Sashe 61
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mummy tace "kedai bari yarinya, ai komai yana tafiya daidai"
Suka kwashe da wata uwar dariya, hakan yayi daidai da shigowar Anwar, hakan yasa suka ja baki sukayi tsit.
Ganin yadda sam halin da Daula ke ciki baya gaban mahaifiyarsa da 'yan uwansa yasa ya girgiza kai, tunda Daula ya kwanta a Asibiti bata taɓa kwana a gurinsa ba, se tafi kwana uku ma bata je ba.
Hajiya Halima tace "Allah sarki yaron kirki, Anwar duk ka rame fa, anya baza' a nemi me kula da Alhaji a dinga biyansa ba, ba haƙƙinka bane yin jinyarsa, duk kayi wani iri jinya ba sauƙi fa"
Ya kalli mahaifiyarsa yace "Ciyar damu ɗaukae ɗawainiyar karatunmu da sauran buƙatunmu da yake haƙƙinsa ne? Me yasa lokacin da yakw ɗawainiyar damu baki ce masa ba haƙƙinsa bane, babanmu yayi mana ba tunda yana raye?"
Ya ajiye kayan hannunsa yayi waje zuciyar sa na ƙuna, da irin wannan hali na mahaifiyarsa.
Ramlah taja wani ɗan gajeren tsaki tace " Mummy ya kamata anemo wanda zasu ɓalle ƙofar ɗakin yarinyar nan, mu ɗibi abunda zamu ɗiba, kuma mu shiga ɗakin ubanta mu kwashi abunda muka samu kafin wancan manyan suzo"
Hajiya Halima tace "hakane, amma dole muyi komai a hankali naga Anwar yana neman ya gane halin da'ake ciki nikuma bazan so hakan ba"
Ramlah tace "Ai Mummy ki rabu da Yaya Anwar É—in nan kawai"
Saleh ne a hukumar 'yan Sanda na farin kaya, ya nemi ganawa da Sulaiman, ai kuwa be sha wata wahala ba saboda Kasancewar shima ma'aikacin tsarone.
Ya shiga Office ɗin Suleiman suka gaisa, Saleh ya gabatarwa Suleiman kansa sannan yace "kamar yadda nima jami' in tsaro ne nazo maka da wata mahimmiyar maganane akan jami'inku da'aka sace tare da 'yar gidan Daula"
Suleiman yace "ya akayi kasan jami' inmu ne? Ba kowa yasan Yusuf ɗan sanda bane"
Saleh yace "ba abun mamaki bane dan na san hakan, Amma yanzu ba wannan ne mafi a'ala ba, ka tsaya ka saurareni da kyau, na kuɓuttar da Jami'inku tare da 'yar gidan Daula"
Wani irin kallo Suleiman yayi masa yace "ya akayi kasan inda suke harka kuɓuttar dasu? Kenan dasa hannunka akan sacesun da' akayi"
Saleh yace "ka dena wannan muzuran, ka tsaya in maka bayani dan baka da ikon da zaka kamani ko gayawa duniya abunda ya faru, idan kayi haka kayi abakin ranka"
Nan Saleh ya warwarewa Suleiman komai sedai be faɗa masa ƙauyen daya bawa su Widad mafaka ba, Suleiman yayi matuƙar girgiza da jin labarin da Saleh ya gaya masa, Saleh yace "a yanzu haka babu wani bincike da akeyi akan ɓatansu, saboda sun siye jam'ian tsaro gaba ɗaya kuma suna harin rayuwar Daula duk saboda dukiyarsa, na fuskanci idan nayi wani kyakkyawan yunƙuri a gurin ceton Daula tabbas Asirina ze tonu, kuma zasu kasheni, kaima na gaya maka dan ka sani, ka samu iyayen Yusuf ka musu bayani, dan hankalinsu ya kwanta, sannan ka gargaɗesu akan suyi shiru da bakin su "
Suleiman ya jinjina kai yace ai abunda za'ayi yanzu shine, zan É—aukeka muje gaban mahaifiyar Yusuf kayi mata bayani da bakinka dan ta samu nutsuwa"
Saleh yace  "kana ganin babu matsala?, bafa nason a ganeni"
Suleiman yace "babu wata matsala insha Allah, hankalin mahaifiyarsa ne yaƙi kwanciya, ta damu sosai"
Saleh yace "shikenan muje"
Suleiman yayi musu jagora har gidansu Yusuf, ba ƙaramin farinciki tayi ba da jin an kuɓuttar mata da Yusuf ɗinta, sedai jin an ɓoye shi a ƙauye, ga kuma bata san ranar dawowarsa ba yasa tace "Allah sarki Yusufa na, koze iya rayuwar ƙauye? Be saba ba nace ko zaku kaini in ganshi?"
