← Book details Akidata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 82

Sashe 35

Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yusuf yace  "No bana son yawan zuwa gurin bana son a ganni a gurin, ta Email ɗina nake so ka turamin, zan baka ɗaya bisa huɗu na kuɗin seka turomin zan baka sauran, bana saɓa Alƙawari dan haka kaima karka saɓa"

Haka ya amince da wannan yarjejeniyar.

*********************************

Saleh ne yake kaiwa yana komowa, Alhaji Bukar ya fito ya sa meshi, ya kalle shi ya yatsuna fuska yace  "lafiya?"

A fusace Saleh yace  "dole ka tambaye ni lafiya, me kasa akayiwa ɗan uwana? Ta yaya zanje in ganshi lafiya ƙalau kawai labari ya isheni wai bashi da lafiya"

Alhaji Bukar yace  "dakata! Da ina son ganin bayan ɗan wanka da tun a shekarun baya gudun karya tona min Asiri da tuni ya bar duniya, zaman kotu daza'a koma bani da fargaba sam, inada ƙwararrun lawyoyi da na biya su wanda zasu tsayamin, dan haka ba abunda zesa in yiwa ɗanuwanka wani abu"

"Au haka ma zakece? Wato kai a wanke ka shikuma ya cigaba da zama a prison ko? Ga wannan mahaukaciyar Yarinyar taje ta sameni, tace muddin wani abu ya samu Bala ni zan maye gurbin sa, me kake tunani ne wai? Yarinyar nan tana da kuÉ—i zata iya aikata duk abunda taso"

Alhaji Bukar ya ɗan daki kafaɗar Saleh yace 

"shiyasa nace kazo mu haÉ—a kai mu raba ta da dukiyar, mu mallaki gundurin dukiyar da muke ta farauta muga ta tsiya"

Saleh ya make hannun Bukar yace  "Niba dukiyar tace a gabana ba, babu irin kyautatawar da mahaifinta be minba, ni dukiyar sa bata gabana, ni burina a wanke ɗan uwana a fito da shi daga kurkuku tunda bashi da laifi"

Wata uwar dariya Alhaji Bukar ya saki yace  "ubanwa yace maka bashi da laifi? Lallai har yanzu kanka a kwano yake, ka ƙyaleshi ya girbi abunda ya shuka, kazo a haɗa kai a nemi Arziki".

Yana gama maganar ya wuce ya bar Saleh a gurin.

************************************

Yusuf yaita safa da Marwa yana duba wayar sa, ba zato Sega abunda ya nema an turo masa ta Email É—insa, message É—in na shigowa Manager ya kira Yusuf, Yusuf yayi masa godiya sannan ya tura masa sauran kuÉ—in, wanda kuÉ—aÉ—en da Widad take bashi ne, dan wani lokacin idan ta bushi iska se yaga alert.

Yusuf ya tura message ɗin cikin System ɗinsa da sauran wayyoyinsa, nan Yafara aiki akan bayanan da aka turo masa, ba ƙaramin mamaki ne ya kamashi ba ganin mutanen da suka ka kama ɗakuna a wannan watan zuwa ranar da suka je Hotel ɗin tare da Widad, wanda ya kama ɗaki ranar da sukaje shida Widad yafi bashi mamaki, Abun tambayar anan shine 'ya akayi Widad tasan da zuwan mutumin gurin? Me Widad taje yi? Gurinwa taje?' me ta gani ya sata kuka? '
Yusuf zuciyarsa ɗaya baya jin Widad zata aikata wani mummunan aiki na alfasha, amma akwai wani ɓoyayyen abu da yakamata ace ya sani.

Kamar wanda aka mintsina ya miƙe ya shirya, ya duba agogonsa ƙarfe takwas na dare, haka ya fita ya tari abun hawa ya tafi unguwar su Nurat.

Unguwar tasu shiru, amma haske ko ina da yake rukunin Gidajen masu kuɗi ne, har ƙofar gidan aka kaishi aka sauke.
Ya sauka ya nufin gidan su Nurat, ya tsaya suka gaisa da megadin, Yusuf yace  "Dan Allah gurin Nurat nazo"

Maigadin ya kalle shi yace "tasan da zuwanka ne?"

"A'a, bata sani ba, Amma ka gaya mata tayi baƙo"

Mai gadi ya kira Nurat a waya yasa a hansfreee ya gayamata tayi baƙo.

"Babu wanda zan haÉ—u dashi yau, dan haka ba zanga kowa ba"

Yusuf yace "kace mata Widad ce ta aiko ni"

Aida jin Widad ce tayo aiken Nurat ta rikice, tace "Kaishi guest room, ina zuwa"

Maigadin yayiwa Yusuf jagora, har wani katafaren Falo, Yusuf ya zauna yana jiran fitowarta.
Ko mintuna goma ba'ayi ba se gata ta fito, ta ƙaraso cikin falon da hanzari, sedai tana arba da Yusuf ta rikice ta buɗe baki zata yi ihu ta gudu, Cikin zafin nama Yusuf ya riƙeta tare da toshe mata baki.

"Meye haka kamar kinga wani aljani ko mugu? Kinga fa mutum ne ni"

Fizgewa tayi, ta shiga Ja da baya ta kwaɓe fuska zata yi kuka tace
"Nifa wallahi tun ranar da kuka bar nan, Widad bata ƙara zuwa gidan mu ba"

Gaba É—aya Nurat ba tafi sa'ar Widad ba, sedai Widad tafi Nurat jiki sannan Izzarta da jin kanta yake sa ka ganta kamar Babba.

