Sashe 79
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Isa yace "Ameen ya Allah, kalli duk manyan motocin dake gidan nan tabi ta siyar, kamar dasu tazo se facaka suke da kuÉ—i, Kai ta wani fannin yanzu bana ganin laifin 'yar masu gida da take musu rashin mutunci"
Murtalah yace "dama Hausawa sunce,' kada Allah ya kawo ranar yabo' duk rashin mutuncin da take Yusuf se yayi ta kare ta, se yanzu nake ganin gaskiyar zancensa da yace bata yiwa mutum wulaƙanci seya yi mata laifi"
Nura yace "Mhmm Ai kawai Allah yasaka mana, amma gidan nan ana abubuwa sedai fatan Allah ya kyauta"
Duk inda Hajiya Sarah tasan zata buga ta buga, amma anƙi sakin Anwar, gaba ɗaya ta rasa inda zata tsoma ranta, Anbi an toshe duk wata hanya da zata saka a samu belin Anwar.
Yanzu ma haka ta dawo fakan fakan kamar korarriya, a mugun guje ta shigo da mota gidan.
Tana shiga ta fara kiran "Ramlah! Ramlah! Ke Amal kuna inane?"
Amal ta fito tace "Mummy Ramlah fa bata nan"
"gidan ubanwa taje?"
Amal tace "sun fita ita da Fahad"
"zanci ubanta ita da Fahad ɗin kuwa, ai tunda ubansa ya watsa min ƙasa a ido, to tabbas zan masa rashin mutunci, zan nuna masa wacece Halima idan ya manta"
Amal tace "Mummy É—an uwan naki?"
"Eh shi É—in, tunda bani da kima a idon sa, nima zan nuna masa bashi da ita a nawa idon"
Amal tace "Mummy a bi dai komai a hankali, kar azo ayi aika aika"
Hajiya Halima tace "dalla rabu dani, ze gane ni ya taɓa, ai ɗa befi ɗa ba, yasani yaron nan besan inda aka kaai mutumin nan ba, amma se cemin yake wai in ƙyale doka tayi aikinta, na zagi dokar shi doka nawa yayi fatali da a rayuwar sa, zega tsiya"
Tai part É—inta tana cigaba da banbami, kamar wadda ke shirin Zarewa.
Saleh da Yusuf da É—an megari suka tafi kai Yusuf Asibiti, aka bar Widad da mutan gida tana ta faman yi musu kuka.
Gwaggo da Hindu ne suka iya zaman rarrashin Widad.
Hari tace wai ke Wudas daga miji na zazzaɓi seki zauna kita mana kuka, memakon ki masa Addu'a "
Ko kallon Hari ba tayi ba, ta miƙe ta tafi ɗakinsu tayi kwanciyarta tana cigaba da kuka.
Nurat suka dinga communicatinga da cousin É—inta akan yadda za'ayi belin Anwar.
Yanzu ma tana kwance akan gadonta hannunta É—auke da waya, tace" Brother ya ake ciki ne? Yakamata a gaggauta fitar da Anwar bashi da laifin komai fa"
"Nurat, kince bakyason asan muna ƙoƙarin belinsa, dan haka nake taka tsantsan, sedai abunda na gano shine tsare Anwar da akayi da manufa akayi shi, idan muka matsa tabbas za'a gano ke kikasa ayi belinamsa, tunda an san alaƙar dake tsakanin mu"
Cikin karaya Nurat tace "yanzu Brother babu abunda zaka iyayimin, Anwar be cancanci ya zauna a gurin nan ba"
Yace "Nurat, lawyan mahaifiyarsa ma yana ta ƙoƙari, amma har yanzu sun hana belinshi bansan meye abunyi ba, amma meyasa kika damu ya fita bayan kin san munin Alaƙar dake tsakanin mahaifinki da Daula?"