Saleh yace "A'a hakan bame yuwuwa bane, akwai hatsari a cikin hakan, sedai zanyi recoding É—in muryarki in kai masa, amma baze yuwu in kaiki inda yake ba"
Umma tace "ynzu dai dan Allah dagaske kake ya tsira baya hannun Azzaluman da suka sace shi?"
Saleh yace "tabbas basa nan, ya kuɓuta"
Umma tace "Allah kaine abun godiya, ubangiji Allah ya ƙara tsare su"
Widad kuwa wunin ranar nan ji take kamar ba ita ba, wai ita da bakinta ta Amince da Auren Yusuf, abun da tafi tsana a rayuwar ta yau da bakinta ta amince.
Amma da:ace wannan me korayen haƙoran me kama dana horo tazo ta dinga kwana da ita, ko wannan yaran nasu masu kallon jaraba, gara tayi maleji ta Auri Yusuf ɗin su dinga kwana guri ɗaya, tunda duk abu dai shi ta sani.
Widad sam bata iya cin Abincin da ake kawo musu, saboda gaba É—aya kwanon da'ake kawo Abincin kansa idan ta kalla be mata ba ba zata ci ba, se taji kamar tayi amai, Yusuf yayi ta fama da ita ga larura tana fama, ga rashin cin Abinci.
Haka a daddafe suka kwana uku, kullum tana kan katifa, Yusuf yana bakin ƙofa a ƙasa, idan ta fito tsakar gidan nan to tare da Yusuf ne ze rakata banɗaki, shima bata shiga banɗakinsu, wannan ɗakin da ba kowa a ciki take wankanta, shima idan tayi abunda zata yi tun safe bata sake yadda ko fitsari ta sake yi.
Ko sannu bata taɓa haɗata da mutan gidan ba, shiyasa suke zaton ko bata jin hausa ma, haka suke wuni a ɗaki bata yadda Yusuf ya fita ya barta, tsakaninsa da ita sedai kallon kallo.
Babban abunda yake ƙara bata haushi be wuce yadda data fito, gaba ɗaya sesu koma kallonta ba, sekace sunga wasu halittu daban, ita tarasa meye abunda suke kallo.
Yanzu tana ɗan iyayiwa kanta wasu abubuwan, dukda bata gama warkewa ba, bata cin Abinci sosai, dukda a da ɗinma ba wani ci take ba, Yanzu kam cimar ƙauyen nan ta sha banban da irin wadda ta saba gani, gaba ɗaya kalar Abincinsu yasha banban da wanda ta saba gani ko ta saba ci.
Yusuf yana son yayiwa megari bayani, amma yana tsoron irin kallon daze masa kuma gashi besan me Saleh yace masa ba game dasu
A haka suka kwana uku, ranar kwana na ukun da yamma ba tsammani suka ji salamar Saleh, ba ƙaramin farinciki Yusuf yayi da zuwan Saleh ba, yayo musu siyayya cikin ledoji.
Saleh suka gaisa da Yusuf, yace "Yusuf ya zaman haƙuri ya me jiki kuma?"
Yusuf yace "Alhamdilillah, me jiki tana samun sauƙi"
Saleh yace "fatan dai komai lafiya, kuna lafiya kuda mutan gidan?"
Yusuf yace "Alhamdilillah komai lafiya ƙalau"
Saleh ya kalli Widad yace "Autar Daula ya jikin naki?"
