Sashe 65
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yusuf yace "gani nayi kina tsaye kina murmushi, shiyasa nace bari inga abunda ya saki nishaɗi haka? Sannan gari akwai sanyi fa, kalli kanki babu ɗan kwali kar mura ta kamaki, sannan kayan jikinki maza na shiga na fita a gidan nan, kar gari yayi haske suzo su sameki a haka, su kansu matan gidan zasu ga hakan wani iri saboda ya saɓawa Al'adunsu"
"Wai kai meyasa ka fiye shishshigi da takura ne?"
"ba shishshigi da takura bane, kinga yanzu kina da Aure fa"
"kaga wannan Auren fa dashi da babu duk ɗaya, karka ƙara sawa ranka wani Aure mukayi"
Yusuf ya ɗanyi murmushi, cike da basar da zancen yace  "kin tsorata nifa, harna kwanta na duba ban ganki ba, shiru shiru kuma naga baki shigo ɗaki ba"
"hmm kayi zaton zan gudune? In gudu inje ina? Ko kana zaton zan gudu da wannan Auren naka a kaina? Idan kaga na gudu ko na bar ƙauyen nan to tabbas ka sakeni ne"
Yusuf yace "idan kuma ban sake kin bafa?"
Juyowa tayi ta saka idonta a nasa tace "me kace?"
Girgiza mata kai yayi alamar bakomai, ta harareshi tace "ban guri in wuce"
Seda ta tafi ya Leƙa me take kallo, ɗakin zomaye ne, an kunna musu aci balbal an rataye ta, se guje guje suke suna haƙa ƙasa, da wasanninsu shine abunda yasa ta nishaɗi ta tsaya take kallonsu.
Yusuf ya koma ya kwanta bacci ya É—auke shi, ita kuwa Widad data gama brush É—in komawa tayi ta cigaba da kallon zomaye, seda ta gaji sannan ta koma É—aki.
Yusuf yayi juyi ya buɗe idonsa a hankali, ya sauke su akan Widad, ta gyara shimfiɗarta sa kanta, ta sauke Akwatunanta tana ta gyara kayan ciki, ta ware masu datti ta tattare Akwatunan ta canza musu guri, duk Yusuf yana kallonta, Widas sam bata son ƙazanta, tana da matuƙar son tsafta a rayuwarta.
Yusuf ya tashi ya kwashe kayan shimfiÉ—arasa ya ninke, bata kula shi ba sabgoginta kawai take, Yusuf yayi mamakin danganar da Widad tayi, dukda har yanzu bata saba da abubuwa da yawa ba.
"wai babu inda za'a samu inji wanki ne? Ina son a wanke min wannan kayan ne"
Yusuf yace "Ai baki da wani injin wankin daya wuceni, in kin haÉ—a se in É—iba inje in wanko su"
Widad tace "kaine zaka wankemin kayan?"
Yusuf yace "eh mana, ko kinga alamar injin wanki a garin nan, tunda muka zo kin taɓa ganin wuta?"
"to gasu nan na haÉ—a, kaje kace a bani ruwan wanka"
Yusuf ya girgiza kai yace "to"
Ya miƙe ya ɗau bokiti ya fita, Widad ta buɗe Akwatinta ta ɗakko towel ta ɗaura, ta saka hijjabi ta biyo bayansa yadda ana haɗa ruwan se ta shiga tayi wanka.
Mutan gidan sunata hada Hadar yadda za'a haÉ—a karin kumallo, ga dukkan alamu yau mutuniyar Widas ce da girki, wato Harira.
Yusuf ya durƙusa ya gaishesu, cikin jin nauyi kafin yayi magana Gwaggo tace "Yusufa na ganka da bokiti, ruwan wankan za'a zuba mata?"
Yusuf yace "eh Mama"
Tace "kawo in zuba maka anan, ya jikin nata kuwa"
Yusuf yace "jiki Alhamdilillah"
Tace "Madalla, nikam ya sunan nata ne? Bamu san sunanta ba"
Yusuf yayi murmushi yace "Sunanta Widad"
Hari dake gaban murhu ta juyo da sauri taceÂ
"Bala'i, wannan wane irin sunane? Hudas ko wudas sekace kayan citta da masoro wane irin sunane wannan"
Tsakin Widad ne yasa Yusuf juyawa, yadda ta tamke fuskane ya tabattar maaa sa taji abunda Hari tace, Yusuf kamar yayi dariya Amma ya basar kar suyi faÉ—a a gaban mutane.
