← Book details Akidata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 82

Sashe 58

Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saleh yace "Aifa kedai halinki yana nan bazaki canza ba" yayi gaba abunsa, ya tafi gurin me gari suka sake tattaunawa sannan ya tafi.

Haka Saleh ya tafi ya bar su Yusuf a cikin wannan ƙasurgumin ƙauye.

A hankali Widad tayi juyi, ta ƙarewa ɗakin da take ciki kallo, wai anan zata zauna ita da suka zo sam bata zaci wai nan mutane ne ke rayuwa a cikin gurin ba se yanzu.

Yusuf yaje yayo Alwala, yazo ya tada salla sedai duk inda yayi se mutanen gidan su bishi da kallo.

Widad ta cire hijjabin jikinta, jikinta se faman ƙaiƙayi yake mata, Yusuf ya idar da salla zeyi magana ta riga shi ta hanyar cewa "zanyi wanka"

ÆŠan zare ido yayi yace "to shikenan, bari inwa mutan gidan magana"

Ya fito tsakar gidan, yaga wadda Saleh ya kira da Gwaggo ɗazu tana ta aiki a tsakar gida, yace mata  "dan Allah Mama ko zamu samu ruwan ɗumi, mara lafiyar zata yi wanka, nikuma ko na sanyi ne na samu se inyi Amfani da shi"

Tayi murmushi tace  "bakomai, na zuba ruwan tuwon dare dama, bari in ɗibar maka"

Yusuf yace  "to nagode"

Ya tafi ɗakin su, ya ɗakko sabon bokiti, aka zuba ruwa aka sirka Yusuf ya koma ɗakin yace  "An haɗa ruwan"

Ta tashi zaune ta fara kiciniyar cire rigar jikinta, sedai hannunta na hagu shine wanda aka harbeta, na dama kuma yana ciwo saboda duka da wahalar mota.

Yusuf ya juya mata baya da nufin ta kintsa ya kaita banÉ—akin.

"Zoka tayani cire wannan rigar na kasa cirewa....

(Akwa ƙura fa🚶 🚶 🚶 🚶 🚶)

Share, share and share please 🙏

Domin, gyara sharhi ko shawara
Ayshercool
07063065680

     _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 28_29

Gaba ɗaya dirircewa Yusuf yayi, se yayi kamar beji me tace ba, ganin yaƙi magana yasa itama tai shiru ta nemi guri ta kashingiɗa.

Yusuf ya waigo yace  "Kin gama kintsawar ne?"

Kawai ya ganta a zaune.

"Ya haka kuma? Se ruwan ya huce?"

"Ban sani ba, ai kana jina ina magana kayi min shiru, nace kazo ka tayani in cire rigar nan, amma kayi kamar baka jiba"

Ikon Allah bata da lafiyar ma, an tsira da ƙyar bakinta be mutu ba, gashi da ƙyar take maganar.

Yusuf yace  "bari inyiwa mutanen gidan magana, se suzo su cire miki"

"Wallahi babu matar da zata taɓani" tai maganar tana kuka

Seda Yusuf yayi shiru, sannan ya tako a hankali kan katifar da take, ya zagaya bayanta hannunsa rawa yake ya zuge zip ɗin doguwar rigar tata ƙasa.

Farar fatarta ta bayyana cikin wata baƙar vest, shiru yayi yana kallonta, ta janyo hijjabi ta mayar ta yunƙura zata miƙe tsaye amma jiri ya kwashe ta.

Yusuf yace  "ki dena gaggawa, a halin da kike ciki ɗin nan, idan kika faɗi zaki ji ciwo fa"

Ya duba ya ɗakko soson wankanta dake cikin Akwatinta, sedai babu sabulu haka ya riƙota suka fito, Gwaggo na ganin haka ta taho da sauri da nufin ta taya Yusuf, Amma Widad ta maƙale hannunta, ta manne a jikin Yusuf tabi gwaggo da ido, gwaggo ta tsaya sororo tana kallonsu.