Banza tayi masa ba tace komai ba, Saleh yace "hmm aike in dan halinki ne ko kashe ki za'ayi mutum baze ceceki ba, sedai amiki dan Allah dan karamcin mahaifinki, mace se tsabar girman kai da izzar tsiya, yanzu dai dole ki sauke su ki rungumi ƙaddarar da tayi kutse cikin rayuwar ki ba tare da kin shirya mata ba, ki sani abunda kika gayawa wanda sukayi garkuwa da ku, sun Sanarwa da wanda suka sa a sace ku, dan haka idanma dagaske kin san wanda suka sa a saceku inama baki sani ba kikace kin sani, sun bada umarnin a kasheku, zuwa yanzu basu san kun kuɓuta ba, da zarar sun farga kun gudu zasu saka ɗambar nemanku, dan haka idan kin gadama ki haƙura ki zauna anan na wani ɗan lokaci domin ki tserar da rayuwar ki, in baki ga dama ba kuma kiyi yadda kike so "
Yadda Widad take a kashingiÉ—e ko motsi ba tayi ba, balle Saleh yasa ran jin wani abu daga gareta.
Yusuf ne yace " Ayi dai haƙuri, Insha Allah zata zauna ma, kuma mungode sosai da taimakon da kayi mana Allah ya saka da alkhairi, ya Yallaɓai kuwa? "
Saleh yace "Yana nan ƙalau, dan ina daf da sanar dashi cewar kun tsira, kasan komai nima se nayi lissafi nake yinshi, domin ɓadda sahu, jiya munje gidanku na gana da mahaifiyarka ma"
Da sauri Yusuf ya É—ago ya kalle shi zeyi magana, Amma Saleh ya girgiza masa kai.
Yusuf yace "Amma ya akayi kasan wanda suka sacemu, harka kuɓutar damu?"
Saleh yace "labarin dogone Malam Yusuf, uwa ɗakinka tasa an kama ɗan uwana an tsare shi tsawon shekaru goma, akan zargin dasa hannunsa akan kisan mahaifiyarta, na haɗa kai da maƙiyanta domin in rama abunda tayi min, sedai suma maƙiyan nata kansu kawai suka sani basu da adalci, gefe guda dukda zargin da yake kan ɗan uwana mahaifinta be fasa kyautatamin ba, yana matuƙar girmamani yana kyautatamin ga kuma kai Yusuf da babu ruwan ka, shiyasa na ceceku ba dan halinta ba Wallahi "
"I don't judge based on Assumptions, what happens ten years back is still dancing in my memory, abunda ya faru a wancan lokacin ina jinsa a raina kuma ina ganinsa a idona tamkar a yanzu yake faruwa, da sa hannun Bala akan abunda ya faru, kuma ko ka ceceni ko kar ka ceceni hakan baze taɓa canza ƙaddarata ba, nasan wanda suke bibiyar abun nan tsawon shekaru suna da Alaƙa da wanda suka kashe mahaifiyata, kallona kawai kuke but am beyond your expectations, idan kaje ka ƙara tabattar musu ko bayan raina se sun Wulaƙanta se Asirinsu ya tonu wulaƙanta mafi muni a duniya "
Tuni Hawaye ya wanke fuskarta, yadda take maganar zaka san abun yana taɓa mata zuciya sosai, Yusuf yace
"Amm inaga ku bar wannan maganar, it's hurt her feelings kuma kaga bata da lafiya, dama ina son muyi wata magana da kai ne"
Saleh yace "Ina jinka"
Yusuf yace "kaga zaman da muke da ita a ɗaki ɗaya be halarta ba, tunda ba muharrama ta bace, kuma kasan ba zata yadda matan gidan nan su kula da ita ba, ga yanayi na jinya tana ciki, da nace mu raba ɗaki taƙi yadda, amma munyi shawarar zamuyi Aure, yadda zan iya jinyarta lokacin da Allah ya ƙaddara zamu bar garin nan semu rabu, da naso in yiwa megari bayani, amma ban san yadda kuka yi da shi ba"
Saleh yace "eh to ni namanta kam banyi tunanin raba muku ɗaki ba, taɓ amma wannan zaka aura? Allah ya baka haƙuri da juriya, tashi muje gurin me garin, dama Jibi in Allah ya kaimu Juma'a se'a ɗaura"
Widad dai bata tanka musu ba, suka tashi suka tafi turakar mai gari.