"Brother, idan akazo batun gaskiya da adalci ba'a kawo maganar alaƙa, an cutar da Anwar fiye da yadda kake zato, shikaɗai ne akan lamarin rashin lafiyar Alhaji Nasir, amma kalli abunda ya biyo baya, kodai an masa hakane dan a tozarta shi, ko kuma wanda ya sace shine yake son wanke kansa ta hanyar sawa a kama Anwar "
Barrister yace "Amma abun da mamaki ta yaya za'a iya sace mutum Attajiri kamar wannan a gadon Asibiti, kuma babu wani ƙwaƙwaran bayani, abun da mamaki fa"
Nurat tace "Brother, dan Allah idan kana da dama ina son kazo in ganka, ina son mu tattauna wani zance da kai dan Allah"
Barrister yace "Fara gayamin mana"
"A'a Brother, nidai so nake ina ganka, akwai magana ne a bakina"
"shikenan karki damu, Insha Allah idan ma samu lokaci zanzo insha Allah"
"Yawwa brother nagode sosai"
Ta kashe wayarta ta ajiye, shiru tayi abubuwa da dama suna damun zuciyarta, har yanzu bata ji alamar labarin inda su Yusuf suke ba, har yanzu bata sake jin wani magana game dasu ba, ta shiga tuna hirar da suka yi da Amal akan alaƙar Widad da Yusuf, ji tayi tana gumi dukda sanyin AC dake ɗakin nata, amma ta shiga haɗa gumi, miƙewa tayi ta tafi toilet da niyyar ta watsa ruwa ta rage damuwa.
Har bayan magariba babu labarin dawowar su Yusuf, nan fa Widad ta sake gigicewa, ta shiga sintir a gidan nan tana  "Allah ka duba Yoseef ka bashi lafiya, Allah ka bashi lafiya ba danni ba"
Gaba ɗaya tausayin ta ya hana Gwaggo nutsuwa, se aikin rarrashin Widad take, ita kuwa Hari harta ƙule saboda ganin abun na Widad take kama harda shagwaɓa dan taga ana lallaɓata, kawai dan mutum yana zazzaɓi ta cikawa mutane gida da ihu.
Dukda Hanne itama tana cikin damuwar rashin lafiyar Yusuf, amma ji take kamar ta make Widad, gaba É—aya ta hana mutane sukuni, se wani kuka take se kace wadda akace ya mutu.
Gwaggo ta zauna tasa Widad a gaba taci Abinci, amma ta gagara ci, Gwaggo tace "Amarya kiyi haƙuri, kici Abinci kinji, ki cigaba dayi masa Addu'a"
Cikin kuka Widad tace "Mama idan wani abu ya samu Yoseef sanadina ne, ba danni ba ba dan yasanni ba da duk baze shiga wannan halin ba"
Gwaggo tace "A'a kiyi haƙuri, Allah ne ya ɗora masa, kuma ze yaye masa"
Har dare basu dawo ba, ba Saleh ba dalilinsa, hankalin Widad ya sake tashi, yanzu take sake ganin Amfanin Yusuf a tare da ita, dare yayi tace bazata iya zama a ɗakin ita kaɗai ba, Gwaggo tace taje ɗakinta ta kwana, amma Widad fafur taƙi, ƙarshe Hindu ce tabi Widad ɗakinsu ta tayata kwana.
Har yanzu hankalin Umman Yusuf yaƙi kwanciya, rashin Yusuf a tare da ita ba ƙaramin abu bane a gurinta, sam rayuwa kawai take ba dan tana jin daɗin rayuwar ba, Yusuf shine ɗanta ɗaya tilo, yau a sanadin aikinsa yayi nesa da ita, bata san inda yake ba, gashi a hukumance babu wanda yace mata komai, se Suleiman da yake sintirin zuwa ganinta yana kwantar mata da hankali.
Wataran a ɗakin Yusuf ɗin take kwana, taita kuka gwanin ban tausayi, tana matuƙar ɗan nata rabuwarta da shi ji take kamar ta rasa komai na rayuwarta.
Bacci kam Widad ba tayi shi ba, Hindu tun tana rarrashin ta harta gaji tayi bacci, Widad kam kwana tayi tana Addu'a, Allah ya bawa Yusuf lafiya.
Se washegari sannan Ila da suka tafi kai Yusuf Asibiti tare yazo gidan, Widad na ganin shi a gigice tace "Ina Yoseef É—in? Yana ina?"
