Sashe 39
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbas yace "garajen Meka ke hakane Yusuf? Ka bari ka kammala binciken nan, idan ka kammala base ka kawo masa ba, Yallaɓan mafa baya nan ana nemansa a headquarter za suyi meeting, kasan koka bashi cewa zeyi kabi komai a hankali"
"So kake inzo inyi laifi kenan? Ni nafi ganewa in fara presenting É—in aikin"
Abbas yace "A'a karka damu, kabi komai a hankali"
Yusuf yace "shikenan bari in tashi in tafi, dama nan aikena aka yi"
Abbas yace "Amma Yusuf akwai cigaba a cikin binciken kuwa?"
Yusuf yace "Sosai makuwa, an samu ci gaba, the more nake binciken the more nake sake cin karo da wasu matsalolin, Amma idan bincikena ya tabbatar da abunda nake zargi, mutane da yawa a ƙasar nan za suji kunya"
Abbas yace "wai tukuna ma inga abunda kayi kake son ka nuna masan, suwaye za suji kunyar?"
Yusuf yace "kabari sena kuma dawowa se mu cigaba da zancen yanzu ina sauri tunda baya nan tafiya zanyi"
Yusuf yaja System ɗinshi yai waje, bayansa Abbas yabi da kallo yana ƙwafa, 'Sena sa an Ƙwace aikin daga hannun ka tukuna za kayi bayani'
Sakina tana so ta yiwa Yusuf magana, amma sam yaƙi bata fuska, tana ji tana gani ya fice daga gurin, tunani ta shiga yi, yadda Yusuf ya yadda da Abbas babu lallai kota gaya masa ya yadda da abunda tace.
Yusuf yaje yayiwa Widad siyayyar data aike shi, ya wuce gida ya gama abunda yake yi sannan ya koma gidan su Widad.
Har yanzu gabansa faÉ—uwa yake, ya É—au kayan ya shiga ya kai mata, sedai da yaje bata part É—in nata se maganta akan gado.
Ya ajiye mata kayayyakin, ya ɗaga ƙasan pillow ɗinta ya sa mata ATM Card ɗinta ya fito.
A falo ya ci karo da maman su Amal, ta masa wani irin mugun kallo tace "kai daga yau, bana son sake ganin ka shigomin falo ba tare da ka nemi izini ba, na gaji da wannan sintirin da kakemin, baligi kana ratsawa kana wuce ɗakin ta, baze yuwu ba"
"kiyi haƙuri Hajiya, nima ba da san raina ba, sedai ita Madam bata jiran izinin kowa kafin ta yanke hukunci, dan haka wannan maganar a tsakanin ku ya kamata ku tattauna ta"
Har Hajiya Halima ta buÉ—e baki zata yi magana se kuma tayi shiru, waiwaya wa yayi yaga Shigowar Widad ce tasa ta yin shiru, bata kula su ba tayi part É—inta, shima Yusuf ya silale ya bar falon.
*******************************
"Maman Yara ina cikin farinciki Ɗana ze dawo, yakamata ayi dukkanin wasu shirye shirye da suka dace domin tarbarsa, yasuhe rabon sa da ƙasar nan? Sannan ya dawo ya tarar da kyakkyawan Albishir"
Haɗe rai Hajiya Sarah tayi tace "nikuma takaici ne fal raina wallahi"
"Saboda me takaici fal ranki, kamar ba É—anki me ze dawo ba?"
"Eh É—ana ne, amma abunda kake shirin yi kaima kasan be kamata ba, ta yaya yarona lafiyayye zaka haÉ—a shi Aure da mahaukaciyar da bata san girman kowa ba, ga bata da tarbiyya"
Alhaji Bulama yace "Easy Madam, Sarah shifa ɗa na kowane, bekamata ki cigaba da aibata Widad ba, itama kamsr 'ya take a gurin mu duba da yadda mahaifinta yayi mana halacci a rayuwa, muna ƙoƙarin yin abunda zesa ta dawo hayyacin ta ne, kuma kinga mu munsan larurarta, Fahad ze iya haƙuri ya zauna da ita, saɓanin a bawa wani a waje Auren ta"
"to kai kaÉ—ai ne yakamata kayi tamakon? Ina sauran mutanen gari? Nidai gaskiya aka haÉ—a Auren É—ana da wannan tantiriyar mara mutuncin an cucemu, kai kanka da kake matsayin uba a gurin ta cin zarafin ka take, inaga É—anka kuma?"
