Sashe 76
Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin damuwa Hindu tace "dan Allah Amarya kiyi haƙuri, ni ban san meyasa take wannan abubuwan ba"
Widad tayi murmushi tace "Ni banyi fushi ba ai, bakomai"
Saleh ya É—au waya ya kira Abbas, sedai har tayi ringing ta katse be É—aga ba, tana katsewar ne Abbas ya biyo kiran, Saleh ya É—aga tare da yin Sallama Abbas ya amsa, Saleh yace
"Malam Abbas, kayi gaba ko waiwaye baka yi, kana da labarin an sace amininka kuwa tare da 'yar gidan Daula?"
Abbas yace "ƙwarai kuwa na sani, dan nine ma na gayawa mahaifiyarsa"
Saleh yace "Wani tunani kayi akai kuwa?"
"wani tunani zanyi kuwa, maganinsa kenan ai, shegen shishshiginsa da rawar kai yaja masa, ni Allah ne ya dube ni, dani naso in maye gurbinsa da dani za'a ɗauke, Amma kuwa an karɓi files ɗin daga hannunsa?"
Shiru Saleh yayi sannan yace "basu karɓa ba tukuna, ni suke jira, har yanzu basu san cewar Yusuf ne jami'in tsaron ba, zancen da nake maka yanzu haka Yusuf sun tsere daga inda aka ɓoye su"
Abbas yace "haba dai, garin yaya akayi suka tsere? Kai Yusuf fa ba ƙaramin hatsabibi bane ba"
Saleh yace "babu wanda ya sani, kuma har suka gudu ba'a samu karɓar abun nan daga hannun yarinyar ba, yanzu maganar da nake maka, shi kansa Daulan an ɗauke shi a gadon Asibiti, babu wanda yasan inda yake"
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, garin yaya, yanzu shikenan munyi biyu babu, nifa ba wanda yake tuntuɓata yanzu tunda akamin transfer"
Saleh yace "karka damu, ina son ka saurareni da kyau, duk abunda ake ciki zan dinga sanar da kai, karka kusakura wani daga cikin su yayi yunƙurin haɗa kai da kai, dan yanzu gaba ɗaya kawunansu a rarrabe yake, duk wanda ya tuntuɓeka koya tambayeka wani abu game da wanda aka bawa binciken nan kace baka sani ba"
Abbas yace "to aini basu sanni ba, kai suka sani me zesa su nemeni?"
"Abbas mutane ne masu wayo matuƙa, yanzu haka a manyanka na gurin aiki wani ze iya bugun cikinka ya tambayeka wani abu, karka kuskura ka gaya wani, wani abu akan harkar nan, na gaya maka kansu ya rarrabu, wasu zasu iya zamewa suyi harkar nan babu mu, bayan wahalar da mukayi "
Abbas yace " bakomai na fahimce ka, Insha Allah babu wanda zeji wata magana daga bakina, dama kai ka jawoni cikin harkar "
Saleh yace " Good nagode "
Sukayi Sallama, Saleh ya jinjina kai yanzu ya sake jinjinawa Widad, lallai bata da laifi naƙin yadda da mutane, ƙir ƙiri Abbas na jikin Yusuf ne, amma saboda kuɗi yake masa zagon ƙasa, tabbas mutum abun tsoro ne, kuma da alama Abbas Soko ne, dan haka yi masa wayo ba wani abu bane me wahala.
Saleh yana son sake komawa gurinsu Widad, dan haka yana ta É—anyi musu siyayya.
Alhaji Musa ne ya kira shi a waya yace 'lallai yana son ganinsa a guest house É—insa'
Haka Saleh ya bar abunda yake yi ya tafi gidan Alhaji Musa.
Yaje ya tarar dashi a lambun dake gidan, suka gaisa Alhaji Musa yace "Saleh ina cikin damuwa fa"
"wace irin damuwa kuma ranka ya daÉ—e?"