Ila yace "ki kwantar da hankalinki, kwantar dashi akai, can cikin garin Bauchi muka kai shi, ya ɗan samu sauƙi Amma yaji jiki fa, kafin muje har Suma ya dinga yi a mota, amma ya farfaɗo, baza'a sallameshi yau ba"
Hanne dake gefe tace "Alhamdilillah"
Gaba É—aya suka juya suna kallonta, banda Widad da tace "dan Allah dagaske kake ya tashi?"
Ila yace "kwarankwatsa dagaske nake, dan yace in gaidaki, Saleh na baro a gurinsa"
Se a lokacin Widad ta É—anji hankalin ta ya É—an kwanta, harta samu tayi wanka, megari ma yayi ta mata Nasiha akan wannan kukan data dingayi.
Ramla kam a kusan buge ta dawo gidan nan, Hajiya Halima bata ga dawowarta ba, Amal ce taga wucewarta kamar tana tangaÉ—i, binta tayi da sauri É—akinta, ta tarar tayi cilli da jakarta da takalmanta ta zube akan carfet tana bacci, Amal tace
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Ramla me zan gani haka, meya same ki?"
Ramla kasa magana tayi se É—aga hannu da take, cikin maye tace "ke.. Keee.. Nace ina ruwank.... Ki dani neeeee.. Ki fita nace"
"Ramla, shaye2 kika fara ne?"
Shiru Ramla tayi mata, ta cigaba da baccinta.
Gaba ɗaya hantar cikin Amal ya kaɗa, tabbas Ramla shaye2 take, dan maye take yi, ta tuna yadda take bacci ba ƙaƙƙautawa, da tayi kamar taje ta gayawa mahaifiyarsu, se kuma ta tuna dama a ƙule take da Fahad da mahaifinsa, muddin ta gayamata za'ayi ɓatacciya ne.
Kwanan Yusuf uku a Asibiti, gaba ɗaya Widad ta rame, idanunta duk sun kumbura, jama'ar ƙauyen duk sun san rashin lafiyar Yusuf, dan shike jansu Sallar Asuba da magariba zuwa isha'iyanzu, kuma ga karatu da yake koya musu suna jin daɗinsa.
Widad ta zuba ido, taga ta ina Za'a dawo mata da Yusuf, dan Ila ya gaya musu ranar za'a sallameshi.
Gwaggo tasa akayi Abinci, aka dama Fura saboda Yusuf.
Ila ya shigo gidan da Sallama yace "ku kintsa, mun dawo maƙota sun baibaye mota zasu shigo da shi"
Da ƙyar Gwaggo ta janye Widad zuwa ɗakinta, saboda maza zasu shigo, dukda damuwar da Widad ke ciki be hana Widad kallon Ɗakin Gwaggo ba, yasha jeren samiru da fanteku, ga gadonta na ƙarfe me rumfa da mudubi, ginin tsurar ƙasane ɗakin amma yayiwa Widad kyau nesa ba kusa ba, ga ƙwarya da'akayi wa itama nata jeren, ƙwaryar ta sha zane mekyau, ga wasu a cikin ragaya, Widad bata taɓa ganin irinsu ba"
Idan ba gizo kunnuwanta suka yi mata ba, to tabbas a cikin muryar mazan da suka yi Sallama hadda Yusuf.
Zumbur ta miƙe tsaye, Gwaggo tace "aikuwa ga muryar ɗana nan, Alhamdilillah lafiya ta samu"
Kasa jurewa Widad tayi, kawai se gani Gwaggo tayi Widad tayi waje, kai tsaye ta nufi ɗakinsu, ga mutane maza a ciki, wasu na ƙoƙarin fitowa, haka ta kutsa ta shiga, ta hango Yusuf yana zaune yana murmushi, sedai yayi rama sosai, yayi haske.
Da gudu ta ƙarasa ta rungume shi, ta kasa magana kawai ta fashe da kuka.
Ɗaya bayan ɗaya suka zame suka bar ɗakin, yau suka ga taɓara, ba kunya bakomai ba kara tazo ta rungume Yusuf a gabansu.
Suna fita Yusuf ya ha&a hannayensa ya rungumeta shima yace "Queen kin rame, duk kinyi wani iri"
Maimakon ta bashi amsa se sake kwanciya da tayi a jikinsa tace "Ya jiki ka warke?"