Suka kwashe da wata uwar dariya, hakan yayi daidai da shigowar Anwar, hakan yasa suka ja baki sukayi tsit.
Ganin yadda sam halin da Daula ke ciki baya gaban mahaifiyarsa da 'yan uwansa yasa ya girgiza kai, tunda Daula ya kwanta a Asibiti bata taɓa kwana a gurinsa ba, se tafi kwana uku ma bata je ba.
Hajiya Halima tace "Allah sarki yaron kirki, Anwar duk ka rame fa, anya baza' a nemi me kula da Alhaji a dinga biyansa ba, ba haƙƙinka bane yin jinyarsa, duk kayi wani iri jinya ba sauƙi fa"
Ya kalli mahaifiyarsa yace "Ciyar damu ɗaukae ɗawainiyar karatunmu da sauran buƙatunmu da yake haƙƙinsa ne? Me yasa lokacin da yakw ɗawainiyar damu baki ce masa ba haƙƙinsa bane, babanmu yayi mana ba tunda yana raye?"
Ya ajiye kayan hannunsa yayi waje zuciyar sa na ƙuna, da irin wannan hali na mahaifiyarsa.
Ramlah taja wani ɗan gajeren tsaki tace " Mummy ya kamata anemo wanda zasu ɓalle ƙofar ɗakin yarinyar nan, mu ɗibi abunda zamu ɗiba, kuma mu shiga ɗakin ubanta mu kwashi abunda muka samu kafin wancan manyan suzo"
Hajiya Halima tace "hakane, amma dole muyi komai a hankali naga Anwar yana neman ya gane halin da'ake ciki nikuma bazan so hakan ba"
Ramlah tace "Ai Mummy ki rabu da Yaya Anwar É—in nan kawai"
Saleh ne a hukumar 'yan Sanda na farin kaya, ya nemi ganawa da Sulaiman, ai kuwa be sha wata wahala ba saboda Kasancewar shima ma'aikacin tsarone.
Ya shiga Office ɗin Suleiman suka gaisa, Saleh ya gabatarwa Suleiman kansa sannan yace "kamar yadda nima jami' in tsaro ne nazo maka da wata mahimmiyar maganane akan jami'inku da'aka sace tare da 'yar gidan Daula"
Suleiman yace "ya akayi kasan jami' inmu ne? Ba kowa yasan Yusuf ɗan sanda bane"
Saleh yace "ba abun mamaki bane dan na san hakan, Amma yanzu ba wannan ne mafi a'ala ba, ka tsaya ka saurareni da kyau, na kuɓuttar da Jami'inku tare da 'yar gidan Daula"
Wani irin kallo Suleiman yayi masa yace "ya akayi kasan inda suke harka kuɓuttar dasu? Kenan dasa hannunka akan sacesun da' akayi"
Saleh yace "ka dena wannan muzuran, ka tsaya in maka bayani dan baka da ikon da zaka kamani ko gayawa duniya abunda ya faru, idan kayi haka kayi abakin ranka"
Nan Saleh ya warwarewa Suleiman komai sedai be faɗa masa ƙauyen daya bawa su Widad mafaka ba, Suleiman yayi matuƙar girgiza da jin labarin da Saleh ya gaya masa, Saleh yace "a yanzu haka babu wani bincike da akeyi akan ɓatansu, saboda sun siye jam'ian tsaro gaba ɗaya kuma suna harin rayuwar Daula duk saboda dukiyarsa, na fuskanci idan nayi wani kyakkyawan yunƙuri a gurin ceton Daula tabbas Asirina ze tonu, kuma zasu kasheni, kaima na gaya maka dan ka sani, ka samu iyayen Yusuf ka musu bayani, dan hankalinsu ya kwanta, sannan ka gargaɗesu akan suyi shiru da bakin su "
Suleiman ya jinjina kai yace ai abunda za'ayi yanzu shine, zan É—aukeka muje gaban mahaifiyar Yusuf kayi mata bayani da bakinka dan ta samu nutsuwa"
Saleh yace  "kana ganin babu matsala?, bafa nason a ganeni"
Suleiman yace "babu wata matsala insha Allah, hankalin mahaifiyarsa ne yaƙi kwanciya, ta damu sosai"
Saleh yace "shikenan muje"
Suleiman yayi musu jagora har gidansu Yusuf, ba ƙaramin farinciki tayi ba da jin an kuɓuttar mata da Yusuf ɗinta, sedai jin an ɓoye shi a ƙauye, ga kuma bata san ranar dawowarsa ba yasa tace "Allah sarki Yusufa na, koze iya rayuwar ƙauye? Be saba ba nace ko zaku kaini in ganshi?"
