhamdilillah, naje harna dawo"
Megari yace "to masha Allah"
Widad kam ko kallon Megari ba tayi ba, balle tace masa wani abu, Megari ya ƙaraso inda take yace "wannan 'ya tawa akwai miskilanci, tunda ba zata kula baban nata ba, toga tsaraba na kawo mata, Allah ya ƙara ƙarfin jiki"
Ya ajiye mata dabino rabin kwano a gabanta, Yusuf yace "Mungode sosai Baba, Allah yasaka da alkhairi"
Megari yace "A' a bakomai Yusufa, Allah ne ya haÉ—a mu zama tare, kuma naji harga Allah kun kwantamin, Allah yayi muku Albarka"
Yusuf yace "Ameen"
Yusuf ya É—au ledae daya shigo da ita, da wadda Megari ya bawa Widad, ya shige gaba Widad na binsa a baya, gwaggo tace
"Amarya karɓi kayan hannun nasa mana"
Widad tace "Ai ze iya É—auka, ni yamin nauyi"
Gwaggo ta jinjinawa gaɓunta irinta Widad, akwai buƙatar a zaunar da ita ayi mata takara akan zama da miji.
Suna shiga É—aki Yusuf yace "yanzu uwaÉ—akina abaki abu amma ki kasa cewa kin gode, baze ji daÉ—i ba fa"
Maimakon tayi magana, sema sosa kai data hauyi tana wasa da gashin kanta ta wuce inda katifarta take, Yusuf ya bita da ido, wato se yanzu yake ganin tsabar yarintar Widad, wato a da ɗinma tsabar izzarta da jin kaine yake sa ka ganta kamar wata babba amma kwanan nan wautar da Widad keyi wasu lokutan, suke ƙara fito da yarintar ta, sedai har yanzu wannan izzar da jin kan basu barta ba.
Yusuf yace yakamata kidinga gaida Megari, kinga yana mana ƙoƙari shima kinji gimbiyata.
Aikuwa nan da nan ta haÉ—a rai , Yusuf yace "meye kuma na haÉ—e ran?"
"Ai kafini sanin abunda ka faÉ—a, kuma kasan bana so"
Hindu ce tayi sallama a ɗakin nasu Yusuf ya amsa, ta shigo da kwano ta durƙusa ta gaida Yusuf, Yusuf ya amsa mata, tace "Amarya gashi inji Gwaggo"
Widad tace "to Nagode"
Hindu ta juya ta fita, Widad ta buÉ—e kaanon tace "yau kuma meye wannan?"
Yusuf ya karɓa ya duba yace "kwaɗon rama ne"
Ta kalle shi tace "meke nan?"
Yusuf yace "kici kiji mana"
Tashi tayi taje ta wanke hannu tazo ta zauna, ta ɗiba takai bakinta, yatsine fuska tayi tana taunawa da ƙyar, kamar tayi kuka tace
"Wai su mutanen nan basa girka abunda akeci ne?"
Yusuf kamar ya tintsire da dariya yace "wannan me ake dashi in ba ciba"
"to naji tsami, ga gishiri da kamar sugar"
Yusuf yace "kyaji dashi, nidai bari inje inyi salla" ya miƙe ya fita.
Abu kamar wasa, sa 'yan sanda suka tashi suka kama Anwar da Doctor Sufyan, wai za' ayi bincike a kansu akan ɓatan Alhaji Nasir Daula, aka kama wasu daga ma'aikatan Asibitin sannan aka rufe Asibitin. Tun ana ɓoye ɓoye har abu ya fara bayyana cewar wai Alhaji Nasir Daula ya ɓata a Asibiti.
Hankalin Hajiya Halima ya tashi, jin an kama mata É—a an kai shi police station, gidan Bulama ta shirya ta tafi bagazan bagazan ta É—au mota ta fice.
Tana fita Isa yace "Matsiyaciyar mata, da yake É—anta aka kama kalli yadda ta fita afujajan, amma mijinta na kwance a Asibiti ko a jikinta, ni É—anne ma yake bani tausayi da nace Allah yasa baza'a sake shi ba"
Murtalah yace "ai Matsiyaciya É—aya kenan, kalli yadda ta saida fiye da rabin motocin gidan nan, kalli Yadda tabi ta rage mana albashi dan Azzaluma ce, Allah sarki Yusuf da uwaÉ—akinsa, ko a wane hali suke oho?"
