← Book details Akidata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 82

Sashe 33

Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murtalah ya kwashe da dariya yace  "bayan kun dawo kuma tai maka tatas a gabanmu ba, saboda ƙazanta kai Nura jiya kaga tijara a tsakar rana, ai idan nine kai ko maganar ba zan ɗakko yau ba" yai maganar yana dariya

Nura ya haÉ—e rai yace
"Bana son rashin mutunci da Iskanci"

Ganin suna nema suyi faÉ—a yasa Yusuf yin gaba abunsa ya barsu a gurin, tafiya kawai yake yi amma jikin sa babu daÉ—i.

Yana shiga falon ya tarar da Ramadan É—an gidan Alhaji Bulama da Amal suna hira.

Yusuf yace  "barkanku da Safiya"

Bata amsa masa ba se Ramadan ne yace  "Yawwa barka dai, bodyguard ɗin gimbiya" Yusuf ya ɗanyi murmushi ya nufi hanyar Widad.

Bayansa Amal tabi da kallo, taji wasu hawaye na ƙoƙarin zubo mata, ta tsani kusancin Widad da Yusuf gani take komai ze iya faruwa, wani sashin na zuciyar ta ma yana gaya mata akwai wata alƙar a tsakaninsu saboda kusancinsu yayi yawa.

Ramadan ya kalleta yace "lafiya kuwa my?"

Girgiza masa kai kawai tayi tace  "lafiya ƙalau"

Yusuf ya shiga ya tsaya a bakin ƙofar bedroom ɗin ta sannan yayi sallama kamar yadda ya saba.

Yayi Sallama kusan uku amma bata amsa ba, haka ya cigaba da tsayuwa a gurin, seda aka kwashi wani lokaci sannan ta fito, kallon sa tayi daga sama zuwa ƙasa sannan tace 
"Sannu ishashshe kaga damar zuwa kenan?"
Shiru Yayi ya sunkuyar da kai, É—akin ta shige yabi bayanta da sallama

"Meya hanaka zuwa jiya? Kuma kaƙi ɗaga waya?"

"Bani da lafiya ne shiyasa"

"ƙarya kake" ta faɗi kai tsaye ba tare da duba ratar shekarun da Yusuf ɗin ya bata ba, shiru ya sake yi bece komai ba, ta tako tazo daf dashi tace 
"for the second time meya hanaka zuwa jiya?"

"bani da lafiya ne" ya sake bata amsa

"wai me yasa baka kunyar yin ƙarya ne, meyasa? Ban gaya maka bana son ƙarya ba?" tai maganar tana ƙoƙarin sa idon ta a cikin nasa

Babu zato ya janyota gaba ɗaya tana facing ɗinsa, ya kafe ta da idon sa, nata cikin nashi ya ƙura mata ido

Ayi sharing please 🙏🙏🙏

Ayshercool
07063065680
                    
                    _*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

      

                   

     PART1
                              Page 13

ELEGANT ONLINE WRITER'S

Ba ƙaramin firgita tayi ba da abunda Yusuf ɗin yayi, sedai riƙon da yayi mata tana iya jin huci me zafin da jikin sa ke fitarwa, masifa take son yi amma gaba ɗaya Yusuf yayi mata wani irin kwarjini ta kasa cewa komai se binsa da tayi da manyan idanunta.

Cike da jarumta Yusuf yace "Meyasa koda yaushe idan nayi abu seki ƙarya tani? A koda yaushe ina ƙoƙarin gaya miki iya gaskiya ta amma seki ce ƙarya nake, kin san yadda mutum keji kuwa idan aka ƙarya tashi, it's really hurts, duk abunda nake yi ba inayi ne dan in samu kusanci dake ba, nasan AƘIDARKI nasan abunda bakya so, ina ƙoƙarin kiyaye dokokin da kika kafamin ne, dokokin dana sawa hannu amma koda yaushe burinki kici zarafina"

"Malam cikani ko"  ta faɗa tana masa wani irin kallo

Cikata yayi ya koma gefe ya tsaya.