"Na fuskanci Nurat tana ƙoƙarin fara yin shisshigi ga al'amuran Daula, gashi yanzu ina ɗari ɗari da su Haruna, ina tsoron Ayi Amfani da ita a cutar da ita koni, yanzu babban abunda ya sake bani mamaki be wuce yadda Daula yayi ɓatan dabo ba, ko kusa ko alama an rasa inda yake, zargina yana ƙara tabatta akan ana min maƙarƙashiya, kodai su Alhaji Haruna suke cuta ta suke al'amuran su suka ɗai, kokuma akwai wani a gefe daya ke harin abunda muke hari, ko kuma yasan siriinmu yake son temakawa Daula"
Saleh yayi ajiyar zuciya yace "banƙi ta taka ba, Amma ko waye wannan tabbas na jikin ku ne, amma abun da mamaki ace an nemi Daula ko sama ko ƙasa an rasa sekace wata takadda"
"Shine abunda ya É—auremin kai ai, ni yanzu gefe zan koma in nemawa kaina mafita, idan abun nan ya samu shikenan, in be samu ba shikenan, suma har yanzu da suka gudu babu wanda ya sake jin É—uriyarsu, dan haka ni inaga tunda babu wanda yasan inda Daula yake, zan fito takarar Senate ne kawai "
Da sauri Saleh ya kalle shi yace " Amma ta yaya kake tunanin mutane zasu yarda su zaɓeka? Bayan Daula ya riga ya ɓata siyasarka a idon duniya? "
Alhaji Musa yace " shiyasa nima na ƙuduri aniyar kota wane hali, sena Wulaƙanta Daula a idon duniya, sannan malamai zan shiga a rufemin bakin jama'a, akwai yarana da suke aiki a wasu daga kamfanunukan Daula, zamu haɗa kai dasu mu karkatar da wasu kuɗaɗe inyi amfani da su, niba kuɗin Daula ne sjka dameni ba, yadda zan Wulaƙanta shi in ɗaiɗaita shine ya dameni, amma ko yanzu na rage raɗaɗin dake zuciyata, kuma zan cigaba da bibiyarsa se naga babu inda ya rage wanda ze jingina yaji daɗi, sannan in dawo kan su Alhaji Munir"
Yadda Alhaji Musa ke maganar babu alamun tausayi ko imani a tare da shi, har zuciyarsa yake faÉ—ar wannan maganganun.
Saleh ya ɓoye duk mamakinsa, ya dinga ziga Alhaji Musa, Alhaji Musa ya kawo kuɗi ya bawa Saleh, Saleh a ransa yace "ka bada kuɗin da zanyiwa maƙiyan ka siyayya, kuma nima zancigaba da bibiyarku, ɗaya bayan ɗaya sena ɗau fansar cin amanata da kuka yi, da saɓa Yarjejeniyar da muka yi daku"
Widad gaba É—aya hirar da suka yi da Hindu ta tsaye mata a zuciya, ta tuna yadda haka siddan se É—an kasuwa yayiwa É—an siyasa kyauta motar miliyoyi, ko biliyoyin nairori, Amma al'ummar su suna tagayyara, da yunwa da rashin kyakkyawan mahalli.
Yusuf yaga gaba ɗaya Widad tayi wani iri, seta zauna tayi shiru tana tunani, dukda shima zuciyarsa ba daɗi, Amma sam baya son ganinta a damuwa dan haka yace "Ran gimbiyata ya daɗe meke damunki ne?"
Jiki a sanyaye tace "Abubuwa da yawa"
Yusuf yace "Kamar me? Ko har yanzu fushin kike dani"?
Jiki a matukar sanyaye ta bashi labarin hirar da suka yi da Hindu, daga ƙarshe tace "tabbas ƙaddarar data sameni na zuwa ƙauyen nan, ishara ce Allah ya nunamin, na rayu cikin gata wanda nake ganin babu wani abu da zan iya nema in rasa a rayuwata, ranar da kace min akwai mutanen da Naira ɗari take gagararsu, gani nake kawai ka faɗane dan ka rainamin hankali saboda a lokacin, abun da ke cikin asusun bankina ya ninka ɗari sau ɗari, bani da wata damuwa ko matsala, Amma ace a rayuwa akwai tarin 'ya' ya mata da suke zaune ba ilimi? Akwai tarin mutanen da suke rayuwa da gurɓataccen ruwan sha? Akwai tarin yara manyan gobe da rayuwarsu ta lalace saboda rashin gurin samun ilimi, Yoseef yaran masu kuɗi na Almubazzaranci da dukiya, da yawanmu bamu san yadda aka tara kuɗin ba... Kasa ƙarasawa tayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, wani irin ɓacin rai ke taso mata, yadda ake ɓarnar kuɗi gurin bukukuwan birthday dana Aure, da makamantan su.