Yusuf yace  "Haba Nur, nifa ba wani abu zanyi miki ba kawai tambayoyi zan miki in tafi"

Girgiza kai ta shiga yi tana kiran sunan Daddy a hankali.

"Daddyn yana nan ne?" ya tambaye ta

Ta girgiza masa kai alamar A'a

"to ki nutsu ki zauna, hira za muyi in tafi"

A hankali ta zauna, tana rarraba ido dan a tsorace take da Yusuf, dan ba zata manta randa Yusuf ya shaƙeta ba, har yayi barazanar sace taba.

Yusuf yace "Calm down dear, hira zamuyi kawai in tafi"

Ganin taƙi sakin jikin ta yasa Yusuf ya miƙe ya zaro komai na Aljihunsa, dan ya tabattar mata da babu wani makami a tare dashi.

Ya kalleta yana ɗan nazarin ta sannan yace 
"ko ki tambaye ni ina Widad ko? Tun ranar da ta bar nan baki sake neman ta ba"

"Na kirata bata É—aga wayata ne, nasan bazata sake yarda dani ba"

"Waye yace miki ba zata sake yarda dake ba? She's very simple and kind, but why do you attempt to kidnapped her?"

Kamar Nurat zatayi kuka tace  "bafa laifi na bane, Daddy ne"

Yusuf ya ɗan ƙara matsowa yace  "Amma me tayi wa Daddy haka da zesa a saceta?" yai maganar yana kallon idon Nurat, Yarinya ce dan haka yake binta a sannu cikin hikima

ÆŠan shiru tayi sannan tace "Nifa ban sani ba"

"Haba me sunan manya, Haske maganin duhu, baki kama da maƙaryata ba, ni ya akayi ma kika san Widad har kuke hulɗa bayan bata son mutane?"

"Nifa ba wani hulɗa mukeyi sosai ba, da tun ina ƙarama, gidan su na U. K yana kusa da namu daga baya suka dawo Nigeria shine... Sekuma tayi shiru tana satar kallon Yusuf.

"Shine me? "

"Dad É—ina sunyi faÉ—a da Daddynta akan Siyasa, shikenan abunda nasani, Amma dan Allah karka gayamata Daddy nane yasa ayi kidnapping É—inta idan ta sani, zata sa a kai Daddy na prison ne"

"bazan gaya mata ba, ai kin gayamin gaskiya, amma naga Daddynta É—an kasuwa ne ba Siyasa ba me zesa suyi faÉ—a da Daddynki akan siyasa"

"to ainima bakomai na sani ba, muna yara lokacin Amma tabbas sunyi faÉ—a ne shine yake son ya rama akan Widad, amma ni ban san me yake so yayi mata ba"

Yusuf yace "shikenan nagane, gaskiya you are so kind dear, Insha Allah bazan bari taji ba, Amma dan Allah karki bari a cutar da ita, kinga marainiya ce ita abun tausayi, ke kina da Mum da Dad É—inki ita kuma she's orphan"

Jinjina masa kai kawai tayi.

Yusuf yace "Bani wayarki in sami ki lambata, se mudinga gaisawa ni daga yau nayi ƙawa, ni zan maye miki gurbin ƙawancen ki da Widad"

Kallon sa tayi ta ɗanyi murmushi yadda yake magana ya burgeta, bashi da hayaniya, ya iya tsara magana daki daki, se yanzu ta gane ranar da yayi mata wannan barazanar ne ya koma kamar wani mugu amma ba haka yake ba, ta miƙa masa wayar sannan tace 
"Amma ni ban sanka a Family É—insu ba, waye kai a gurin ta?"

Yusuf yayi murmushi yace
"i don't belong to her family, but a very important person attached to her destiny"

Kallon sa tayi cike da rashin fahimta za tayi magana ya kashe mata ido É—aya, gaba É—aya seta sunkuyar da kai ta kasa maganar, ya daÉ—e yana daddana wayarta, ita kuma ta kasa cewa komai.
Seda ya gama abunda yake sannan ya miƙo mata wayar yace 

"Nagode sosai ƙawata, Allah ya bar zumunci, ni zan koma naji daɗin kasancewa dake da wannan hirar da mukayi"

Murmushi tayi tareda sunkuyar da kai tace  "baka gayamin sunan ka bafa"

"Sunana Abokin Nurat, Just call me Aboki or any name you like, good night Nur"

Ya ƙarasa maganar tare da nufar hanyar fita yana addu'a Allah ya  shiga lamarin sa akan wannan aiki me hatsarin gaske da yake yi, yasa hanyar da ya ɗakko ta zama mafita ga al'amuran.
Yayinda Nurat ta rakashi da ido har ya fice

Nurat tana komawa cikin gida Maman ta tace
"Ke lafiya kuwa? Waye wannan yazo kika daÉ—e haka?"
"Abokina ne yazo muka gaisa" tai maganar cike da basarwa ta shige É—akin ta tana tunanin Yusuf

(Masha Allah, daga wannan posting bana tunanin zan kuma wani posting se Allah ya kaimu ranar Asabar insha Allah, gobe in Allah ya yadda zan fara jarrabawar ƙarshe ta makaranta, ku sani a addu'oinku please 🙏 🙏 🙏
Dana kammala exams insha Allah zanyi ƙoƙari ku dinga samun update akan lokaci, comments ɗinku zesa kudinga samun update kullum, idan kun shirya yanzu aka fara wasan, ba'a fara komai ba thank you for being with me 😍 😍 😍)

Domin gyara sharhi ko shawara, feel free to contact me
Ayshercool
07063065680                   

                     _*AƘIDA TA*_
   

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in

                              PART1
                                  
                                  Page 14

ELEGANT ONLINE WRITER'S
Chapter 35 · 0% Book details