"Sarah, bazan zaɓawa yarona abunda ze cutar da shi ba, Aure yana gyara mutum, wuyarta su zauna a guri ɗaya ze iya canza ta"
"A'a canza halin wannan yarinyar banga ta inda ze yuwu ba Sam, kawai ka canza shawara da tunani"
Tai maganar tare da miƙewa ta bar masa ɗakin
************************************
Yallaɓai Suleiman na dawowa, Abbas ya miƙe ya tafi Office ɗinsa, ya shiga ya gaida Sulaiman cikin girmamawa irin ta masu ɗamara, se da yayi masa izini sannan ya zauna, suka sake gaisawa.
Abbas yace "Yallaɓai, lokaci fa na ƙurewa, game da aikin nan daka bawa Yusuf, bana tunanin abunda aka sashi yake yi, ɗazu yazo gurin nan, na ɗanyi masa tambayoyi akan aikin, Amma Amsoshin daya bani sam basu gamsheni ba, da alama dukiyar dake gidan da alherin da suke masa yasa ya bar aikin da 'aka sashi "
" Amma a iya sanina Yusuf mutum ne me hazaƙa, nasan shi da ƙwazo da himma akan aiki, ba shida kwaɗayi sam"
"Yallaɓai mutum na iya canzawa a kowane lokaci, Yusuf abokina ne, amma ba yadda zanyi, bana son inci amanar aiki ko' a samu matsala akan harkar aikin mu kimar mu ta zube a idon duniya, Amma ya kamata kayi wani abu yallaɓai"
Suleiman ya ɗanyi shiru sannan yace "idan kuwa hakane, to tabbas Yusuf ya bani mama, sedai zan kira shi muyi magana, zan bibiye shi idan har na gano maganar da kake gayamin gaskiya ne, zan ɗau mataki na musamman akansa"
Abbas yace "Yallaɓai idan har ka kira shi kuyi magana ai zaka ɓata komai, zeyi duk me yuwuwa ya kare kansa koda kuwa ƙarya ze maka danka yarda da shi, tunda shima jami'in tsaro ne yasan duk hanyar da zebi ya kare kansa"
Suleman yace "Abbas base ka nunamin aikina ba, Nagode da wannan bayani naka zan bincika, ka ciji jami'i nagari tunda har kishin aikin ka be hanaka ɓoye laifin Abokin ka ba"
Abbas ya miƙe ya sarawa Suleiman sannan ya fice.
Koda ya bar Office É—in Suleiman Office É—insa ya koma yana tunani, tunani yake akanme zeyi wanda zesa gaba É—aya aikin da Yusuf yayi ya lalace kowa ma ya huta?
************************************
Gaba ɗaya Nurat ta rasa abunda yake mata daɗi, ta shiga damuwa rashin samun wayar mutumin da ko sunansa bata sani ba, dama Widad ta dena ɗaga wayarta gaba ɗaya, tun ranar da tazo birthday ɗin ta, abun nan ya faru, ta fara shawarar ko gidan su Widad zata je don ta tambaye ta wannan wanda suka zo taren.
Sedai kuma tayi wani tunani, aiki ne me matuƙar sauƙi a gurin Widad ta sa aka mata a ɗaure, bata da tabbacin Abokinta ya gayawa Widad abunda ya faru kokuma A'a, gaba ɗaya ta rasa abunda yake mata daɗi, komai ya dena mata daɗi se tunanin wannan bawan Allah, me matuƙar kirki, a farko tayi zaton shima mugu ne lokacin da ya ritsata har yayi mata barazana, amma yanzu ta gane ba haka abun yake ba, ranar da yazo gidan yanayin yadda ya mu'analance ta da kyakkyawar ma'amala.