Seda tayi ajiyar zuciya sannan tace

"hmm tunda nake babu wanda ya taɓa Yimin abunda kayi min a yanzu, ina ɗaga maka ƙafa ne saboda wasu dalilai biyu zuwa uku, dalilai biyu bakomai ne a gurina ba, dan ba zasu hanani yanke hukuncin dana ga dama akan ka ba, dalili ɗaya ne me ƙarfin da yazo da ƙaddarar da ni ban isa in canza shi ba koda hakan bemin ba, ba yadda zanyi da kai dukda har yanzu ina doubting akan wannan dalilin, Anyway zamu fita yanzu zamu je gidan gona"

"A wace motar?" ya tambayeta a taƙaice

"kowacce ta bashi amsa"

Har ya juya ze fita yaji tace 
"meya sameka a fuskarka?"

Ya juyo ya kalleta

"kar kayi min ƙarya" ta faɗa kafin ya bata amsa

"Duka ne" ya bata amsa

"Kamar ya ya duka? Suwaye suka dakeka?"

"Nima ban sansu ba"

Ɗan tsayawa tayi tana nazarinsa, yayin da ya ɗauke kai yaƙi kallonta

"Shikenan, muje"

Suka fito falo, yana gaba tana bayan sa, Amal ta bisu da wata uwar harara.

Ramadan yace 

"Allah ya temaki 'yar masu gida, Gimbiyar gida a biki a zauna lafiya, a ɓata miki mutum yai kwanan baƙinciki,' yar gaban goshi sha lelen masu arziki, tun ɗazu nake zaman jiranki anan, Megida ne ya aiko ni, yace yana son ganinki"

Ta yamutsa fuska tace  "Ina da abunyi, da  haka ba zani ba"

Ramadan yace "haka zanje in gaya masa"

"Eh haka za kaje ka gaya masa, bazan zo ba, bazan ƙara zuwa inda yake ba"

"shikenan, kunfi kusa keda shi"

Ta juya suka fice ita da Yusuf.

Amal tace  "Ramadan, dan Allah yanzu baka jin haushin irin abunda takewa mahaifinku?"

Ramadan yace  "to me zance Amal? Ni meye nawa a ciki? Da mahaifina da mahaifinta tashi nayi na gansu tare, kuma haka muka tashi muka ga an sangartata se abunda take so sukeyi, sun ɗauki son duniya sun ɗora mata, ba'a kwaɓarta komai tayi dai dai ne, meyasa zanji haushi, tunda ba yau ta fara ba, kuma idan tayi baya jin haushi, a gabana a gaban sa idan bata ga dama ba  Bulama take cemasa kanta tsaye, an riga an barta ta tashi akan wannan AƘIDAR"

"gaskiya ni abun yana damuna, mu kanmu a cikin gidan nan bamu tsira daga wulaƙancin ta ba, bamu ba har mahaifiyar mu fa"

"kin san wani abu? Ni yanzu babbar damuwa ta itace, Daddy yace  Fahad zasu aurawa ita, Fahad kuma mutum me faɗa baya son raini ni ban san ta yaya za'ayi wannan zaman auren ba"

Amal tace  "ai duk wanda ya kwashi wannan ya kwashi masifa, gata mahaukaciya ga ba tarbiyya, gaskiya ina tausayin Fahad"

***********************************

Yusuf yayi parking ɗin motar a gidan gona, Widad na fitowa kamar kullum haka ma'aikatan suka yo caa suna gaishe ta, ɗaga musu hannu tayi ta kalli Wani daga cikin ma'aikatan, wanda ya tsare Yusuf da tambayoyi wancan karon tace 
"Ya aiki ya kuma dabbobi na?"

"lafiya ƙalau ranki ya daɗe, ko za'a ɗakko dokin ne?"