Nura yace "Ai wallahi se yanzu nake ganin ranar yarinyar nan, duk wulaƙancinta haƙƙinmu baya ciwo koda megida baya nan, ubangiji Allah ya bayyana Alhaji Daula"
Isa yace "Ameen dai abubuwa se faruwa suke kamar almara wai anemi mutum a gadon Asibiti a rasa, Allah ya kyauta"
Suka haɗa baki sukace "Ameen"
Yusuf ya dawo daga salla, yaga kwanon rama a rufe, yace "kaddai baki ci ba"?
Dabinonta take ci tace "ni bazan iya cin wannan Abunba"
Yana duba kwanon yaga ta tattare ƙuli ƙulin, da tumatir da Albasar da gurjin dake kai ta cinye abunta, ta bar gayan ramar duk ta lashe ƙulin jiki.
Murmushi yayi bece komai ba, ya ci ramar nan a haka, se jikinta yayi sanyi taga bata kyauta ba.
"Gimbiyata, ga wake nan na siyo mana a kasuwa yau da yamma za'a kawo kayan tea harda bredi"
Da sauri ta kalle shi tace "dan Allah dagaske hadda bredi?"
"ya zan miki ƙarya, inje ki hukunta ni, dagaske nake"
"Yau zanci bredi"
Yusuf yace "hadda shayi makuwa, bari inje in watsa ruwa na gaji sosai"
Widad ta gaji da zaman ɗaki, ta fito tsakar gida ƙarƙashin bishiya ta zauna, yaron gurin hansai ne da baze wuce shekaru uku ba, yake ta kallon Widad yana leƙa gashin kanta, murmushi Widad tayi tace "Naga kana son gashin nan, zo in baka ka taɓa"
Tsayawa yaron yayi yana murmushi, a hankali ya ƙaraso inda Widad take, ta riƙe hannunsa ta ɗora akan gashinta, nan yaron ya shiga wasa da gashin nata yana dariya.
Hansai data fito taga abunda yake faruwa, tunda suka dawo suka tarar dasu Widad, ko sannu bata taɓa haɗasu ba, ko murmurewa bata taɓa ganin tayi ba, Hausawa sukace me ɗa wawa se taji daɗin yadda Widad take wasa da ɗan nata.
Hindu data fito tsakar gidanma, tana ganin haka ta ƙaraso tace "kai Sani sakar mata gashi mana, ya takura miki ko?"
Widad tace "A'a nibe takura min ba, naga yana son kamawa ne shiyasa nace yazo ya taɓa"
Hindu tace "Abunka daba'a saba ganiba shiyasa yazo ya saki gaba"
Widad tayi murmushi har haƙoranta suka fito tace "gashin ne ba'a saba gani ba, bayan duk kanku ba'a aske yake ba"
Hindu tace "to ai ganin gashi me yawan naki dai basu saba gani ba, kuma dan Allah ke 'yar ƙasar nan ce?"
Hansai dake ƙoƙarin haɗa wuta tace "wallahi nima abunda ke bani mamaki kenan, dan Allah' yar ƙasar nan ce ke?"
Widad tace "taɓ 'yar ƙasar nan ceni mana, banyi kama da Hausawa bane"
Hindu tace "gaskiya ko bahaushiya ce ke, to sedai ko ruwa biyu"
Widad tace "ruwa biyu kamar yaya?"
Hansai tace "kamar ace mamanki bahaushiya mahaifinki wani yaren, ko mahaifinki bahaushe mamanki wata yaren"
Widad ta É—anyi jim sannan ta murmusa tace "dukkansu Hausawa ne, mazauna Kano"
Hindu tace "kano, dan Allah a kano kike?"
Widad tace "kin taɓa zuwa ne?"
"Ni waze kaini kano? Muna dai jin labarin kano, ance garin yana da kyau sosai, kuma mutanen kano suna da kirki"
Widad tace "Insha Allah wataran zaki kano, ba laifi kam kano tana da kyau, nikam ya sunanki ne"
Hindu tace "sunana Hindu"
Widad tace "Masha Allah, Hindatu"
Gwaggo ce ta fito hannunta ɗauke da ƙwarya da rariya tace "Amarya yau hira ake haka? Badan da kaina naga kina surutu ba, da zance bake bace"
Widad tace "Wallahi gwaggo bani da surutu, amma ina magana sosai ai"
Hanne kuwa dake bakin rijiya tana wanke wanke ko kulasu ba tayi ba.
Itakuwa Hari fitowa tayi da gero, ta zuba a turmi ta fara daka tana habaice habaicenta, basu kulata ba suka cigaba da hira.