Yusuf ya taso daga inda yake, yazo ya samu guri ya zauna kusa da ita yace "Widad baki ga komai ba, a yanzu haka a cikin ni'ima muke, a gidan megari muke a zaune, kuma gidansa da rufin Asiri, ya kike tunanin gidajen sauran talakawa da suke garin nan? Wanima abunda zasu cin ma babu, Widad talauci gaskiya ne, shiyasa Wulaƙanta mutane bashi da kyau "
Widad tace" tabbas wulaƙanta mutane bashi da kyau, nasan mutane dayawa sunamin kallon mace me izza da Wulaƙanta mutane, sedai...
Se kuma tayi shiru, Yusuf yace "sedai me?"
"Bakomai" ta bashi amsa tare da basar da zancen.
Da Asuba bayan Yusuf ya dawo daga sallar Asuba yazo ya tattara kwanuka zeje ya wanke, Widad tace "ka bari zan wanke"
Yusuf yace "No ki huta kawai, bari in wanke ai ba yawa kwanukan"
Widad tace "ce maka akayi ban iya wanke wanken bane?"
"Ni na isa ince gimbiya bata iya wanke wanke ba?"
Widad tace "gashi nan kuwa ka faÉ—a"
"A'a ni ban faÉ—a ba, taso muje muyi tare"
Widad ta tashi tabi Yusuf suka je suka wanke kwanukan tare, ta tattare duk kwanukan wanke wanken da'akayi fatali dasu na Abincin dare a tsakar gidan, ta haÉ—esu a guri É—aya, Yusuf yasa tsintsiya duk girman tsakar gidan yana sharewa, Widad ta dinga kallon ikon Allah, yadda Yusuf yake sarrafa tsintsiya kamar mace.
Widad tace "dan Allah dagaske kai ka É—aine a gidanku?"
Yusuf yace "Eh nikaÉ—ai ne Mamana ta haifa, ni nake mata aikin gida, shara, wanke_wanke hadda girki duk ta koyamin ni nake yi, idan ta tafi unguwa kafin ta dawo nayi komai"
Widad tace "shiyasa ka iya aiki sosai, nima nasan da tare na girma da Ammi na da duk na iya aiki, da baza'a dinga kallon ban iya komaiba"
Yusuf yazo kusa da ita ya tsaya, ya kalleta yace "karki damu gimbiyata, Insha Allah muna tare zaki iya komai kafin mu koma gida"
Widad ta kalle shi tace "dagaske har girki zaka koyamin? Nafa iya girki amma ba sosai ba"
Hannu yasa ya ɗago haɓarta yace "zaki iya komai insha Allah, duk zan koya miki, amma bana son taurin kai, dan nasan halinki"
"Nice me taurin kai?"
Yusuf yace "eh kina dashi amma kaÉ—an"
Murmushi Widad tayi tace "Ni dai in zaka koyamin zanyi duk abunda kake so"
Yusuf yace "dagaske?"
Widad ta jinjina masa kai, ya matso daf da ita yace "to shikenan, Yimin kiss a goshina ma ba'a baki ba, se in koya miki kunna risho yau"
Tureshi tayi tace "Baza'ai wannan É—inba"
Matseta yayi a jikin bishiyar ya riƙota, cikin sigar magiya yace "please Gimbiyata, ko sau ɗaya ki nuna kin damu dani please"
Cikin tsiwa tace "to Jaririne kai? Ko goya ka zanyi?"
Kwantar da kansa yayi a kafaÉ—arta yace "to goyanin mana, ko daga nan zuwa É—akine"
"Eh ba shakka, ba kunya wai in goya ka, sakeni ko in cijeka yanzun nan"
Hanne ce ta fito daga É—akinsu, tana fitowa idonta ya sauka akan Yusuf da Widad dake tsaye a jikin bishiyar ceÉ—iya dake tsakar gidan, kamar zasu shige jikin juna.