"A'a sedai ina so kayi min rakiya in zaga su"

"to shikenan ranki ya daÉ—e" haka suka shiga suna zagawa, sosai Widad take jin nishaÉ—i idan tana kallon dabbobi, gaba É—aya mantawa take da damuwar da take ciki, suna cikin tafiya tace

"Sale naji wata magana, ban sani ba ko kai ka jita, takanas nace bari inzo domin mu tattauna ta"

Saleh yace  "Allah yasa ba wani abun akace nayi ba ranki ya daɗe?"

"idan ka yadda da kanka ba kayi lefi ba meye na tsarguwa? Labari ya isheni cewar É—an uwanka bala bashi ds lafiya, naje har prison dan in duba shi, amma akace min an fita da shi zuwa babban Asibiti dan be san wake kansa ba, ban kai ga zuwa duba shi ba har sena je naga lawyer na tukuna "

A gigice Sale ya kalle ta yace " ya za'ayi ace yana rashin lafiya, harta kai ga baya gane mutane? Shekaranjiya fa naje duba shi, na sameshii lafiya ƙalau, taya haka zata faru? "

"Nima abunda na gaza ganewa kenan, ace beyi rashin lafiya ba se daya rage 'yan kwanaki a cigaba da shari'a, Babban Albishir É—in dana zo maka da shi shine, muddin na tabbatar da sa hannun ka, zaka maye gurbinsa ne"

Saleh ya kalleta da sauri, bata bari yace komai ba, ta juya ta tafi. Turus Saleh yayi yana nazarin maganganun Widad.
Tunda Yusuf ya fara aiki da Widad, a kullum se yaga abun mamakin daze kulle masa kai.

Ya kunna motar suna shirin tafiya wayar ta ta ɗau ruri, tana kallon screen ɗin wayar ta ɗan ɓata rai ta tura baki, ɗaga wayar tayi tasa a hansfree  "Hello Daddy"

"lovely fushi kike dani ko?"

"A'a"

"Fushi kike mana, Daddynki yace ya aiko a kira masa ke kince ace bazakiyi zo ba, Baby Why meyasa kike haka?" shiru tayi taƙi cewa komai.

"Yanzu haka munyi waya, ina so kije kiji meze ce miki"

"Daddy nifa yanzu wani gurin zani, Na gaya maka ina cikin damuwa kunƙi saurara ta, sema kawomin wasu abubuwa da bana buƙata yake, na gaya maka akwai matsala amma kunƙi saurara ta"

"Ba shawara nake baki ba, Umarni ne kije gurin Bulama yana son ganin ki"

Tura baki tayi ta ajiye wayar tana haɗe rai, Yusuf be nemi shawarar ta ba ya kaita gidan Bulama, Ranta a ɓace ta buɗe motar ta fita tana tura baki, har tayi gaba ta tsaya ta juya taga Yusuf yana rufe mota
"Malam ni ka hanzarta ba zaman jiranka zan tsaya yiba"

Yusuf ya biyo bayanta, suna shiga katafaren falon suka tarar da Iman, ƙanwar Ramadan, Iman tai murmushi tace  "Ohhh beb, ashe zaki zo yanzu Ramadan ya dawo"

Hannu kawai ta É—agawa Iman ta nufi matattakalr bene.
Iman tace "Widad, Nurat ta kirani tace min tun ranar da kika bar gurin birthday ɗinta baki ƙara ɗaga wayarta ba, i hope ba saɓani kuka samu ba, dukda nasan halinki dai"

Shiru Widad tayi ta tsaya, saboda yadda abubuwa suka yi mata yawa, sam bata cigaba da bibiyar meyasa meta a gurin birthday ɗin Nurat ba, dan tafi tunanin ko ciwonta ne ya tashi a gurin, shiyasa ta kasa tuna komai, juyawa tayi tana kallon inda Yusuf yake, ya ɗauke kai yaƙi kallon ta.

Still ba tace komai ba ta cigaba da tafiya Yusuf na binta.

A babban falon dake saman benen wanda ya kasance na Bulama anan suka tarar da Bulama shida matarsa.
Chapter 33 · 0% Book details