Gwaggo tace "Ai Amarya mutum rahama ne, ko yaya idan kina É—an fitowa ana hira zaki rage kaÉ—aici, amma ace ke mijinki kawai kika sani"
Widad tace "Mama kenan, to ai shikaÉ—ai É—in kawai na sani, kawo in tayaki tankaÉ—awa"
Gwaggo tace "A'a kar in takura miki"
Widad tace "ni baki takuramin ba"
Ta ɗaga kai ta kalli Hari tace "dan Allah malama kiyi ɗaya, ko dakan kokuma waƙe waƙen haba dan Allah, da wanne za muji ƙarar daka ko kuma na wannan hayaniyar da kike yi"
Hari tace "Allah ya haɗani da Baƙar Jaraba ni Hari jikar Hama, na kulaki ne ko tsabar jan bala'i ne? Wallahi ki fita a sabgata, tun kafin in miki wulaƙanci"
Widad ta sunkuyar da kai tana dariya, dama abunda take so kenan, ta zungurota taita masifa, dan ita yanzu ta maida Hari comedy.
Widad ta karɓi tankaɗe kamar abun Arziki, ta riƙe rariyar da hannu ɗaya, ta ɗaga hannun sama tana girgiza rariyar, garin kuwa se kama gabansa yake, dan haka iska ta dinga kwashe shi, gwaggo kuma takasa yi mata magana saboda kawaici.
Yusuf ne yayi sallama hannunsa ɗauke da ledar viva, hango Widad yayi tayi buɗu buɗu a cikin gari, gashi a ƙarƙashin bishiya take tankaɗen, iska duk ta kwashe garin.
Hanne na ganinsa ta wani fara mutsu mutsu da gyare2, tace "sannu da zuwa" Yusuf be kula da ita ba
Da sauri ya ƙarasa inda Widad take yace 'Subhanallah Widad waye ya saki wannan aikin "
Gwaggo tace "seda nace base tayi ba, tace in bata tayi"
Yusuf yace "wa yace ki bata, Mama bata iya bafa, kalli yadda tayi miki Asarar gari"
Murmushi gwaggo tayi, ta É—auke kai daga kallonsu.
Widad tace "Na iya, ba gashi inayi ba, kai komai nayi seka gwalemin"
Yusuf yace "Ni na isa kiyi abu in gwale, amma kalli yadda kika ɓata gurin"
"Ni dai ka ƙyaleni in cigaba da aikina"
Yace "Naji, amma kawo in nuna miki yadda akeyi"
"A'a ni naga yadda akeyi ai, shine nima nake gwadawa"
Gwaggo kam gaba ɗaya kunya suka bata, dan haka ta miƙe ta bar musu gurin gaba ɗaya.
Yusuf yayi ƙasa da murya yace "dan Allah kiyi haƙuri ki kawo, wallahi baki iya ba kawaici kawai tayi miki, amma wannan aika aika kike mata"
Sakar masa rariyar tayi, ya shiga gwada mata yadda ake yi, kawai ta kwashe da dariya, ya kalle ta yace "lafiya kuwa?"
"A'a gani nayi ka iya sosai"
Ba ƙaramin kyau tayi ba dariyar da tayi, karon farko da tayi fara'a haka sosai ya gani.
Kawai ya shagala da kallonta, ya É—anyi murmushi ya cigaba da nuna mata yadda akeyi.
Hanne kuwa ji tayi ta tsani Widad gaba ɗaya, ko ganinta bata son yi ganin Yadda Yusuf ke wani ƙure Widad da ido se taji kamar tayi kuka.
Megari ne yayi sallama ya shigo, yace "Malam Yusuf ka dawo kenan?"
Yusuf yace "eh Baba na dawo" Megari yana jin daÉ—in yadda Yusuf yake girmamashi
Yace "ya kasuwar kuwa?"
Yusuf yace "Alhamdilillah, naje harna dawo"
Megari yace "to masha Allah"
Widad kam ko kallon Megari ba tayi ba, balle tace masa wani abu, Megari ya ƙaraso inda take yace "wannan 'ya tawa akwai miskilanci, tunda ba zata kula baban nata ba, toga tsaraba na kawo mata, Allah ya ƙara ƙarfin jiki"
Ya ajiye mata dabino rabin kwano a gabanta, Yusuf yace "Mungode sosai Baba, Allah yasaka da alkhairi"
Megari yace "A' a bakomai Yusufa, Allah ne ya haÉ—a mu zama tare, kuma naji harga Allah kun kwantamin, Allah yayi muku Albarka"
Yusuf yace "Ameen"
Yusuf ya É—au ledae daya shigo da ita, da wadda Megari ya bawa Widad, ya shige gaba Widad na binsa a baya, gwaggo tace
"Amarya karɓi kayan hannun nasa mana"
Widad tace "Ai ze iya É—auka, ni yamin nauyi"
Gwaggo ta jinjinawa gaɓunta irinta Widad, akwai buƙatar a zaunar da ita ayi mata takara akan zama da miji.