Gwaggo tace "kaga 'yar halak, ana zancenta se gata, sedai ni wannan sunan nata na Larabawa bazan iya faÉ—a ba, Amarya ya jikin naki?"
Widad a ranta tace "wai Amarya Taɓɗijan"
Yusuf yace "Ana miki ya jiki?"
"Naji sauƙi"
Galala Hari ta bita da kallo tace "Ashe bahaushiya ce, wallahi ganinta nake kamar bata jin hausa, yo aini harna fara tunanin ko kurma ce, ashe tana magana sannu Amarya wudas, ashe kina magana Allah sarki, ya jiki?"
Sake yamutsa fuska Widad tayi, 'ita dai wannan matar bata gajiya da magana, kodai bata san yadda haƙoranta suke bane take buɗesu tana surutu haka, bar wani kore kore ne a jikinsu, ga maganar tsiya da take dashi"
Widad bata kulata ba, aka haÉ—a mata ruwanta, Yusuf ya kaimata inda take wanka.
Aka haÉ—a Yusuf da yaro ya rakashi rafin da matasan garin suke haÉ—uwa suyi wanki.
Amlace ta shiga ɗakin Ramlah, ta dinga bubbuga mata filo, da ƙyar Ramlah ta tashi a fusace tace "Meye haka Amal?"
Amal tace "Anya lafiyar ki kuwa? Ƙarfe biyi fa, amma har yanzu bacci kike, yakamata ki tashi haka ai"
Miƙewa tayi zaune tana miƙa tare da duba agogo, dagaske biyu na rana, haka ta miƙe ta tafi banɗaki tayi wanka sannan ta ɗanji ƙarfin jikinta.
Koda Saleh ya dawo kano, be biya ko'ima ba Asibiti ya fara zuwa duba jikin Alhaji Nasir, amma yanayin jikin nasa se godiyar Allah, Nurses suka gaya masa Anwar yaje masallaci.
Saleh ya zauna a kusa da Alhaji Nasir, wanda idanunsa ke lumshe yake numfashi da temakon Na'urar dakw bashi iskar Oxygen, ya riƙo hannunsa da suka yi sanyi ƙalau, cike da tausayawa ya kai bakinsa daidai kunnensa yace
"Allah ya baka lafiya Yallaɓai, 'ya' yanka sun kuɓuta daga hannun miyagun nan, yanzu haka suna wasu ƙauye na basu mafaka, saboda tseratar da Rayuwarsu, Yusuf yayi ƙoƙari matuƙa ya kula da Amanarka, yana kula da gimbiyarka sosai, Amma munyi maka wani laifi da ban san ya zaka ɗauki abunba, Na wuce gaba Yusuf ya Auri 'yarka, dan kasan bata yadda da kowa seshi, kuma baze yuwu ya cigaba da kula da ita ba, tunda ba muharramarsa bace"
Dukda Alhaji Nasir ba iya magana zeba, da alama yana jin abunda Saleh yake faɗa, ƙara riƙe hannun Saleh yayi gam sannan yayi masa murmushi.
Saleh yace "Amma karka kuskura ka gayawa kowa, kayi shiru da bakinka"
Anwar ne ya shigo bakinsa É—auke da Sallama, yana ganin Saleh yayi murmushi yace "Saleh sannu da zuwa, naje Sallane"
Saleh yace "bakomai Anwar, ya me jiki?"
Shiru Anwar yayi, Æ™walla na taruwa a idonsa yaceÂ
"Saleh na rasa wane irin abokai Allah ya bawa bawan Allah nan, sam hankalinsu baya kansa, amma lokacin da yake da lafiya sune kan gaba gurin nuna masa ƙauna, Amma dubi yanzu, look at how he's suffering alone, ba wanda ya bani mamaki kamar mahaifiyata"
Anwar ya ƙarasa maganar, jijiyoyin kansa na tashi idonsa yayi ja, Alhaji Nasir ne yayiwa Anwar Alamar yaje da hannunsa.