Yusuf yace "Mama karki damu, kiyi haƙuri haka halinta yake bata da yadda ne"

Matar dake gaban murhu ta juyo ta kallesu tace "yau nake ganin ikon Allah, wannan gwandamemiyar matar ce take ƙyuya se kace me shan Nono, taɓ amma lamari ya ɓaci, koda yake wannan kamar ma ba irin tamuce ta nan ƙasar ba"

Widad tabi matar gaban murhun da kallo, haƙoranta yellow shar ga haƙorannata wasu sunyi goyon kura, gata baƙa sosai ga fuskarta duk tsagu, gashi se ƙara baje hanci take.

Gwaggo tace "Haba Hari, ina ruwanki da ita irinku ne ke sawa adinga cewa Hausawa basu da kirki, yanzu da taji abunda kike faÉ—a ba"

Zatonsu duk Widad bata jin hausa, gwaggo ta kalli Yusuf tace "ga banÉ—akin can seka kaita"

Suna zuwa ƙofar banɗakin Widad tayi tiris taƙi gaba taƙi baya.
Yusuf yace "muje mana seki shiga kiyi wankan"

Girgiza masa kai tayi tace  "Ni wallahi tsoro nake ji bazan iya shiga ba" sam Widad gurin be mata kama da banɗaki ba, kamar wani gidan horo haka taga gurin.

"meye abun tsoron, zan jiraki anan gurin kiyi ki fito"

Riƙe shi tayi tsam tana girgiza kai tace  "Ni na fasa wankan, bazan shiga nan ba"

Gwaggo tace  "ɗan nan ya naga bata shiga ba, lafiya kuwa?"

Yusuf yace  "wai tsoro take ji ba zata iya shiga ba"

Gwaggo tace  "Allah sarki, ƙasashenku babu irin wannan banɗakin ko? Abun duk se haƙuri ai, akwai wani ɗaki da babu komai a ciki ta shiga tayi a ciki kawai"

Yusuf yace "mungode Mama"

"A'a bakomai"

Ta nuna musu ɗakin, duk yadda Yusuf ya tsani roƙo, haka ya karya billensa ya tambayi sabulun wanka, sedai Sabulun da suke wanka da shi irin sabulun nan ne kore na wanki me ƙarnin tsiya, Yusuf ya miƙawa Widad, tasa hannu ta karɓi sabulun ta kalli Yusuf kawai yaga Hawaye a idonta.

Tausayinta ya kama shi, amma ya basar kamar bega hawayen idonta ba, haka ta shiga ɗakin da siminti a ƙasan ɗakin, tayi wankan nan tsigar jikinta na tashi saboda yadda ruwan in ya zuba a ƙasa yake taɓata, ga tashin zuciya saboda ƙarnin sabulun, ba shiri ta ajiye sabulun tayi wankan a haja, sedai taji daɗin ruwan zafin sosai "

Ta fito tana kama bango, Yusuf ya riƙeta ya maida ita ɗaki, ya duba Akwatinta ya ɗakko kaya ya bata, ta saka itama tayi salla.

Saleh beje gida ba se bayan sha biyu na dare, yayi tunanin ko yaje yayi magana da doctor Safwan amma wata zuciyar ta hana shi, saboda yadda Safwan ya dinga rawar jiki da yaji batun kuÉ—i tsaf zeje ya gaya musu, yaje ya sameshi.
Gaba ɗaya tunaninsa ya koma kan yaze ƙwaci Alhaji Nasir a gurin wannan Azzaluman mutanen? Dan ba ƙaramin shiri suke dashi ba.