************************************.
Fahad ne da Anwar tsaye a tashar jirgin Sama, Anwar yace "Fahad ina taya ka murnar kammala karatun ka, Allah ubangiji ya kaika gida lafiya, sena taho nima in next couple of weeks Insha Allah"
Fahad yayi murmushi yace "to baban Soyayya, kaima ina taya ka murna, tsiran namu befi sati biyu, ina maka fatan Nasara ɗan uwana seka taho".
Suka rungume juna suna murmushi, sannan Fahad yaja trolley É—insa yayi gaba.
"Amal kin san wani abu kuwa? Munyi waya da Yaya Anwar yace min Fahad yau ze dawo Nigeria, baki ji daÉ—in da nake ji ba, dan Allah me ya kamata inyi wanda zan sake kama zuciyar sa, yaji in ba niba se rijiya"
Wani banzan kallo Amal tayi wa Ramlah tace "Ban sani ba, kije kiyi abunda kika ga ya dace"
Cike da mamaki Ramlah tace "lafiyar ki kuwa? Me yayi zafi daga neman shawara zaki hayayyaƙomin?"
"dole kice haka mana, da yake matsalarki itace damuwa kawai, ni ina lokacin da nake cikin tawa damuwar ziga Mummy kikeyi, kuka haɗemin kai kuka dinga hantara ta, har dena kulani kukayi saboda kawai nace ina son Yusuf, Ashe ke kaɗai kika san So, ni ban sanshi ba ko? Can ta mulmule miki gara tun wuri kema ki cire shi daga ranki, dan in kin manta bari in tuna miki, 'yar masu gida akace ze aura kuma kinsan baki isa kice kina da matsala da hakan ba, danke ba mutum bace a kanta, kuma kinsan baki isa kiyi takara da ita ba, akan haka ba' aƙi a baki red card daga gidan nan ba, you better go back to your senses "
Tana gama faɗin haka ta miƙe ta fice daga ɗakin, wani zazzafan gumi ne ya shiga karyowa Ramla, dan gaba ɗaya ta manta ds batun ance za'a haɗa Auren Widad da Fahad.
Gaba É—aya kanta ys kulle dan bata san wama yakamata ta tunkara ba, Mummy ba abunda zata iyayi, shiru tayi tana tunanin meye mafita? "
************************************
Widad ta dudduba Aiken da Yusuf ya kawo mata, ya siyo komai kamar yadda tace, harda receipt ya kawo mata, tana duddubawa taci karo da wata leda, ɗakko ledar tayi ta buɗe me zata gani, wasu tsala tsalan Abaya ne kala biyar, kowacce da kalar ta sunsha stones se ƙyalli sukeyi, ta ɗauka ɗaya bayan ɗaya tana jujjuya su.
'me wannan gayen yake nufi?' ta tambayi kanta
'harni ze saiwa kaya ya bani? Meya maida ni ko nayi masa kalar saka wannan kayan?'
Tattare kayan tayi ta fito falo a fusace, da watsasu akan kujera, part É—in su Amal ta nufa tana huci, babu ko sallama ta banka É—akin su Amal, gaba É—aya seda suka razana, mussman Amal dan a tsorace take tun ranar da Widad ta gansu tare da Yusuf.
Ta kalli Amal tace "Kije bakin gate, ki kiramin wancan sakaran direban yanzun nan" tana gama maganar ta juya ta fice
Ramalh na ganin a yadda Widad ta shigo tayi magana, tasan akwai matsala dan haka ta miƙe ta fita dan ganin me ze faru,
Jikin Amal na rawa ta miƙe tayi waje kiran Yusuf.
Koda saƙon Kiran Widad ya riski Yusuf yasan a rina, yasan ze fuskanci wulaƙanci, Amma ya dake ya shiga cikin gidan.
A falo ya tarar da ita a tsaye, tana wani irin huci, haɗi da sauke numfashi, Tabbas Widad Yarinya ce ƙarama Amma Allah yayi mata kwarjini na musamman.
