Sashe 56
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya Halima tace "ko bangon duniya za'a kai shi idan Allah yayi niyyar karɓar rayuwarsa ba yadda muka iya, anan ɗinma naga likitocin suna iya ƙoƙarin su, meye kuma se an kwashi jiki an tafi ƙasar waje dan ɓarnar kuɗi"
"Mummy ɓarnar kuɗi kuma? Koma ɓarnar kuɗin ne naga nasane ai, meye amfaninsu in baza'a nema masa lafiya ba"
"kaga Anwar ka kiyaye ni, kafini sanin abunda ya dace ne? Fita ka ban guri kafin in ɓata maka rai, sakarai kawai"
Fitowa yayi gwiwa a saɓule yana tunanin wannan halina Mummynsa.
Gidan Bulama ya tafi, yaje ya tarar yana shirin fita, suka gaisa da Anwar, Anwar yace "Daddy gurinka nazo"
Bulama yace "gashi ina shirin fita ne, Amma meya faru?"
Anwar yace "Daddy dama cewa nayi meze hana a fita da Daddynmu waje a duba shi yadda ya kamata a can, naga kullum ciwon nasa gaba yake ba sauƙi"
Alhaji Bulama yace "Anwar kazo da magana me kyau, amma ka sani ko an fitar da Daula waje in har baze cire damuwa dake ransa ba, babu yadda za'ayi magunguna suyi masa aiki, haka likitoci suke ta faɗa"
"Amma da dai an jarraba, amma jikinsa yana bani tsoro"
Alhaji Bulama yayi shiru sannan yace "shikenan Anwar, zamu yi maganar da mahaifiyarka, zanga abunda ya dace ayi"
Anwar yayi masa godiya sannan ya tafi.
Alhaji Haruna ne zaune akan kujera, fuskar nan tasa babu alamar imani ya kalli wani matashi dake zaune yace
"doctor Sufyan, mun yaba da ƙoƙarin da kuke yi a Asibitinka akan Shahararren Attajirin da'ake ji dashi a faɗin ƙasar nan wato Alhaji Nasir Daula"
Doctor Sufyan yayi murmushi yace "Nagode ranka ya daɗe"
Alhaji Musa yace "Kasan meyasa muka kiraka?"
Sufyan ya girgiza kai alamar aa'
Alhaji Haruna ya gyara zama yace "Abunda muke so da kai shine, bama son Daula ya tashi"
Zare ido Sufyan yayi yace "kamar yaya?"
Alhaji Musa yace "Nutsu ka kwantar da hankalinka, ba muna nufin ka kasheshi ba, A'a bama so ya tashi ya warke ta hanyar dena bashi magungunan da ya dace, kayi duk abunda zakayi masa wanda ze ƙara kwantar dashi, idan kayi haka akwai lada me tsoka da zamu baka"
Saleh dake gurin gaba ɗaya ya rikice yace "Amma Yallaɓai ba muyi haka daku ba, idan kuma ya rasa ransa fa?"
Alhaji Haruna yace "Saleh ka rufewa mutane baki, karka ɓatamin rai"
Ya maida hankalinsa kan doctor Sufyan yace "Yaya zakayi ko bazaka yi ba?"
Doctor Sufyan yace "Nifa na ɗau Alƙawarin bazan cutar da lafiyar kowa ba kafin in fara aiki, kuma Alhaji Nasir ya yadda dani, na daɗe ina duba shi lokaci ɗaya kuma se in....
" Kai dakata " Alhaji Musa ya dakawa Sufyan tsawa yace " karka kawo mana maganar banza malam, idan baka yi ba zamu nemi wani, kwata kwata aikin wata uku muke so kayi mana, za mu baka Naira miliyan goma, idan yayi maka kaɗan zamu ƙara maka"
Zare ido Sufyan yayi yace "miliyan Goma"
"ƙwarai kuwa, miliyan goma idan kuma kaƙi zamu saka wani amma ka tabattar da kaima ba zamu ƙyaleka ba"
Cikin hanzari Sufyan yace "zanyi ma, na amince zanyi insha Allah karka damu Alhaji"
Shiru Saleh yayi yana tunani, wato akan kuɗi mutanen yanzu duk alkhairinka sesu manta, idan baze manta ba dangin Sufyan ɗaiɗaiku ne Daula be kai aikin Hajji ba, Amma ya amince ze karɓi kuɗi ya cutar da Alhaji Nasir "
Da Sufyan ze tafi dubu É—ari biyar suka bashi wai ya zuba mai a mota.