Suna shiga É—aki Yusuf yace "yanzu uwaÉ—akina abaki abu amma ki kasa cewa kin gode, baze ji daÉ—i ba fa"
Maimakon tayi magana, sema sosa kai data hauyi tana wasa da gashin kanta ta wuce inda katifarta take, Yusuf ya bita da ido, wato se yanzu yake ganin tsabar yarintar Widad, wato a da ɗinma tsabar izzarta da jin kaine yake sa ka ganta kamar wata babba amma kwanan nan wautar da Widad keyi wasu lokutan, suke ƙara fito da yarintar ta, sedai har yanzu wannan izzar da jin kan basu barta ba.
Yusuf yace yakamata kidinga gaida Megari, kinga yana mana ƙoƙari shima kinji gimbiyata.
Aikuwa nan da nan ta haÉ—a rai , Yusuf yace "meye kuma na haÉ—e ran?"
"Ai kafini sanin abunda ka faÉ—a, kuma kasan bana so"
Hindu ce tayi sallama a ɗakin nasu Yusuf ya amsa, ta shigo da kwano ta durƙusa ta gaida Yusuf, Yusuf ya amsa mata, tace "Amarya gashi inji Gwaggo"
Widad tace "to Nagode"
Hindu ta juya ta fita, Widad ta buÉ—e kaanon tace "yau kuma meye wannan?"
Yusuf ya karɓa ya duba yace "kwaɗon rama ne"
Ta kalle shi tace "meke nan?"
Yusuf yace "kici kiji mana"
Tashi tayi taje ta wanke hannu tazo ta zauna, ta ɗiba takai bakinta, yatsine fuska tayi tana taunawa da ƙyar, kamar tayi kuka tace
"Wai su mutanen nan basa girka abunda akeci ne?"
Yusuf kamar ya tintsire da dariya yace "wannan me ake dashi in ba ciba"
"to naji tsami, ga gishiri da kamar sugar"
Yusuf yace "kyaji dashi, nidai bari inje inyi salla" ya miƙe ya fita.
Abu kamar wasa, sa 'yan sanda suka tashi suka kama Anwar da Doctor Sufyan, wai za' ayi bincike a kansu akan ɓatan Alhaji Nasir Daula, aka kama wasu daga ma'aikatan Asibitin sannan aka rufe Asibitin. Tun ana ɓoye ɓoye har abu ya fara bayyana cewar wai Alhaji Nasir Daula ya ɓata a Asibiti.
Hankalin Hajiya Halima ya tashi, jin an kama mata É—a an kai shi police station, gidan Bulama ta shirya ta tafi bagazan bagazan ta É—au mota ta fice.
Tana fita Isa yace "Matsiyaciyar mata, da yake É—anta aka kama kalli yadda ta fita afujajan, amma mijinta na kwance a Asibiti ko a jikinta, ni É—anne ma yake bani tausayi da nace Allah yasa baza'a sake shi ba"
Murtalah yace "ai Matsiyaciya É—aya kenan, kalli yadda ta saida fiye da rabin motocin gidan nan, kalli Yadda tabi ta rage mana albashi dan Azzaluma ce, Allah sarki Yusuf da uwaÉ—akinsa, ko a wane hali suke oho?"
Nura yace "Ai wallahi se yanzu nake ganin ranar yarinyar nan, duk wulaƙancinta haƙƙinmu baya ciwo koda megida baya nan, ubangiji Allah ya bayyana Alhaji Daula"
Isa yace "Ameen dai abubuwa se faruwa suke kamar almara wai anemi mutum a gadon Asibiti a rasa, Allah ya kyauta"
Suka haɗa baki sukace "Ameen"
Yusuf ya dawo daga salla, yaga kwanon rama a rufe, yace "kaddai baki ci ba"?
Dabinonta take ci tace "ni bazan iya cin wannan Abunba"
Yana duba kwanon yaga ta tattare ƙuli ƙulin, da tumatir da Albasar da gurjin dake kai ta cinye abunta, ta bar gayan ramar duk ta lashe ƙulin jiki.
Murmushi yayi bece komai ba, ya ci ramar nan a haka, se jikinta yayi sanyi taga bata kyauta ba.
"Gimbiyata, ga wake nan na siyo mana a kasuwa yau da yamma za'a kawo kayan tea harda bredi"
Da sauri ta kalle shi tace "dan Allah dagaske hadda bredi?"
"ya zan miki ƙarya, inje ki hukunta ni, dagaske nake"
"Yau zanci bredi"
Yusuf yace "hadda shayi makuwa, bari inje in watsa ruwa na gaji sosai"