Anwar ya ƙarasa gaban gadon Alhaji Nasir ya zauna.
Alhaji Nasir ya kamo hannun Anwar, sannan ya miƙa hannunsa ɗaya yana shafa kan Anwar tareda yi masa murmushi a hankali yace "Nagode, Nagode"
Kawai Anwar ya rungume Daula ya fashe da kuka, shima Daula hawayene suka fara bin gefen idonsa, da ba ƙaramin mamaki ya shiga ba, ganin yadda gaba ɗaya mutanensa da suke tare dashi suka watse suka barshi, ciki harda matarsa da take morarsa.
Yusuf yaje ya tarar da matasa da magidanta a gurin wankin nan, wasu na wanki wasu na wanka a ruwan, in an koro dabbobi suma suzo su sha ruwan, amma a haka yaga wasu na É—iba na tafiya dashi abun ya bashi mamaki, dama a gurin salla megari ya gabatar dashi, dan haka wasu daga cikinsu sun sanshi.
Duk rashin son mutane irin na Yusuf ya É—an sake dasu, suka dinga hira suma bashi labari akan yanayin garin nasu.
Abun ya dinga bawa Yusuf mamaki, suna rayuwa cike da son juna mutanen ƙauyen, sedai abun mamaki ɗan majaillisar dake wakiltar yankin kakannisa 'yan garinne, amma abun mamaki sukace lokacin da yake campaign har falafalan wuta aka samu su, ya gina musu borehole guda ɗaya can wajen gidan kakaninsa shima se anyi tafiya me nisan gaske borehole ɗin yake, yace idan suka zaɓe shi yaci ze janyo musu wutar lantarki, tundaga wannan campaign da yazo tsawon shekara uku basu sake ganinsa ba, ko gidan kakannin nasa baya zuwa ziyara gaba ɗaya ya koma Abuja.
Haka Yusuf suka cigaba da hira shikuma yana wankinsa, seda ya gama suka bushe ya ninko kayan tsaf, sannan suka taho sa wani maƙocin gidan megari zuwa gida.
Yana zuwa gida ya tarar da Widad a ƙofar ɗakinsu a zaune, zaman dirshen a ƙasa fuskarta tayi jawur saboda kuka, Yusuf ya razana ko ciwonta ne ya tashi.
Gwaggo na ganinsa tace "yawwa Yusufa, wallahi muna tsakar gida muna aiki muka jiyo ihunta, ta fito da gudu mukaje kanta, juyin duniya taƙi magana tayi zamanta a nan gurin, munce ta bar ranar ta shiga ko ɗakina ta zauna taƙi.
Yusuf ya ƙarasa inda take ya ajiye bokitin hannunsa me ɗauke da ninkakkun kayansu yace "lafiya kuwa? Meyasameki haka?"
Cikin harshen turanci tace masa, "wasu ƙwarine suka yi ta cizona, sekuma naga spider manya guda biyu a ɗakin, dana fito nan ma ƙwarin suka cigaba da cizona"
Girgiza kai yayi yace "shikenan tunda na dawo tashi mu shiga É—aki, kalli a yadda kike kin zauna a tsakar gida kowa yana kallonki a haka, kuma kinga kin tayarwa da mutanen gidan hankali"
"wallahi bazan shiga ba se an cire wannan spider ni bana sonshi, bana son ganinsa it's irritating me, looks at my body"
Se yanzu ya lura da yadda kafofin gashinta suka buÉ—e, jikinta yayi wani irin burÉ—in_ burÉ—in, fuskarta ma tayi ja saboda cizon sauro.
Hari tace "Allah dai yasa ba wani abun mukayi mata ba, dan naga alamar makirace, tun ɗazu muke fama taƙi magana, Amma tana ganin mijinta ta fara magana hadda karairaya"
Widad ta ɗaga kai ta ƙurawa Hari ido, yayin da gwaggo taji haushin abunda Harin tayi.
Yusuf kam ba ƙaramin dariya Hari ke bashi ba idan ta kunna Widad, yasan Widad tana mata kawaici ne kafin ta ɗan sake.
Yace "ba wani abun kukayi mata ba, wai wani abune ya cijeta amma, bakomai yanzu zan shiga in duba"
Yusuf ya shiga ya duba bega gizo2 ba, sedai cinnaku dake yawo a É—akin, da alama su suka cijeta.