Saleh yayi shiru abun duniya duk ya dameshi.
Su Alhaji Musa kuwa cigaba da ƙulle ƙullen sharrinsu suka yi.
Wayar Alhaji Haruna ce ta fara ringing, suka tsagaita da dariyar da suke Ya É—aga wayar yace
"Yaya me Adda, ya ake ciki ta faÉ—a maka kuwa?"
"Ina fa ta faɗa se wahalar damu take, ga taurin kai da tsiwar tsiya, sannan ta bada saƙo a baku"
Alhaji Musa a gigice yace "Kamar ya ta bada saƙo abamu ta sanmu ne?"
Me adda yace "ina nasan mata, cewa tayi mu cewa wanda suka sa a sace ta, ta tattaar duk wata hujja akan su, ko bayan an kashe ta asirinku ze tonu"
Wani gumine ya shiga tsatsafowa Alhaji Haruna yace "ƙarya take bata sanmu ba, a gidan uban wa ta sanmu balle ta tattara wata hujja a kanmu, yanzu kana ina ne?"
"ina cikin gari mana, naje Asibiti ne wani yarfi yarinyar nan ta min na kasa ko miƙewa tsaye, na ɗauka ma na tashi daga aiki"
Alhaji Musa yace "wani sakarci ne zesa ku baro su acan, maza ka koma ku gana mata Azaba iya Azaba seta faɗi inda takaddun suke, idan ta faɗi inda suke ku kashe su kawai"
Saleh yace "What akan me za'a kashe ta?"
Alhaji Musa be saurari Saleh ba ya cigaba da wayar sa.
Me Adda yace "gaskiya Oga kisan Yarinya kamar wannan ba kamar kashe sauran mutane bane, tsaf wannan cinnakun zasuyi ram damu"
Alhji Haruna yace "ba wanda ze kama ku, zancen nan da muke maka gaba ɗaya mun siye jami'an tsaro ba wani bincike da'ake akan ɓatan nata, dan haka ka gaggauta zuwa jibi idan bata faɗa ba ka tirsasa ta, ta gaya maka wasu hujjoji take dasu sannan ka kashe mana su"
Me Adda yace "angama Oga"
Alhaji Haruna ya sharce gumi yace "bala'i, Musa anya ba dagaske yarinyar nan ta gano mu ba, karfa muje dagaske take"
"Rabu da ita ƙarya take, da dagaske ta sanmu da tuni ta ɗau mataki akanmu, amma kasan bamu gayawa Munir da Bukar hukuncin da muka yanke ba?"
Alhaji Haruna yace "Suma idan mun gaya musu hukuncin da za susa ayi mata kenan a kashe ta kawai, karta ja mana masifa"
Alhaji Musa ya kalli Saleh yace "wai kai meye naka na saka baki dan munce a kashe ta, kabi a sannu fa wallahi kar kasa musa a haɗa da kai, kabi umarnin mu kawai"
Saleh yayi murmushi yace "Tausayin Daula ne ya kamani wallahi, karka damu bazan baku kunya ba insha Allah dani za'a kammala komai nima in samu rabona"
"daka temaki kanka" cewar Alhaji Haruna, yayin da cikkunansu suka É—uri ruwa.
Yusuf yana nan zaune rungume da Widad, har duhu yayi gari ya waye, sam be bacci ba gani yake da yayi bacci Widad zata mutu, dan bugun zuciyar ta da yake ji shike tabattar masa tana da rai, dan wani lokacin har motsawa take.
A hankali Yusuf ya kwantar da ita, yayi taimama yayi sallar Asuba, shima gaba ɗaya jikinsa a sake yake babu ƙwari saboda azabar wahala, ga yunwa ga duka ga cizon sauro ga azabar sanyi dake gurin, amma gaba ɗaya yafi tausayawa Widad, lokaci lokaci yakan kwance hannun nata, ya goge jinin ya sake ɗaure mata, ga wani irin zazzafan zazzabi da ko sauka bayayi a jikinta.