Saleh yace "A'a hakan bame yuwuwa bane, akwai hatsari a cikin hakan, sedai zanyi recoding É—in muryarki in kai masa, amma baze yuwu in kaiki inda yake ba"
Umma tace "ynzu dai dan Allah dagaske kake ya tsira baya hannun Azzaluman da suka sace shi?"
Saleh yace "tabbas basa nan, ya kuɓuta"
Umma tace "Allah kaine abun godiya, ubangiji Allah ya ƙara tsare su"
Widad kuwa wunin ranar nan ji take kamar ba ita ba, wai ita da bakinta ta Amince da Auren Yusuf, abun da tafi tsana a rayuwar ta yau da bakinta ta amince.
Amma da:ace wannan me korayen haƙoran me kama dana horo tazo ta dinga kwana da ita, ko wannan yaran nasu masu kallon jaraba, gara tayi maleji ta Auri Yusuf ɗin su dinga kwana guri ɗaya, tunda duk abu dai shi ta sani.
Widad sam bata iya cin Abincin da ake kawo musu, saboda gaba É—aya kwanon da'ake kawo Abincin kansa idan ta kalla be mata ba ba zata ci ba, se taji kamar tayi amai, Yusuf yayi ta fama da ita ga larura tana fama, ga rashin cin Abinci.
Haka a daddafe suka kwana uku, kullum tana kan katifa, Yusuf yana bakin ƙofa a ƙasa, idan ta fito tsakar gidan nan to tare da Yusuf ne ze rakata banɗaki, shima bata shiga banɗakinsu, wannan ɗakin da ba kowa a ciki take wankanta, shima idan tayi abunda zata yi tun safe bata sake yadda ko fitsari ta sake yi.
Ko sannu bata taɓa haɗata da mutan gidan ba, shiyasa suke zaton ko bata jin hausa ma, haka suke wuni a ɗaki bata yadda Yusuf ya fita ya barta, tsakaninsa da ita sedai kallon kallo.
Babban abunda yake ƙara bata haushi be wuce yadda data fito, gaba ɗaya sesu koma kallonta ba, sekace sunga wasu halittu daban, ita tarasa meye abunda suke kallo.
Yanzu tana ɗan iyayiwa kanta wasu abubuwan, dukda bata gama warkewa ba, bata cin Abinci sosai, dukda a da ɗinma ba wani ci take ba, Yanzu kam cimar ƙauyen nan ta sha banban da irin wadda ta saba gani, gaba ɗaya kalar Abincinsu yasha banban da wanda ta saba gani ko ta saba ci.
Yusuf yana son yayiwa megari bayani, amma yana tsoron irin kallon daze masa kuma gashi besan me Saleh yace masa ba game dasu
A haka suka kwana uku, ranar kwana na ukun da yamma ba tsammani suka ji salamar Saleh, ba ƙaramin farinciki Yusuf yayi da zuwan Saleh ba, yayo musu siyayya cikin ledoji.
Saleh suka gaisa da Yusuf, yace "Yusuf ya zaman haƙuri ya me jiki kuma?"
Yusuf yace "Alhamdilillah, me jiki tana samun sauƙi"
Saleh yace "fatan dai komai lafiya, kuna lafiya kuda mutan gidan?"
Yusuf yace "Alhamdilillah komai lafiya ƙalau"
Saleh ya kalli Widad yace "Autar Daula ya jikin naki?"