Yaje daf da ita ya tsaya ya sunkuyar da kai ba tare da yace komai ba.
"Kalleni nan"
"So kake inzo inyi laifi kenan? Ni nafi ganewa in fara presenting É—in aikin"
Abbas yace "A'a karka damu, kabi komai a hankali"
Yusuf yace "shikenan bari in tashi in tafi, dama nan aikena aka yi"
Abbas yace "Amma Yusuf akwai cigaba a cikin binciken kuwa?"
Yusuf yace "Sosai makuwa, an samu ci gaba, the more nake binciken the more nake sake cin karo da wasu matsalolin, Amma idan bincikena ya tabbatar da abunda nake zargi, mutane da yawa a ƙasar nan za suji kunya"
Abbas yace "wai tukuna ma inga abunda kayi kake son ka nuna masan, suwaye za suji kunyar?"
Yusuf yace "kabari sena kuma dawowa se mu cigaba da zancen yanzu ina sauri tunda baya nan tafiya zanyi"
Yusuf yaja System ɗinshi yai waje, bayansa Abbas yabi da kallo yana ƙwafa, 'Sena sa an Ƙwace aikin daga hannun ka tukuna za kayi bayani'
Sakina tana so ta yiwa Yusuf magana, amma sam yaƙi bata fuska, tana ji tana gani ya fice daga gurin, tunani ta shiga yi, yadda Yusuf ya yadda da Abbas babu lallai kota gaya masa ya yadda da abunda tace.
Yusuf yaje yayiwa Widad siyayyar data aike shi, ya wuce gida ya gama abunda yake yi sannan ya koma gidan su Widad.
Har yanzu gabansa faÉ—uwa yake, ya É—au kayan ya shiga ya kai mata, sedai da yaje bata part É—in nata se maganta akan gado.
Ya ajiye mata kayayyakin, ya ɗaga ƙasan pillow ɗinta ya sa mata ATM Card ɗinta ya fito.
A falo ya ci karo da maman su Amal, ta masa wani irin mugun kallo tace "kai daga yau, bana son sake ganin ka shigomin falo ba tare da ka nemi izini ba, na gaji da wannan sintirin da kakemin, baligi kana ratsawa kana wuce ɗakin ta, baze yuwu ba"
"kiyi haƙuri Hajiya, nima ba da san raina ba, sedai ita Madam bata jiran izinin kowa kafin ta yanke hukunci, dan haka wannan maganar a tsakanin ku ya kamata ku tattauna ta"
Har Hajiya Halima ta buÉ—e baki zata yi magana se kuma tayi shiru, waiwaya wa yayi yaga Shigowar Widad ce tasa ta yin shiru, bata kula su ba tayi part É—inta, shima Yusuf ya silale ya bar falon.
*******************************
"Maman Yara ina cikin farinciki Ɗana ze dawo, yakamata ayi dukkanin wasu shirye shirye da suka dace domin tarbarsa, yasuhe rabon sa da ƙasar nan? Sannan ya dawo ya tarar da kyakkyawan Albishir"
Haɗe rai Hajiya Sarah tayi tace "nikuma takaici ne fal raina wallahi"
"Saboda me takaici fal ranki, kamar ba É—anki me ze dawo ba?"
"Eh É—ana ne, amma abunda kake shirin yi kaima kasan be kamata ba, ta yaya yarona lafiyayye zaka haÉ—a shi Aure da mahaukaciyar da bata san girman kowa ba, ga bata da tarbiyya"
Alhaji Bulama yace "Easy Madam, Sarah shifa ɗa na kowane, bekamata ki cigaba da aibata Widad ba, itama kamsr 'ya take a gurin mu duba da yadda mahaifinta yayi mana halacci a rayuwa, muna ƙoƙarin yin abunda zesa ta dawo hayyacin ta ne, kuma kinga mu munsan larurarta, Fahad ze iya haƙuri ya zauna da ita, saɓanin a bawa wani a waje Auren ta"
"to kai kaÉ—ai ne yakamata kayi tamakon? Ina sauran mutanen gari? Nidai gaskiya aka haÉ—a Auren É—ana da wannan tantiriyar mara mutuncin an cucemu, kai kanka da kake matsayin uba a gurin ta cin zarafin ka take, inaga É—anka kuma?"