A hankali Widad ta buÉ—e ido, sedai dishi dishi take gani bata gane komai, tana yi tana lumshe ido haka take kallon Yusuf.
Yusuf ya girgiza ta yace "Alhamdilillah, you are alive"
Bata iya amsa masa ba, sedai idonta ya sake rufewa
Yana rungume da ita, yayi shiru yana ta ambaton Allah, babu zato ba tsammani yaji ana ta sukuwa a saman roofing ɗin ɗakin, Yusuf ya ɗaga kai yana son gane meke faruwa haka? Cigaba da sukuwa akayi a gurin anata ƙoƙarin ɓare kwanon, can kuma se'aka dena, yaji anata ƙoƙarin buɗe ƙofar da suke ciki, waze gani Saleh ne ya shigo cikin ɗakin.
A gigice Yusuf yace "kaine? Da kai aka haɗa baki kenan aka mana haka?"
Saleh yace "baka da lokacin wannan tambayoyin, zuwa nayi na tseratar da ku, ka adana tambayoyinka, idan kun tsira seka yi su"
Hankalinsa ya kai kan hannun Widad dake sume yama zubar da jini, da sauri ya ƙaraso yace "meya sameta haka? Harbinta sukayi?"
Yusuf bece masa komai ba, sedai kallon tuhuma da yake ta binsa dashi.
Saleh yace "zaka iya tafiya kuwa?"
Yusuf ya jinjina masa kai alamar eh, "to taso maza"
Yusuf ya yunƙura ya miƙe, amma ƙafafunsa se rawa suke saboda dukan daya sha, ga uwa uba yunwar da yake ji.
Amma cikin jarumta, da sadaukarwa ya miƙe ya goya Widad a bayansa.
Suka fito daga gidan, Saleh ya maida gidan ya rufe, sannan ya ɓare saman roofing yayi hanya, sannan yayi musu jagora hannunsa ɗauke da compass dake nuna masa direction suka nausa cikin daji.
Yusuf ji yake kamar ze kifa, amma haka ya cigaba da tafiya, Saleh ya kalle shi yace "ko zaka sauketa in ta yaka?"
Yusuf ya girgiza kai yace "A'a karka damu"
Tafiya sukayi bata wasa ba, ƙafar Yusuf ko takalmi babu, ya dinga taka abubuwa danma ta cikin ciyayi suke kutsawa, haka suka dinga tafiyar cikin sauri, suna bi takan ciyayi dan kaucewa barin sawunsu yadda za'a gane hanyar da suka bi, daji ne har daji me sarƙaƙiyar tsiya, da manyan bishiyu.
Sunyi tafiya me nisan gaske sannan suka fito titi, sam Yusuf be san a ina suke bama, Saleh ya nunawa Yusuf mota yace "ya shiga"
Yusuf yayi turus ya kalli Saleh, a wahalce yace "wannan taimakon ma da kayi mana mungode, amma bazan hauba, Insha Allah zamu bar gurin nan".
"Yusuf, wallahi suka kamaku kashe ku zasuyi, da inada niyyar cutar daku da bazan ceceku ba"
Da ƙyar Yusuf ya yadda, ya hau motar, da alama Saleh ya gama shirya komai.
Shima Saleh haka yayi doguwar tafiya dasu a motar, tafiya kamar za'a bar duniya dazuka kawai suke ratsawa, tituna bakowa se su kaÉ—ai, Shiru ne ya wanzu tsakaninsu har suka fara fita gari.
Wani É—an madaidaicin Asibiti suka tarar a hanya, Saleh yayi parking Yasa Yusuf ya É—akko Widad suka shiga Asibitin.
Kuɗi Saleh ya ajiyewa likitan, dan haka ba wani dogon bincike suka karɓi Widad, Amma Yusuf yaƙi zuwa ko'ina, a gabansa aka cirewa Widad bullet, akace se an tafi neman jini za'a ƙara mata.