Me Adda suka koma inda suka ajiye su Widad, da niyyar ayita ta ƙare, suna zuwa suka buɗe gidan, suka shiga suka saka mukulli suka buɗe ɗakin suka ga wayam ba kowa a ciki, a kiɗime ɗayan yace  "Me Adda bafa kowa a ɗakin nan"

Ƙarasawa yayi da sauri ya shiga ɗakin shima amma ba kowa a ciki, nan da nan suka gigice suka shiga lalauben su Widad.

Me Adda yace "Mutanen da ko iya takawa basayi, ta yaya zasu gudu? Duk matakan tsaron dake gurin nan ina sukabi suka fita?"

Cam ɗaya daga cikinsu ya ɗaga kai ya kalli Roofing ɗakin yace  "me Adda kalli ta nan suka fice" yai maganar yana nuna musu saman roofing ɗakin

Me Adda a gigice yace "ya zama dole mu bazama neman su, amma ta yaya suka samu abu sukayi hanya har suka fita?"

ÆŠaya daga cikinsu yace "Allah ne ya san yadda suka gudu"

Me Adda yace  "bamu da lokacin ɓatawa, maza maza mubi sahun su yadda suke a galabaice ba lallai su iya tafiya me nisa ba"
Haka kuwa akayi suka rarraba kansu a cikin daji.

Saleh yaje duba Alhaji Nasir a Asibiti, ya tarar da Anwar a gurinsa, suka gaisa yayi masa ya me jiki, ya É—an dubi Anwar yace
"Amma meyasa baza'a fita da Alhaji waje a nema masa magani ba?"

Anwar yace  "Nayi duk me yuwuwa inga an fita da shi, amma Mummy da Alhaji Bulama sunce nan ma ana kula da shi"

Saleh yace "Abunda za'ayi yanzu shi ne, ka É—auke shi ka canza masa Asibiti ba tare da ka sanar dasu ba, ko ba'a fita dashi waje ba a camza masa Asibiti, sedai kawai suga ka canza maaa Asibiti"

Anwar yace  "Amma zasuji babu daɗi idan nayi hakan, suna ganin nanma ana ƙoƙari akansa amma inyi haka kamar ban kyauta ba"

"Anwar zamanku a Asibitin nan yaci ace jikinsa yana karɓar treatment yadda yakamata, amma har yanzu babu wani cigaba, mu canza masa wani Asibitin kawai"

Anwar yace  "Kana ganin babu matsala idan muka yi hakan?"

"eh babu matsala, Amma karkace ni nace ka canza masa Asibiti"

Anwae yace  "shikenan, ka kawo shawara me kyau insha Allah gobe in Allah ya kaimu da Safe, sedai suzo su tarar na canza masa Asibiti ni kaina rashin samun sauƙin nan nasa yana bani mamaki"

Doctor Sufyan ne yake ta zagaye acikin Office É—insa, yana tunanin me yakamata yayi akan batun su Alhaji Haruna, yana tuno irin halacci da kirkin Alhaji Daula, idan aka haÉ—a kai dashi aka cutar dashi to tabbas mesa Adalci ba, Amma wani mataki Alhaji Musa zasu É—auka akansa idan har be abunda sukace ba?.

Fitowa yayi da sauri daga office É—in nasa ya nufi É—akin da Alhaji Nasir yake, yana zuwa shiga suka haÉ—u da Saleh, suka yi kallon kallo babu wanda ya cewa kowa komai suka wuce.

Ya shiga É—akin da Sallama, Anwar ya amsa masa, doctor Sufyan yace "Anwar yame jikin kuwa?"

"Jiki sedai muce Alhamdilillah, amma doctor na fara karaya da yanayin jikin sa, babu wani cigaba fa gashi nayiwa su Mummy magana a fita dashi amma sunƙi amincewa, na rasa dalili"

Sufyan yace  "ka kwantar da hankalinka Anwar, treatments ɗin dai da muke masa anan, shi za suyi masa a can, komai ze tafi dai dai ze warke in Allah ya yarda"

Anwar yace "Shikenan Allah yasa"
Chapter 58 · 0% Book details