Yasa tsintsiya ya shashsharesu tsaf, sannan yace ta dawo É—akin.
Yusuf "Yace meye ya cijekin?"
"Wai kai meyasa ka fiye shishshigi da takura ne?"
"ba shishshigi da takura bane, kinga yanzu kina da Aure fa"
"kaga wannan Auren fa dashi da babu duk ɗaya, karka ƙara sawa ranka wani Aure mukayi"
Yusuf ya ɗanyi murmushi, cike da basar da zancen yace  "kin tsorata nifa, harna kwanta na duba ban ganki ba, shiru shiru kuma naga baki shigo ɗaki ba"
"hmm kayi zaton zan gudune? In gudu inje ina? Ko kana zaton zan gudu da wannan Auren naka a kaina? Idan kaga na gudu ko na bar ƙauyen nan to tabbas ka sakeni ne"
Yusuf yace "idan kuma ban sake kin bafa?"
Juyowa tayi ta saka idonta a nasa tace "me kace?"
Girgiza mata kai yayi alamar bakomai, ta harareshi tace "ban guri in wuce"
Seda ta tafi ya Leƙa me take kallo, ɗakin zomaye ne, an kunna musu aci balbal an rataye ta, se guje guje suke suna haƙa ƙasa, da wasanninsu shine abunda yasa ta nishaɗi ta tsaya take kallonsu.
Yusuf ya koma ya kwanta bacci ya É—auke shi, ita kuwa Widad data gama brush É—in komawa tayi ta cigaba da kallon zomaye, seda ta gaji sannan ta koma É—aki.
Yusuf yayi juyi ya buɗe idonsa a hankali, ya sauke su akan Widad, ta gyara shimfiɗarta sa kanta, ta sauke Akwatunanta tana ta gyara kayan ciki, ta ware masu datti ta tattare Akwatunan ta canza musu guri, duk Yusuf yana kallonta, Widas sam bata son ƙazanta, tana da matuƙar son tsafta a rayuwarta.
Yusuf ya tashi ya kwashe kayan shimfiÉ—arasa ya ninke, bata kula shi ba sabgoginta kawai take, Yusuf yayi mamakin danganar da Widad tayi, dukda har yanzu bata saba da abubuwa da yawa ba.
"wai babu inda za'a samu inji wanki ne? Ina son a wanke min wannan kayan ne"
Yusuf yace "Ai baki da wani injin wankin daya wuceni, in kin haÉ—a se in É—iba inje in wanko su"
Widad tace "kaine zaka wankemin kayan?"
Yusuf yace "eh mana, ko kinga alamar injin wanki a garin nan, tunda muka zo kin taɓa ganin wuta?"
"to gasu nan na haÉ—a, kaje kace a bani ruwan wanka"
Yusuf ya girgiza kai yace "to"
Ya miƙe ya ɗau bokiti ya fita, Widad ta buɗe Akwatinta ta ɗakko towel ta ɗaura, ta saka hijjabi ta biyo bayansa yadda ana haɗa ruwan se ta shiga tayi wanka.
Mutan gidan sunata hada Hadar yadda za'a haÉ—a karin kumallo, ga dukkan alamu yau mutuniyar Widas ce da girki, wato Harira.
Yusuf ya durƙusa ya gaishesu, cikin jin nauyi kafin yayi magana Gwaggo tace "Yusufa na ganka da bokiti, ruwan wankan za'a zuba mata?"
Yusuf yace "eh Mama"
Tace "kawo in zuba maka anan, ya jikin nata kuwa"
Yusuf yace "jiki Alhamdilillah"
Tace "Madalla, nikam ya sunan nata ne? Bamu san sunanta ba"
Yusuf yayi murmushi yace "Sunanta Widad"
Hari dake gaban murhu ta juyo da sauri taceÂ
"Bala'i, wannan wane irin sunane? Hudas ko wudas sekace kayan citta da masoro wane irin sunane wannan"
Tsakin Widad ne yasa Yusuf juyawa, yadda ta tamke fuskane ya tabattar maaa sa taji abunda Hari tace, Yusuf kamar yayi dariya Amma ya basar kar suyi faÉ—a a gaban mutane.