Yusuf yace a ɗibi nashi, Saleh yace "baze yuwu a ɗebi naka ba, kaima a galabaice kake akwai buƙatar a duba ka"
Yusuf ya dage sedai a gwada jininsa in zeyi a É—iba a sa mata.
"Mummy ɓarnar kuɗi kuma? Koma ɓarnar kuɗin ne naga nasane ai, meye amfaninsu in baza'a nema masa lafiya ba"
"kaga Anwar ka kiyaye ni, kafini sanin abunda ya dace ne? Fita ka ban guri kafin in ɓata maka rai, sakarai kawai"
Fitowa yayi gwiwa a saɓule yana tunanin wannan halina Mummynsa.
Gidan Bulama ya tafi, yaje ya tarar yana shirin fita, suka gaisa da Anwar, Anwar yace "Daddy gurinka nazo"
Bulama yace "gashi ina shirin fita ne, Amma meya faru?"
Anwar yace "Daddy dama cewa nayi meze hana a fita da Daddynmu waje a duba shi yadda ya kamata a can, naga kullum ciwon nasa gaba yake ba sauƙi"
Alhaji Bulama yace "Anwar kazo da magana me kyau, amma ka sani ko an fitar da Daula waje in har baze cire damuwa dake ransa ba, babu yadda za'ayi magunguna suyi masa aiki, haka likitoci suke ta faɗa"
"Amma da dai an jarraba, amma jikinsa yana bani tsoro"
Alhaji Bulama yayi shiru sannan yace "shikenan Anwar, zamu yi maganar da mahaifiyarka, zanga abunda ya dace ayi"
Anwar yayi masa godiya sannan ya tafi.
Alhaji Haruna ne zaune akan kujera, fuskar nan tasa babu alamar imani ya kalli wani matashi dake zaune yace
"doctor Sufyan, mun yaba da ƙoƙarin da kuke yi a Asibitinka akan Shahararren Attajirin da'ake ji dashi a faɗin ƙasar nan wato Alhaji Nasir Daula"
Doctor Sufyan yayi murmushi yace "Nagode ranka ya daɗe"
Alhaji Musa yace "Kasan meyasa muka kiraka?"
Sufyan ya girgiza kai alamar aa'
Alhaji Haruna ya gyara zama yace "Abunda muke so da kai shine, bama son Daula ya tashi"
Zare ido Sufyan yayi yace "kamar yaya?"
Alhaji Musa yace "Nutsu ka kwantar da hankalinka, ba muna nufin ka kasheshi ba, A'a bama so ya tashi ya warke ta hanyar dena bashi magungunan da ya dace, kayi duk abunda zakayi masa wanda ze ƙara kwantar dashi, idan kayi haka akwai lada me tsoka da zamu baka"
Saleh dake gurin gaba ɗaya ya rikice yace "Amma Yallaɓai ba muyi haka daku ba, idan kuma ya rasa ransa fa?"
Alhaji Haruna yace "Saleh ka rufewa mutane baki, karka ɓatamin rai"
Ya maida hankalinsa kan doctor Sufyan yace "Yaya zakayi ko bazaka yi ba?"
Doctor Sufyan yace "Nifa na ɗau Alƙawarin bazan cutar da lafiyar kowa ba kafin in fara aiki, kuma Alhaji Nasir ya yadda dani, na daɗe ina duba shi lokaci ɗaya kuma se in....
" Kai dakata " Alhaji Musa ya dakawa Sufyan tsawa yace " karka kawo mana maganar banza malam, idan baka yi ba zamu nemi wani, kwata kwata aikin wata uku muke so kayi mana, za mu baka Naira miliyan goma, idan yayi maka kaɗan zamu ƙara maka"
Zare ido Sufyan yayi yace "miliyan Goma"
"ƙwarai kuwa, miliyan goma idan kuma kaƙi zamu saka wani amma ka tabattar da kaima ba zamu ƙyaleka ba"
Cikin hanzari Sufyan yace "zanyi ma, na amince zanyi insha Allah karka damu Alhaji"
Shiru Saleh yayi yana tunani, wato akan kuɗi mutanen yanzu duk alkhairinka sesu manta, idan baze manta ba dangin Sufyan ɗaiɗaiku ne Daula be kai aikin Hajji ba, Amma ya amince ze karɓi kuɗi ya cutar da Alhaji Nasir "
Da Sufyan ze tafi dubu É—ari biyar suka bashi wai ya zuba mai a mota.