"Sarah, bazan zaɓawa yarona abunda ze cutar da shi ba, Aure yana gyara mutum, wuyarta su zauna a guri ɗaya ze iya canza ta"
"A'a canza halin wannan yarinyar banga ta inda ze yuwu ba Sam, kawai ka canza shawara da tunani"
Tai maganar tare da miƙewa ta bar masa ɗakin
************************************
Yallaɓai Suleiman na dawowa, Abbas ya miƙe ya tafi Office ɗinsa, ya shiga ya gaida Sulaiman cikin girmamawa irin ta masu ɗamara, se da yayi masa izini sannan ya zauna, suka sake gaisawa.
Abbas yace "Yallaɓai, lokaci fa na ƙurewa, game da aikin nan daka bawa Yusuf, bana tunanin abunda aka sashi yake yi, ɗazu yazo gurin nan, na ɗanyi masa tambayoyi akan aikin, Amma Amsoshin daya bani sam basu gamsheni ba, da alama dukiyar dake gidan da alherin da suke masa yasa ya bar aikin da 'aka sashi "
" Amma a iya sanina Yusuf mutum ne me hazaƙa, nasan shi da ƙwazo da himma akan aiki, ba shida kwaɗayi sam"
"Yallaɓai mutum na iya canzawa a kowane lokaci, Yusuf abokina ne, amma ba yadda zanyi, bana son inci amanar aiki ko' a samu matsala akan harkar aikin mu kimar mu ta zube a idon duniya, Amma ya kamata kayi wani abu yallaɓai"
Suleiman ya ɗanyi shiru sannan yace "idan kuwa hakane, to tabbas Yusuf ya bani mama, sedai zan kira shi muyi magana, zan bibiye shi idan har na gano maganar da kake gayamin gaskiya ne, zan ɗau mataki na musamman akansa"
Abbas yace "Yallaɓai idan har ka kira shi kuyi magana ai zaka ɓata komai, zeyi duk me yuwuwa ya kare kansa koda kuwa ƙarya ze maka danka yarda da shi, tunda shima jami'in tsaro ne yasan duk hanyar da zebi ya kare kansa"
Suleman yace "Abbas base ka nunamin aikina ba, Nagode da wannan bayani naka zan bincika, ka ciji jami'i nagari tunda har kishin aikin ka be hanaka ɓoye laifin Abokin ka ba"
Abbas ya miƙe ya sarawa Suleiman sannan ya fice.
Koda ya bar Office É—in Suleiman Office É—insa ya koma yana tunani, tunani yake akanme zeyi wanda zesa gaba É—aya aikin da Yusuf yayi ya lalace kowa ma ya huta?
************************************
Gaba ɗaya Nurat ta rasa abunda yake mata daɗi, ta shiga damuwa rashin samun wayar mutumin da ko sunansa bata sani ba, dama Widad ta dena ɗaga wayarta gaba ɗaya, tun ranar da tazo birthday ɗin ta, abun nan ya faru, ta fara shawarar ko gidan su Widad zata je don ta tambaye ta wannan wanda suka zo taren.
Sedai kuma tayi wani tunani, aiki ne me matuƙar sauƙi a gurin Widad ta sa aka mata a ɗaure, bata da tabbacin Abokinta ya gayawa Widad abunda ya faru kokuma A'a, gaba ɗaya ta rasa abunda yake mata daɗi, komai ya dena mata daɗi se tunanin wannan bawan Allah, me matuƙar kirki, a farko tayi zaton shima mugu ne lokacin da ya ritsata har yayi mata barazana, amma yanzu ta gane ba haka abun yake ba, ranar da yazo gidan yanayin yadda ya mu'analance ta da kyakkyawar ma'amala.