Gwaggo tace "kaga 'yar halak, ana zancenta se gata, sedai ni wannan sunan nata na Larabawa bazan iya faÉ—a ba, Amarya ya jikin naki?"
Widad a ranta tace "wai Amarya Taɓɗijan"
Yusuf yace "Ana miki ya jiki?"
"Naji sauƙi"
Galala Hari ta bita da kallo tace "Ashe bahaushiya ce, wallahi ganinta nake kamar bata jin hausa, yo aini harna fara tunanin ko kurma ce, ashe tana magana sannu Amarya wudas, ashe kina magana Allah sarki, ya jiki?"
Sake yamutsa fuska Widad tayi, 'ita dai wannan matar bata gajiya da magana, kodai bata san yadda haƙoranta suke bane take buɗesu tana surutu haka, bar wani kore kore ne a jikinsu, ga maganar tsiya da take dashi"
Widad bata kulata ba, aka haÉ—a mata ruwanta, Yusuf ya kaimata inda take wanka.
Aka haÉ—a Yusuf da yaro ya rakashi rafin da matasan garin suke haÉ—uwa suyi wanki.
Amlace ta shiga ɗakin Ramlah, ta dinga bubbuga mata filo, da ƙyar Ramlah ta tashi a fusace tace "Meye haka Amal?"
Amal tace "Anya lafiyar ki kuwa? Ƙarfe biyi fa, amma har yanzu bacci kike, yakamata ki tashi haka ai"
Miƙewa tayi zaune tana miƙa tare da duba agogo, dagaske biyu na rana, haka ta miƙe ta tafi banɗaki tayi wanka sannan ta ɗanji ƙarfin jikinta.
Koda Saleh ya dawo kano, be biya ko'ima ba Asibiti ya fara zuwa duba jikin Alhaji Nasir, amma yanayin jikin nasa se godiyar Allah, Nurses suka gaya masa Anwar yaje masallaci.
Saleh ya zauna a kusa da Alhaji Nasir, wanda idanunsa ke lumshe yake numfashi da temakon Na'urar dakw bashi iskar Oxygen, ya riƙo hannunsa da suka yi sanyi ƙalau, cike da tausayawa ya kai bakinsa daidai kunnensa yace
"Allah ya baka lafiya Yallaɓai, 'ya' yanka sun kuɓuta daga hannun miyagun nan, yanzu haka suna wasu ƙauye na basu mafaka, saboda tseratar da Rayuwarsu, Yusuf yayi ƙoƙari matuƙa ya kula da Amanarka, yana kula da gimbiyarka sosai, Amma munyi maka wani laifi da ban san ya zaka ɗauki abunba, Na wuce gaba Yusuf ya Auri 'yarka, dan kasan bata yadda da kowa seshi, kuma baze yuwu ya cigaba da kula da ita ba, tunda ba muharramarsa bace"
Dukda Alhaji Nasir ba iya magana zeba, da alama yana jin abunda Saleh yake faɗa, ƙara riƙe hannun Saleh yayi gam sannan yayi masa murmushi.
Saleh yace "Amma karka kuskura ka gayawa kowa, kayi shiru da bakinka"
Anwar ne ya shigo bakinsa É—auke da Sallama, yana ganin Saleh yayi murmushi yace "Saleh sannu da zuwa, naje Sallane"
Saleh yace "bakomai Anwar, ya me jiki?"
Shiru Anwar yayi, Æ™walla na taruwa a idonsa yaceÂ
"Saleh na rasa wane irin abokai Allah ya bawa bawan Allah nan, sam hankalinsu baya kansa, amma lokacin da yake da lafiya sune kan gaba gurin nuna masa ƙauna, Amma dubi yanzu, look at how he's suffering alone, ba wanda ya bani mamaki kamar mahaifiyata"
Anwar ya ƙarasa maganar, jijiyoyin kansa na tashi idonsa yayi ja, Alhaji Nasir ne yayiwa Anwar Alamar yaje da hannunsa.
Anwar ya ƙarasa gaban gadon Alhaji Nasir ya zauna.