Saleh yayi shiru abun duniya duk ya dameshi.
Su Alhaji Musa kuwa cigaba da ƙulle ƙullen sharrinsu suka yi.
Wayar Alhaji Haruna ce ta fara ringing, suka tsagaita da dariyar da suke Ya É—aga wayar yace
"Yaya me Adda, ya ake ciki ta faÉ—a maka kuwa?"
"Ina fa ta faɗa se wahalar damu take, ga taurin kai da tsiwar tsiya, sannan ta bada saƙo a baku"
Alhaji Musa a gigice yace "Kamar ya ta bada saƙo abamu ta sanmu ne?"
Me adda yace "ina nasan mata, cewa tayi mu cewa wanda suka sa a sace ta, ta tattaar duk wata hujja akan su, ko bayan an kashe ta asirinku ze tonu"
Wani gumine ya shiga tsatsafowa Alhaji Haruna yace "ƙarya take bata sanmu ba, a gidan uban wa ta sanmu balle ta tattara wata hujja a kanmu, yanzu kana ina ne?"
"ina cikin gari mana, naje Asibiti ne wani yarfi yarinyar nan ta min na kasa ko miƙewa tsaye, na ɗauka ma na tashi daga aiki"
Alhaji Musa yace "wani sakarci ne zesa ku baro su acan, maza ka koma ku gana mata Azaba iya Azaba seta faɗi inda takaddun suke, idan ta faɗi inda suke ku kashe su kawai"
Saleh yace "What akan me za'a kashe ta?"
Alhaji Musa be saurari Saleh ba ya cigaba da wayar sa.
Me Adda yace "gaskiya Oga kisan Yarinya kamar wannan ba kamar kashe sauran mutane bane, tsaf wannan cinnakun zasuyi ram damu"
Alhji Haruna yace "ba wanda ze kama ku, zancen nan da muke maka gaba ɗaya mun siye jami'an tsaro ba wani bincike da'ake akan ɓatan nata, dan haka ka gaggauta zuwa jibi idan bata faɗa ba ka tirsasa ta, ta gaya maka wasu hujjoji take dasu sannan ka kashe mana su"
Me Adda yace "angama Oga"
Alhaji Haruna ya sharce gumi yace "bala'i, Musa anya ba dagaske yarinyar nan ta gano mu ba, karfa muje dagaske take"
"Rabu da ita ƙarya take, da dagaske ta sanmu da tuni ta ɗau mataki akanmu, amma kasan bamu gayawa Munir da Bukar hukuncin da muka yanke ba?"
Alhaji Haruna yace "Suma idan mun gaya musu hukuncin da za susa ayi mata kenan a kashe ta kawai, karta ja mana masifa"
Alhaji Musa ya kalli Saleh yace "wai kai meye naka na saka baki dan munce a kashe ta, kabi a sannu fa wallahi kar kasa musa a haɗa da kai, kabi umarnin mu kawai"
Saleh yayi murmushi yace "Tausayin Daula ne ya kamani wallahi, karka damu bazan baku kunya ba insha Allah dani za'a kammala komai nima in samu rabona"
"daka temaki kanka" cewar Alhaji Haruna, yayin da cikkunansu suka É—uri ruwa.
Yusuf yana nan zaune rungume da Widad, har duhu yayi gari ya waye, sam be bacci ba gani yake da yayi bacci Widad zata mutu, dan bugun zuciyar ta da yake ji shike tabattar masa tana da rai, dan wani lokacin har motsawa take.
A hankali Yusuf ya kwantar da ita, yayi taimama yayi sallar Asuba, shima gaba ɗaya jikinsa a sake yake babu ƙwari saboda azabar wahala, ga yunwa ga duka ga cizon sauro ga azabar sanyi dake gurin, amma gaba ɗaya yafi tausayawa Widad, lokaci lokaci yakan kwance hannun nata, ya goge jinin ya sake ɗaure mata, ga wani irin zazzafan zazzabi da ko sauka bayayi a jikinta.