Banza tayi masa ba tace komai ba, Saleh yace "hmm aike in dan halinki ne ko kashe ki za'ayi mutum baze ceceki ba, sedai amiki dan Allah dan karamcin mahaifinki, mace se tsabar girman kai da izzar tsiya, yanzu dai dole ki sauke su ki rungumi ƙaddarar da tayi kutse cikin rayuwar ki ba tare da kin shirya mata ba, ki sani abunda kika gayawa wanda sukayi garkuwa da ku, sun Sanarwa da wanda suka sa a sace ku, dan haka idanma dagaske kin san wanda suka sa a saceku inama baki sani ba kikace kin sani, sun bada umarnin a kasheku, zuwa yanzu basu san kun kuɓuta ba, da zarar sun farga kun gudu zasu saka ɗambar nemanku, dan haka idan kin gadama ki haƙura ki zauna anan na wani ɗan lokaci domin ki tserar da rayuwar ki, in baki ga dama ba kuma kiyi yadda kike so "
Yadda Widad take a kashingiÉ—e ko motsi ba tayi ba, balle Saleh yasa ran jin wani abu daga gareta.
Yusuf ne yace " Ayi dai haƙuri, Insha Allah zata zauna ma, kuma mungode sosai da taimakon da kayi mana Allah ya saka da alkhairi, ya Yallaɓai kuwa? "
Saleh yace "Yana nan ƙalau, dan ina daf da sanar dashi cewar kun tsira, kasan komai nima se nayi lissafi nake yinshi, domin ɓadda sahu, jiya munje gidanku na gana da mahaifiyarka ma"
Da sauri Yusuf ya É—ago ya kalle shi zeyi magana, Amma Saleh ya girgiza masa kai.
Yusuf yace "Amma ya akayi kasan wanda suka sacemu, harka kuɓutar damu?"
Saleh yace "labarin dogone Malam Yusuf, uwa ɗakinka tasa an kama ɗan uwana an tsare shi tsawon shekaru goma, akan zargin dasa hannunsa akan kisan mahaifiyarta, na haɗa kai da maƙiyanta domin in rama abunda tayi min, sedai suma maƙiyan nata kansu kawai suka sani basu da adalci, gefe guda dukda zargin da yake kan ɗan uwana mahaifinta be fasa kyautatamin ba, yana matuƙar girmamani yana kyautatamin ga kuma kai Yusuf da babu ruwan ka, shiyasa na ceceku ba dan halinta ba Wallahi "
"I don't judge based on Assumptions, what happens ten years back is still dancing in my memory, abunda ya faru a wancan lokacin ina jinsa a raina kuma ina ganinsa a idona tamkar a yanzu yake faruwa, da sa hannun Bala akan abunda ya faru, kuma ko ka ceceni ko kar ka ceceni hakan baze taɓa canza ƙaddarata ba, nasan wanda suke bibiyar abun nan tsawon shekaru suna da Alaƙa da wanda suka kashe mahaifiyata, kallona kawai kuke but am beyond your expectations, idan kaje ka ƙara tabattar musu ko bayan raina se sun Wulaƙanta se Asirinsu ya tonu wulaƙanta mafi muni a duniya "
Tuni Hawaye ya wanke fuskarta, yadda take maganar zaka san abun yana taɓa mata zuciya sosai, Yusuf yace
"Amm inaga ku bar wannan maganar, it's hurt her feelings kuma kaga bata da lafiya, dama ina son muyi wata magana da kai ne"
Saleh yace "Ina jinka"
Yusuf yace "kaga zaman da muke da ita a ɗaki ɗaya be halarta ba, tunda ba muharrama ta bace, kuma kasan ba zata yadda matan gidan nan su kula da ita ba, ga yanayi na jinya tana ciki, da nace mu raba ɗaki taƙi yadda, amma munyi shawarar zamuyi Aure, yadda zan iya jinyarta lokacin da Allah ya ƙaddara zamu bar garin nan semu rabu, da naso in yiwa megari bayani, amma ban san yadda kuka yi da shi ba"
Saleh yace "eh to ni namanta kam banyi tunanin raba muku ɗaki ba, taɓ amma wannan zaka aura? Allah ya baka haƙuri da juriya, tashi muje gurin me garin, dama Jibi in Allah ya kaimu Juma'a se'a ɗaura"
Widad dai bata tanka musu ba, suka tashi suka tafi turakar mai gari.