Widad tayi murmushi tace "Ni banyi fushi ba ai, bakomai"
Saleh ya É—au waya ya kira Abbas, sedai har tayi ringing ta katse be É—aga ba, tana katsewar ne Abbas ya biyo kiran, Saleh ya É—aga tare da yin Sallama Abbas ya amsa, Saleh yace
"Malam Abbas, kayi gaba ko waiwaye baka yi, kana da labarin an sace amininka kuwa tare da 'yar gidan Daula?"
Abbas yace "ƙwarai kuwa na sani, dan nine ma na gayawa mahaifiyarsa"
Saleh yace "Wani tunani kayi akai kuwa?"
"wani tunani zanyi kuwa, maganinsa kenan ai, shegen shishshiginsa da rawar kai yaja masa, ni Allah ne ya dube ni, dani naso in maye gurbinsa da dani za'a ɗauke, Amma kuwa an karɓi files ɗin daga hannunsa?"
Shiru Saleh yayi sannan yace "basu karɓa ba tukuna, ni suke jira, har yanzu basu san cewar Yusuf ne jami'in tsaron ba, zancen da nake maka yanzu haka Yusuf sun tsere daga inda aka ɓoye su"
Abbas yace "haba dai, garin yaya akayi suka tsere? Kai Yusuf fa ba ƙaramin hatsabibi bane ba"
Saleh yace "babu wanda ya sani, kuma har suka gudu ba'a samu karɓar abun nan daga hannun yarinyar ba, yanzu maganar da nake maka, shi kansa Daulan an ɗauke shi a gadon Asibiti, babu wanda yasan inda yake"
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, garin yaya, yanzu shikenan munyi biyu babu, nifa ba wanda yake tuntuɓata yanzu tunda akamin transfer"
Saleh yace "karka damu, ina son ka saurareni da kyau, duk abunda ake ciki zan dinga sanar da kai, karka kusakura wani daga cikin su yayi yunƙurin haɗa kai da kai, dan yanzu gaba ɗaya kawunansu a rarrabe yake, duk wanda ya tuntuɓeka koya tambayeka wani abu game da wanda aka bawa binciken nan kace baka sani ba"
Abbas yace "to aini basu sanni ba, kai suka sani me zesa su nemeni?"
"Abbas mutane ne masu wayo matuƙa, yanzu haka a manyanka na gurin aiki wani ze iya bugun cikinka ya tambayeka wani abu, karka kuskura ka gaya wani, wani abu akan harkar nan, na gaya maka kansu ya rarrabu, wasu zasu iya zamewa suyi harkar nan babu mu, bayan wahalar da mukayi "
Abbas yace " bakomai na fahimce ka, Insha Allah babu wanda zeji wata magana daga bakina, dama kai ka jawoni cikin harkar "
Saleh yace " Good nagode "
Sukayi Sallama, Saleh ya jinjina kai yanzu ya sake jinjinawa Widad, lallai bata da laifi naƙin yadda da mutane, ƙir ƙiri Abbas na jikin Yusuf ne, amma saboda kuɗi yake masa zagon ƙasa, tabbas mutum abun tsoro ne, kuma da alama Abbas Soko ne, dan haka yi masa wayo ba wani abu bane me wahala.
Saleh yana son sake komawa gurinsu Widad, dan haka yana ta É—anyi musu siyayya.
Alhaji Musa ne ya kira shi a waya yace 'lallai yana son ganinsa a guest house É—insa'
Haka Saleh ya bar abunda yake yi ya tafi gidan Alhaji Musa.
Yaje ya tarar dashi a lambun dake gidan, suka gaisa Alhaji Musa yace "Saleh ina cikin damuwa fa"
"wace irin damuwa kuma ranka ya daÉ—e?"