A hankali Widad ta buÉ—e ido, sedai dishi dishi take gani bata gane komai, tana yi tana lumshe ido haka take kallon Yusuf.
Yusuf ya girgiza ta yace "Alhamdilillah, you are alive"
Bata iya amsa masa ba, sedai idonta ya sake rufewa
Yana rungume da ita, yayi shiru yana ta ambaton Allah, babu zato ba tsammani yaji ana ta sukuwa a saman roofing ɗin ɗakin, Yusuf ya ɗaga kai yana son gane meke faruwa haka? Cigaba da sukuwa akayi a gurin anata ƙoƙarin ɓare kwanon, can kuma se'aka dena, yaji anata ƙoƙarin buɗe ƙofar da suke ciki, waze gani Saleh ne ya shigo cikin ɗakin.
A gigice Yusuf yace "kaine? Da kai aka haɗa baki kenan aka mana haka?"
Saleh yace "baka da lokacin wannan tambayoyin, zuwa nayi na tseratar da ku, ka adana tambayoyinka, idan kun tsira seka yi su"
Hankalinsa ya kai kan hannun Widad dake sume yama zubar da jini, da sauri ya ƙaraso yace "meya sameta haka? Harbinta sukayi?"
Yusuf bece masa komai ba, sedai kallon tuhuma da yake ta binsa dashi.
Saleh yace "zaka iya tafiya kuwa?"
Yusuf ya jinjina masa kai alamar eh, "to taso maza"
Yusuf ya yunƙura ya miƙe, amma ƙafafunsa se rawa suke saboda dukan daya sha, ga uwa uba yunwar da yake ji.
Amma cikin jarumta, da sadaukarwa ya miƙe ya goya Widad a bayansa.
Suka fito daga gidan, Saleh ya maida gidan ya rufe, sannan ya ɓare saman roofing yayi hanya, sannan yayi musu jagora hannunsa ɗauke da compass dake nuna masa direction suka nausa cikin daji.
Yusuf ji yake kamar ze kifa, amma haka ya cigaba da tafiya, Saleh ya kalle shi yace "ko zaka sauketa in ta yaka?"
Yusuf ya girgiza kai yace "A'a karka damu"
Tafiya sukayi bata wasa ba, ƙafar Yusuf ko takalmi babu, ya dinga taka abubuwa danma ta cikin ciyayi suke kutsawa, haka suka dinga tafiyar cikin sauri, suna bi takan ciyayi dan kaucewa barin sawunsu yadda za'a gane hanyar da suka bi, daji ne har daji me sarƙaƙiyar tsiya, da manyan bishiyu.
Sunyi tafiya me nisan gaske sannan suka fito titi, sam Yusuf be san a ina suke bama, Saleh ya nunawa Yusuf mota yace "ya shiga"
Yusuf yayi turus ya kalli Saleh, a wahalce yace "wannan taimakon ma da kayi mana mungode, amma bazan hauba, Insha Allah zamu bar gurin nan".
"Yusuf, wallahi suka kamaku kashe ku zasuyi, da inada niyyar cutar daku da bazan ceceku ba"
Da ƙyar Yusuf ya yadda, ya hau motar, da alama Saleh ya gama shirya komai.
Shima Saleh haka yayi doguwar tafiya dasu a motar, tafiya kamar za'a bar duniya dazuka kawai suke ratsawa, tituna bakowa se su kaÉ—ai, Shiru ne ya wanzu tsakaninsu har suka fara fita gari.
Wani É—an madaidaicin Asibiti suka tarar a hanya, Saleh yayi parking Yasa Yusuf ya É—akko Widad suka shiga Asibitin.
Kuɗi Saleh ya ajiyewa likitan, dan haka ba wani dogon bincike suka karɓi Widad, Amma Yusuf yaƙi zuwa ko'ina, a gabansa aka cirewa Widad bullet, akace se an tafi neman jini za'a ƙara mata.
Yusuf yace a ɗibi nashi, Saleh yace "baze yuwu a ɗebi naka ba, kaima a galabaice kake akwai buƙatar a duba ka"
Yusuf ya dage sedai a gwada jininsa in zeyi a É—iba a sa mata.