" Na warke amma ina ganin yadda kika rame naji zata dawo"
Murtalah yace "dama Hausawa sunce,' kada Allah ya kawo ranar yabo' duk rashin mutuncin da take Yusuf se yayi ta kare ta, se yanzu nake ganin gaskiyar zancensa da yace bata yiwa mutum wulaƙanci seya yi mata laifi"
Nura yace "Mhmm Ai kawai Allah yasaka mana, amma gidan nan ana abubuwa sedai fatan Allah ya kyauta"
Duk inda Hajiya Sarah tasan zata buga ta buga, amma anƙi sakin Anwar, gaba ɗaya ta rasa inda zata tsoma ranta, Anbi an toshe duk wata hanya da zata saka a samu belin Anwar.
Yanzu ma haka ta dawo fakan fakan kamar korarriya, a mugun guje ta shigo da mota gidan.
Tana shiga ta fara kiran "Ramlah! Ramlah! Ke Amal kuna inane?"
Amal ta fito tace "Mummy Ramlah fa bata nan"
"gidan ubanwa taje?"
Amal tace "sun fita ita da Fahad"
"zanci ubanta ita da Fahad ɗin kuwa, ai tunda ubansa ya watsa min ƙasa a ido, to tabbas zan masa rashin mutunci, zan nuna masa wacece Halima idan ya manta"
Amal tace "Mummy É—an uwan naki?"
"Eh shi É—in, tunda bani da kima a idon sa, nima zan nuna masa bashi da ita a nawa idon"
Amal tace "Mummy a bi dai komai a hankali, kar azo ayi aika aika"
Hajiya Halima tace "dalla rabu dani, ze gane ni ya taɓa, ai ɗa befi ɗa ba, yasani yaron nan besan inda aka kaai mutumin nan ba, amma se cemin yake wai in ƙyale doka tayi aikinta, na zagi dokar shi doka nawa yayi fatali da a rayuwar sa, zega tsiya"
Tai part É—inta tana cigaba da banbami, kamar wadda ke shirin Zarewa.
Saleh da Yusuf da É—an megari suka tafi kai Yusuf Asibiti, aka bar Widad da mutan gida tana ta faman yi musu kuka.
Gwaggo da Hindu ne suka iya zaman rarrashin Widad.
Hari tace wai ke Wudas daga miji na zazzaɓi seki zauna kita mana kuka, memakon ki masa Addu'a "
Ko kallon Hari ba tayi ba, ta miƙe ta tafi ɗakinsu tayi kwanciyarta tana cigaba da kuka.
Nurat suka dinga communicatinga da cousin É—inta akan yadda za'ayi belin Anwar.
Yanzu ma tana kwance akan gadonta hannunta É—auke da waya, tace" Brother ya ake ciki ne? Yakamata a gaggauta fitar da Anwar bashi da laifin komai fa"
"Nurat, kince bakyason asan muna ƙoƙarin belinsa, dan haka nake taka tsantsan, sedai abunda na gano shine tsare Anwar da akayi da manufa akayi shi, idan muka matsa tabbas za'a gano ke kikasa ayi belinamsa, tunda an san alaƙar dake tsakanin mu"
Cikin karaya Nurat tace "yanzu Brother babu abunda zaka iyayimin, Anwar be cancanci ya zauna a gurin nan ba"
Yace "Nurat, lawyan mahaifiyarsa ma yana ta ƙoƙari, amma har yanzu sun hana belinshi bansan meye abunyi ba, amma meyasa kika damu ya fita bayan kin san munin Alaƙar dake tsakanin mahaifinki da Daula?"