"Na fuskanci Nurat tana ƙoƙarin fara yin shisshigi ga al'amuran Daula, gashi yanzu ina ɗari ɗari da su Haruna, ina tsoron Ayi Amfani da ita a cutar da ita koni, yanzu babban abunda ya sake bani mamaki be wuce yadda Daula yayi ɓatan dabo ba, ko kusa ko alama an rasa inda yake, zargina yana ƙara tabatta akan ana min maƙarƙashiya, kodai su Alhaji Haruna suke cuta ta suke al'amuran su suka ɗai, kokuma akwai wani a gefe daya ke harin abunda muke hari, ko kuma yasan siriinmu yake son temakawa Daula"
Saleh yayi ajiyar zuciya yace "banƙi ta taka ba, Amma ko waye wannan tabbas na jikin ku ne, amma abun da mamaki ace an nemi Daula ko sama ko ƙasa an rasa sekace wata takadda"
"Shine abunda ya É—auremin kai ai, ni yanzu gefe zan koma in nemawa kaina mafita, idan abun nan ya samu shikenan, in be samu ba shikenan, suma har yanzu da suka gudu babu wanda ya sake jin É—uriyarsu, dan haka ni inaga tunda babu wanda yasan inda Daula yake, zan fito takarar Senate ne kawai "
Da sauri Saleh ya kalle shi yace " Amma ta yaya kake tunanin mutane zasu yarda su zaɓeka? Bayan Daula ya riga ya ɓata siyasarka a idon duniya? "
Alhaji Musa yace " shiyasa nima na ƙuduri aniyar kota wane hali, sena Wulaƙanta Daula a idon duniya, sannan malamai zan shiga a rufemin bakin jama'a, akwai yarana da suke aiki a wasu daga kamfanunukan Daula, zamu haɗa kai dasu mu karkatar da wasu kuɗaɗe inyi amfani da su, niba kuɗin Daula ne sjka dameni ba, yadda zan Wulaƙanta shi in ɗaiɗaita shine ya dameni, amma ko yanzu na rage raɗaɗin dake zuciyata, kuma zan cigaba da bibiyarsa se naga babu inda ya rage wanda ze jingina yaji daɗi, sannan in dawo kan su Alhaji Munir"
Yadda Alhaji Musa ke maganar babu alamun tausayi ko imani a tare da shi, har zuciyarsa yake faÉ—ar wannan maganganun.
Saleh ya ɓoye duk mamakinsa, ya dinga ziga Alhaji Musa, Alhaji Musa ya kawo kuɗi ya bawa Saleh, Saleh a ransa yace "ka bada kuɗin da zanyiwa maƙiyan ka siyayya, kuma nima zancigaba da bibiyarku, ɗaya bayan ɗaya sena ɗau fansar cin amanata da kuka yi, da saɓa Yarjejeniyar da muka yi daku"
Widad gaba É—aya hirar da suka yi da Hindu ta tsaye mata a zuciya, ta tuna yadda haka siddan se É—an kasuwa yayiwa É—an siyasa kyauta motar miliyoyi, ko biliyoyin nairori, Amma al'ummar su suna tagayyara, da yunwa da rashin kyakkyawan mahalli.
Yusuf yaga gaba ɗaya Widad tayi wani iri, seta zauna tayi shiru tana tunani, dukda shima zuciyarsa ba daɗi, Amma sam baya son ganinta a damuwa dan haka yace "Ran gimbiyata ya daɗe meke damunki ne?"
Jiki a sanyaye tace "Abubuwa da yawa"
Yusuf yace "Kamar me? Ko har yanzu fushin kike dani"?
Jiki a matukar sanyaye ta bashi labarin hirar da suka yi da Hindu, daga ƙarshe tace "tabbas ƙaddarar data sameni na zuwa ƙauyen nan, ishara ce Allah ya nunamin, na rayu cikin gata wanda nake ganin babu wani abu da zan iya nema in rasa a rayuwata, ranar da kace min akwai mutanen da Naira ɗari take gagararsu, gani nake kawai ka faɗane dan ka rainamin hankali saboda a lokacin, abun da ke cikin asusun bankina ya ninka ɗari sau ɗari, bani da wata damuwa ko matsala, Amma ace a rayuwa akwai tarin 'ya' ya mata da suke zaune ba ilimi? Akwai tarin mutanen da suke rayuwa da gurɓataccen ruwan sha? Akwai tarin yara manyan gobe da rayuwarsu ta lalace saboda rashin gurin samun ilimi, Yoseef yaran masu kuɗi na Almubazzaranci da dukiya, da yawanmu bamu san yadda aka tara kuɗin ba... Kasa ƙarasawa tayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, wani irin ɓacin rai ke taso mata, yadda ake ɓarnar kuɗi gurin bukukuwan birthday dana Aure, da makamantan su.