************************************.
Fahad ne da Anwar tsaye a tashar jirgin Sama, Anwar yace "Fahad ina taya ka murnar kammala karatun ka, Allah ubangiji ya kaika gida lafiya, sena taho nima in next couple of weeks Insha Allah"
Fahad yayi murmushi yace "to baban Soyayya, kaima ina taya ka murna, tsiran namu befi sati biyu, ina maka fatan Nasara ɗan uwana seka taho".
Suka rungume juna suna murmushi, sannan Fahad yaja trolley É—insa yayi gaba.
"Amal kin san wani abu kuwa? Munyi waya da Yaya Anwar yace min Fahad yau ze dawo Nigeria, baki ji daÉ—in da nake ji ba, dan Allah me ya kamata inyi wanda zan sake kama zuciyar sa, yaji in ba niba se rijiya"
Wani banzan kallo Amal tayi wa Ramlah tace "Ban sani ba, kije kiyi abunda kika ga ya dace"
Cike da mamaki Ramlah tace "lafiyar ki kuwa? Me yayi zafi daga neman shawara zaki hayayyaƙomin?"
"dole kice haka mana, da yake matsalarki itace damuwa kawai, ni ina lokacin da nake cikin tawa damuwar ziga Mummy kikeyi, kuka haɗemin kai kuka dinga hantara ta, har dena kulani kukayi saboda kawai nace ina son Yusuf, Ashe ke kaɗai kika san So, ni ban sanshi ba ko? Can ta mulmule miki gara tun wuri kema ki cire shi daga ranki, dan in kin manta bari in tuna miki, 'yar masu gida akace ze aura kuma kinsan baki isa kice kina da matsala da hakan ba, danke ba mutum bace a kanta, kuma kinsan baki isa kiyi takara da ita ba, akan haka ba' aƙi a baki red card daga gidan nan ba, you better go back to your senses "
Tana gama faɗin haka ta miƙe ta fice daga ɗakin, wani zazzafan gumi ne ya shiga karyowa Ramla, dan gaba ɗaya ta manta ds batun ance za'a haɗa Auren Widad da Fahad.
Gaba É—aya kanta ys kulle dan bata san wama yakamata ta tunkara ba, Mummy ba abunda zata iyayi, shiru tayi tana tunanin meye mafita? "
************************************
Widad ta dudduba Aiken da Yusuf ya kawo mata, ya siyo komai kamar yadda tace, harda receipt ya kawo mata, tana duddubawa taci karo da wata leda, ɗakko ledar tayi ta buɗe me zata gani, wasu tsala tsalan Abaya ne kala biyar, kowacce da kalar ta sunsha stones se ƙyalli sukeyi, ta ɗauka ɗaya bayan ɗaya tana jujjuya su.
'me wannan gayen yake nufi?' ta tambayi kanta
'harni ze saiwa kaya ya bani? Meya maida ni ko nayi masa kalar saka wannan kayan?'
Tattare kayan tayi ta fito falo a fusace, da watsasu akan kujera, part É—in su Amal ta nufa tana huci, babu ko sallama ta banka É—akin su Amal, gaba É—aya seda suka razana, mussman Amal dan a tsorace take tun ranar da Widad ta gansu tare da Yusuf.
Ta kalli Amal tace "Kije bakin gate, ki kiramin wancan sakaran direban yanzun nan" tana gama maganar ta juya ta fice
Ramalh na ganin a yadda Widad ta shigo tayi magana, tasan akwai matsala dan haka ta miƙe ta fita dan ganin me ze faru,
Jikin Amal na rawa ta miƙe tayi waje kiran Yusuf.
Koda saƙon Kiran Widad ya riski Yusuf yasan a rina, yasan ze fuskanci wulaƙanci, Amma ya dake ya shiga cikin gidan.
A falo ya tarar da ita a tsaye, tana wani irin huci, haɗi da sauke numfashi, Tabbas Widad Yarinya ce ƙarama Amma Allah yayi mata kwarjini na musamman.
Yaje daf da ita ya tsaya ya sunkuyar da kai ba tare da yace komai ba.
"Kalleni nan"