"Brother, idan akazo batun gaskiya da adalci ba'a kawo maganar alaƙa, an cutar da Anwar fiye da yadda kake zato, shikaɗai ne akan lamarin rashin lafiyar Alhaji Nasir, amma kalli abunda ya biyo baya, kodai an masa hakane dan a tozarta shi, ko kuma wanda ya sace shine yake son wanke kansa ta hanyar sawa a kama Anwar "
Barrister yace "Amma abun da mamaki ta yaya za'a iya sace mutum Attajiri kamar wannan a gadon Asibiti, kuma babu wani ƙwaƙwaran bayani, abun da mamaki fa"
Nurat tace "Brother, dan Allah idan kana da dama ina son kazo in ganka, ina son mu tattauna wani zance da kai dan Allah"
Barrister yace "Fara gayamin mana"
"A'a Brother, nidai so nake ina ganka, akwai magana ne a bakina"
"shikenan karki damu, Insha Allah idan ma samu lokaci zanzo insha Allah"
"Yawwa brother nagode sosai"
Ta kashe wayarta ta ajiye, shiru tayi abubuwa da dama suna damun zuciyarta, har yanzu bata ji alamar labarin inda su Yusuf suke ba, har yanzu bata sake jin wani magana game dasu ba, ta shiga tuna hirar da suka yi da Amal akan alaƙar Widad da Yusuf, ji tayi tana gumi dukda sanyin AC dake ɗakin nata, amma ta shiga haɗa gumi, miƙewa tayi ta tafi toilet da niyyar ta watsa ruwa ta rage damuwa.
Har bayan magariba babu labarin dawowar su Yusuf, nan fa Widad ta sake gigicewa, ta shiga sintir a gidan nan tana  "Allah ka duba Yoseef ka bashi lafiya, Allah ka bashi lafiya ba danni ba"
Gaba ɗaya tausayin ta ya hana Gwaggo nutsuwa, se aikin rarrashin Widad take, ita kuwa Hari harta ƙule saboda ganin abun na Widad take kama harda shagwaɓa dan taga ana lallaɓata, kawai dan mutum yana zazzaɓi ta cikawa mutane gida da ihu.
Dukda Hanne itama tana cikin damuwar rashin lafiyar Yusuf, amma ji take kamar ta make Widad, gaba É—aya ta hana mutane sukuni, se wani kuka take se kace wadda akace ya mutu.
Gwaggo ta zauna tasa Widad a gaba taci Abinci, amma ta gagara ci, Gwaggo tace "Amarya kiyi haƙuri, kici Abinci kinji, ki cigaba dayi masa Addu'a"
Cikin kuka Widad tace "Mama idan wani abu ya samu Yoseef sanadina ne, ba danni ba ba dan yasanni ba da duk baze shiga wannan halin ba"
Gwaggo tace "A'a kiyi haƙuri, Allah ne ya ɗora masa, kuma ze yaye masa"
Har dare basu dawo ba, ba Saleh ba dalilinsa, hankalin Widad ya sake tashi, yanzu take sake ganin Amfanin Yusuf a tare da ita, dare yayi tace bazata iya zama a ɗakin ita kaɗai ba, Gwaggo tace taje ɗakinta ta kwana, amma Widad fafur taƙi, ƙarshe Hindu ce tabi Widad ɗakinsu ta tayata kwana.
Har yanzu hankalin Umman Yusuf yaƙi kwanciya, rashin Yusuf a tare da ita ba ƙaramin abu bane a gurinta, sam rayuwa kawai take ba dan tana jin daɗin rayuwar ba, Yusuf shine ɗanta ɗaya tilo, yau a sanadin aikinsa yayi nesa da ita, bata san inda yake ba, gashi a hukumance babu wanda yace mata komai, se Suleiman da yake sintirin zuwa ganinta yana kwantar mata da hankali.
Wataran a ɗakin Yusuf ɗin take kwana, taita kuka gwanin ban tausayi, tana matuƙar ɗan nata rabuwarta da shi ji take kamar ta rasa komai na rayuwarta.
Bacci kam Widad ba tayi shi ba, Hindu tun tana rarrashin ta harta gaji tayi bacci, Widad kam kwana tayi tana Addu'a, Allah ya bawa Yusuf lafiya.
Se washegari sannan Ila da suka tafi kai Yusuf Asibiti tare yazo gidan, Widad na ganin shi a gigice tace "Ina Yoseef É—in? Yana ina?"