Yusuf ya taso daga inda yake, yazo ya samu guri ya zauna kusa da ita yace "Widad baki ga komai ba, a yanzu haka a cikin ni'ima muke, a gidan megari muke a zaune, kuma gidansa da rufin Asiri, ya kike tunanin gidajen sauran talakawa da suke garin nan? Wanima abunda zasu cin ma babu, Widad talauci gaskiya ne, shiyasa Wulaƙanta mutane bashi da kyau "
Widad tace" tabbas wulaƙanta mutane bashi da kyau, nasan mutane dayawa sunamin kallon mace me izza da Wulaƙanta mutane, sedai...
Se kuma tayi shiru, Yusuf yace "sedai me?"
"Bakomai" ta bashi amsa tare da basar da zancen.
Da Asuba bayan Yusuf ya dawo daga sallar Asuba yazo ya tattara kwanuka zeje ya wanke, Widad tace "ka bari zan wanke"
Yusuf yace "No ki huta kawai, bari in wanke ai ba yawa kwanukan"
Widad tace "ce maka akayi ban iya wanke wanken bane?"
"Ni na isa ince gimbiya bata iya wanke wanke ba?"
Widad tace "gashi nan kuwa ka faÉ—a"
"A'a ni ban faÉ—a ba, taso muje muyi tare"
Widad ta tashi tabi Yusuf suka je suka wanke kwanukan tare, ta tattare duk kwanukan wanke wanken da'akayi fatali dasu na Abincin dare a tsakar gidan, ta haÉ—esu a guri É—aya, Yusuf yasa tsintsiya duk girman tsakar gidan yana sharewa, Widad ta dinga kallon ikon Allah, yadda Yusuf yake sarrafa tsintsiya kamar mace.
Widad tace "dan Allah dagaske kai ka É—aine a gidanku?"
Yusuf yace "Eh nikaÉ—ai ne Mamana ta haifa, ni nake mata aikin gida, shara, wanke_wanke hadda girki duk ta koyamin ni nake yi, idan ta tafi unguwa kafin ta dawo nayi komai"
Widad tace "shiyasa ka iya aiki sosai, nima nasan da tare na girma da Ammi na da duk na iya aiki, da baza'a dinga kallon ban iya komaiba"
Yusuf yazo kusa da ita ya tsaya, ya kalleta yace "karki damu gimbiyata, Insha Allah muna tare zaki iya komai kafin mu koma gida"
Widad ta kalle shi tace "dagaske har girki zaka koyamin? Nafa iya girki amma ba sosai ba"
Hannu yasa ya ɗago haɓarta yace "zaki iya komai insha Allah, duk zan koya miki, amma bana son taurin kai, dan nasan halinki"
"Nice me taurin kai?"
Yusuf yace "eh kina dashi amma kaÉ—an"
Murmushi Widad tayi tace "Ni dai in zaka koyamin zanyi duk abunda kake so"
Yusuf yace "dagaske?"
Widad ta jinjina masa kai, ya matso daf da ita yace "to shikenan, Yimin kiss a goshina ma ba'a baki ba, se in koya miki kunna risho yau"
Tureshi tayi tace "Baza'ai wannan É—inba"
Matseta yayi a jikin bishiyar ya riƙota, cikin sigar magiya yace "please Gimbiyata, ko sau ɗaya ki nuna kin damu dani please"
Cikin tsiwa tace "to Jaririne kai? Ko goya ka zanyi?"
Kwantar da kansa yayi a kafaÉ—arta yace "to goyanin mana, ko daga nan zuwa É—akine"
"Eh ba shakka, ba kunya wai in goya ka, sakeni ko in cijeka yanzun nan"
Hanne ce ta fito daga É—akinsu, tana fitowa idonta ya sauka akan Yusuf da Widad dake tsaye a jikin bishiyar ceÉ—iya dake tsakar gidan, kamar zasu shige jikin juna.