Alhaji Nasir ya kamo hannun Anwar, sannan ya miƙa hannunsa ɗaya yana shafa kan Anwar tareda yi masa murmushi a hankali yace "Nagode, Nagode"
Kawai Anwar ya rungume Daula ya fashe da kuka, shima Daula hawayene suka fara bin gefen idonsa, da ba ƙaramin mamaki ya shiga ba, ganin yadda gaba ɗaya mutanensa da suke tare dashi suka watse suka barshi, ciki harda matarsa da take morarsa.
Yusuf yaje ya tarar da matasa da magidanta a gurin wankin nan, wasu na wanki wasu na wanka a ruwan, in an koro dabbobi suma suzo su sha ruwan, amma a haka yaga wasu na É—iba na tafiya dashi abun ya bashi mamaki, dama a gurin salla megari ya gabatar dashi, dan haka wasu daga cikinsu sun sanshi.
Duk rashin son mutane irin na Yusuf ya É—an sake dasu, suka dinga hira suma bashi labari akan yanayin garin nasu.
Abun ya dinga bawa Yusuf mamaki, suna rayuwa cike da son juna mutanen ƙauyen, sedai abun mamaki ɗan majaillisar dake wakiltar yankin kakannisa 'yan garinne, amma abun mamaki sukace lokacin da yake campaign har falafalan wuta aka samu su, ya gina musu borehole guda ɗaya can wajen gidan kakaninsa shima se anyi tafiya me nisan gaske borehole ɗin yake, yace idan suka zaɓe shi yaci ze janyo musu wutar lantarki, tundaga wannan campaign da yazo tsawon shekara uku basu sake ganinsa ba, ko gidan kakannin nasa baya zuwa ziyara gaba ɗaya ya koma Abuja.
Haka Yusuf suka cigaba da hira shikuma yana wankinsa, seda ya gama suka bushe ya ninko kayan tsaf, sannan suka taho sa wani maƙocin gidan megari zuwa gida.
Yana zuwa gida ya tarar da Widad a ƙofar ɗakinsu a zaune, zaman dirshen a ƙasa fuskarta tayi jawur saboda kuka, Yusuf ya razana ko ciwonta ne ya tashi.
Gwaggo na ganinsa tace "yawwa Yusufa, wallahi muna tsakar gida muna aiki muka jiyo ihunta, ta fito da gudu mukaje kanta, juyin duniya taƙi magana tayi zamanta a nan gurin, munce ta bar ranar ta shiga ko ɗakina ta zauna taƙi.
Yusuf ya ƙarasa inda take ya ajiye bokitin hannunsa me ɗauke da ninkakkun kayansu yace "lafiya kuwa? Meyasameki haka?"
Cikin harshen turanci tace masa, "wasu ƙwarine suka yi ta cizona, sekuma naga spider manya guda biyu a ɗakin, dana fito nan ma ƙwarin suka cigaba da cizona"
Girgiza kai yayi yace "shikenan tunda na dawo tashi mu shiga É—aki, kalli a yadda kike kin zauna a tsakar gida kowa yana kallonki a haka, kuma kinga kin tayarwa da mutanen gidan hankali"
"wallahi bazan shiga ba se an cire wannan spider ni bana sonshi, bana son ganinsa it's irritating me, looks at my body"
Se yanzu ya lura da yadda kafofin gashinta suka buÉ—e, jikinta yayi wani irin burÉ—in_ burÉ—in, fuskarta ma tayi ja saboda cizon sauro.
Hari tace "Allah dai yasa ba wani abun mukayi mata ba, dan naga alamar makirace, tun ɗazu muke fama taƙi magana, Amma tana ganin mijinta ta fara magana hadda karairaya"
Widad ta ɗaga kai ta ƙurawa Hari ido, yayin da gwaggo taji haushin abunda Harin tayi.
Yusuf kam ba ƙaramin dariya Hari ke bashi ba idan ta kunna Widad, yasan Widad tana mata kawaici ne kafin ta ɗan sake.
Yace "ba wani abun kukayi mata ba, wai wani abune ya cijeta amma, bakomai yanzu zan shiga in duba"
Yusuf ya shiga ya duba bega gizo2 ba, sedai cinnaku dake yawo a É—akin, da alama su suka cijeta.
Yasa tsintsiya ya shashsharesu tsaf, sannan yace ta dawo É—akin.
Yusuf "Yace meye ya cijekin?"