Ila yace "ki kwantar da hankalinki, kwantar dashi akai, can cikin garin Bauchi muka kai shi, ya ɗan samu sauƙi Amma yaji jiki fa, kafin muje har Suma ya dinga yi a mota, amma ya farfaɗo, baza'a sallameshi yau ba"
Hanne dake gefe tace "Alhamdilillah"
Gaba É—aya suka juya suna kallonta, banda Widad da tace "dan Allah dagaske kake ya tashi?"
Ila yace "kwarankwatsa dagaske nake, dan yace in gaidaki, Saleh na baro a gurinsa"
Se a lokacin Widad ta É—anji hankalin ta ya É—an kwanta, harta samu tayi wanka, megari ma yayi ta mata Nasiha akan wannan kukan data dingayi.
Ramla kam a kusan buge ta dawo gidan nan, Hajiya Halima bata ga dawowarta ba, Amal ce taga wucewarta kamar tana tangaÉ—i, binta tayi da sauri É—akinta, ta tarar tayi cilli da jakarta da takalmanta ta zube akan carfet tana bacci, Amal tace
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Ramla me zan gani haka, meya same ki?"
Ramla kasa magana tayi se É—aga hannu da take, cikin maye tace "ke.. Keee.. Nace ina ruwank.... Ki dani neeeee.. Ki fita nace"
"Ramla, shaye2 kika fara ne?"
Shiru Ramla tayi mata, ta cigaba da baccinta.
Gaba ɗaya hantar cikin Amal ya kaɗa, tabbas Ramla shaye2 take, dan maye take yi, ta tuna yadda take bacci ba ƙaƙƙautawa, da tayi kamar taje ta gayawa mahaifiyarsu, se kuma ta tuna dama a ƙule take da Fahad da mahaifinsa, muddin ta gayamata za'ayi ɓatacciya ne.
Kwanan Yusuf uku a Asibiti, gaba ɗaya Widad ta rame, idanunta duk sun kumbura, jama'ar ƙauyen duk sun san rashin lafiyar Yusuf, dan shike jansu Sallar Asuba da magariba zuwa isha'iyanzu, kuma ga karatu da yake koya musu suna jin daɗinsa.
Widad ta zuba ido, taga ta ina Za'a dawo mata da Yusuf, dan Ila ya gaya musu ranar za'a sallameshi.
Gwaggo tasa akayi Abinci, aka dama Fura saboda Yusuf.
Ila ya shigo gidan da Sallama yace "ku kintsa, mun dawo maƙota sun baibaye mota zasu shigo da shi"
Da ƙyar Gwaggo ta janye Widad zuwa ɗakinta, saboda maza zasu shigo, dukda damuwar da Widad ke ciki be hana Widad kallon Ɗakin Gwaggo ba, yasha jeren samiru da fanteku, ga gadonta na ƙarfe me rumfa da mudubi, ginin tsurar ƙasane ɗakin amma yayiwa Widad kyau nesa ba kusa ba, ga ƙwarya da'akayi wa itama nata jeren, ƙwaryar ta sha zane mekyau, ga wasu a cikin ragaya, Widad bata taɓa ganin irinsu ba"
Idan ba gizo kunnuwanta suka yi mata ba, to tabbas a cikin muryar mazan da suka yi Sallama hadda Yusuf.
Zumbur ta miƙe tsaye, Gwaggo tace "aikuwa ga muryar ɗana nan, Alhamdilillah lafiya ta samu"
Kasa jurewa Widad tayi, kawai se gani Gwaggo tayi Widad tayi waje, kai tsaye ta nufi ɗakinsu, ga mutane maza a ciki, wasu na ƙoƙarin fitowa, haka ta kutsa ta shiga, ta hango Yusuf yana zaune yana murmushi, sedai yayi rama sosai, yayi haske.
Da gudu ta ƙarasa ta rungume shi, ta kasa magana kawai ta fashe da kuka.
Ɗaya bayan ɗaya suka zame suka bar ɗakin, yau suka ga taɓara, ba kunya bakomai ba kara tazo ta rungume Yusuf a gabansu.
Suna fita Yusuf ya ha&a hannayensa ya rungumeta shima yace "Queen kin rame, duk kinyi wani iri"
Maimakon ta bashi amsa se sake kwanciya da tayi a jikinsa tace "Ya jiki ka warke?"
" Na warke amma ina ganin yadda kika rame naji zata dawo"