← Book details Akidata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 82

Sashe 80

Akidata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hanne ce tayi sallama da kayan Abinci a hannunta, sedai me taga Yusuf da Widad rungume da juna, take taji jikinta ya hau rawa, bata taɓa ganin hakan a zahiri ba, sannan ga wani kishi daya taso mata, take ta saki kwanon dake hannunta.

(Gobe insha Allah, zan kammala book 1,Ashirin ga wata insha Allah zan fara book 2&3,  tuni an fara biyan kuɗin, kuma zaku iya hanzarta biya ta wannan hanyar dake ƙasa "

Normal group duka littafi biyun  ₦300
Idan kuma ɗaya zaki siya  ₦200

VIP ₦ 500

Inkuma sena gama zaki sai complete document ₦700

Account Number
Aisha Adam
0009450228
Ja'iz Bank

Ko katin MTN banda VTU please
A turo evidence of payment ta 07063065680

Duk Wanda ya biya yayi min magana ta what's app number É—ina inyi adding É—insa a group É—in Nagode

Domin gyara sharhi ko shawara
Ayshercool

  _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED  (BANYI EDITING BA)

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 44_45

Yusuf ne yayi saurin ɗagowa ya kalli Hanne, Yusuf yace "Subhanallah, garin yaya kika ɓarar da Abinci?"

Widad kam ko motsawa ba tayi ba balle ta tashi daga jikin Yusuf.
  Cikin rawar jiki Hanne tace  "Tuntuɓe nayi shine ya zube, bari in samo in kwashe"
Ta juya ta fita da sauri, tana fita tsakar gida Gwaggo ta kalleta tace "ke meye haka, ba dai Abincin da nace ki kaiwa mara lafiyan kika zubar ba?"

Cikin inda inda tace "Amm.. Mm... Tuntuɓe nayi shine ya zube"

A fusace Gwaggo tace "kekam kamar mara hankali wani lokacin, kije ki kai Abinci kawai seki zubar dan shirme"

Hanne ba tace komai ba ta tafi ta ɗau tsintsiya da abun kwashe shara ta tafi gyara inda ta ɓata musu, cike da zullumin me zata je ta sake tararwa.

Gwaggo tace "Hindu tashi ki duba sauran kunu a É—akina ki kai musu ba'a bar mara lafiya da Yunwa ba"

Sukam Maƙota da suka rako Yusuf ne suka dinga jinjina rashin ta ido irin na Widad, a gabansu ba kunya taje ta rungume mijinta.

Wani da'ake kira da Lado me Jakai yace "to ai kunsan su ba namu ne na nan ba, jama'ar birni ne baku ga matar tasa bama kamar balarabiya, su sun saba irin wannan bakomai ne ba"

ÆŠayan da'ake cewa Liti yace "Aradu amma ai kunya wani abuce, tunda nasan duk abu Hausawa ne"

Lado yace "ku kuga haka, su a gurinsu ba wani abun bane ba"

Liti yace "Sumi sumi dashi haka, Amma ta rungume shi ya wani basar abunsa, memakon ma ya É—anyi mata tsawa ya hanata"

Wani me shekaru a cikin su yace "Kai waye ya gaya maka suna hantarar matansu, lallaɓasu suke yi, ni wallahi birgeni ma suka yi"

Kwashewa sukayi da Dariya gaba ɗayansu, harda ƙyaƙyacewa.

Hindu tayi Sallama, da kofin kunu tace "gashi inji Gwaggo, tace dan Allah kuyi haƙuri Hanne ta zubar da Abincin"

Yusuf yace "bakomai Hindatu hakanma mungode"

Hindu tace  "Amarya yau za'a ci Abinci, tunda me gidan ya dawo"

Yusuf yace "Ai naga alama bata cin Abinci ta rame sosai"

Hindu tace  "bata ci, Gwaggo taita fama da ita sedai tayi ta kuka, ko bacci bata iyayi"

Widad ta yatsine baki tace "Akanme zanƙi bacci, in kasa cin Abinci toni ƙiba ma nayi, ci nake in ƙoshi"

Hindu tayi dariya tace "bari a kirawo Gwaggo a tambaye ta"

Sukayi dariya, Hindu tayi waje, Yusuf ya kalli Widad yace "bani kunun insha dan inajin Yunwa"

Widad ta miƙe ta ɗakko kofin kunu, tazo ta zauna tana bawa Yusuf, Saleh ne yayi Sallama ya shigo ɗakinsu.

Kallon Widad yayi yai murmushi yace "Allah me iko, Allah ba yadda be iyaba, wai Gimbiyar Daula ce ke bawa direbanta Abinci a baki, abun da mamaki"

Banza tayi masa ta cigaba da bawa Yusuf kunu, Yusuf yace "Saleh ƙaraso ka zauna mana"

Saleh yace "to bari in ƙaraso, ina fatan hankalinki ya kwanta ban gudu dashi ba, gashi na dawo miki da shi, kuma Alhamdilillah jikinsa yayi kyau"

Shiru ta kuma yi bata ce komai ba, Yusuf yace "Ana magana fa"

Widad tace "me zance?"

Saleh yace "base kince komai ba kam, Malaria me ƙarfi da typhoid ne suka kama Yusuf, sannan ulcer na damunsa, ga rashin sabo da wasu abubuwa da yake yi, wanda be saba ba, dan haka shine damuwa gajiya da pressure ga kuma zazzaɓi gaba ɗaya suka dameshi, amma Alhamdilillah mun samu an ceto miki shi, yasamu sauƙi Alhamdilillah, na samo Net guda ɗaya, yace min ba guri ɗaya muke kwana ba, dan haka ga guda biyu nan ke ɗaya shi ɗaya, likita yace 'ya dena zama da yunwa, ya dena barin sauro yana cizonsa, sannan a kula ya shanye magungunansa"

Widad tace "Aishi zaka gayawa bani ba, tunda ze iya kula da kansa ko"

Mamkine ya kama Saleh, ya tuna yadda ta dinga kuka ranar da zasu tafi da Yusuf, amma yanzu tana faÉ—ar wata magana daban, shi kansa Yusuf beji daÉ—in hakan ba, amma ya basar.

Saleh yace "koma dai menene, Zan zauna zuwa jibi in Allah ya kaimu zan koma, nayi muku siyayya wajen gobe in Allah ya kaimu za'a kawo muku"

Yusuf yace "Mungode sosai da É—awainiyar da kake mana, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya biya ka"

Saleh yace  "Ameen"

Ita kuwa madigar, miƙewa tayi tai waje abunta, ba tare da ta sake tanka musu ba.

Amal na kwance akan gadonta tayi shiru sosai take tunani, tayi zurfi sosai a tunani, Mummy ta shigo É—aki Amal ta tarar a kwance tayi shiru tana ta tunani"

Mummy tace "ke meye haka? Tunanin me kike yi? "

Amal ta ɗan tura baki tace "lafiya ƙalau Mummy"

"Amma kika zauna kika yi shiru haka? Kina ƙarama dake kike tunani haka"

"Mummy ina É—an zancen zuci ne kawai"

"to idan waccan uwar baccin ta tashi ki gaya mata zan fita, ni na rasa gane kan wannan baccin banzan dat take yi sekace wata kasa"

Ita dai Amal bata gayawa Mummy abunda Ramlan keyi ba.

Bayan fitar Mummy kwanciya Amal ta sake yi tana cigaba da tunani, kuma ba tunanin kowa take ba face Yusuf, tun tana dannewa yanzu abu yavfara gagara, bata iya ɓoyewa sam, Bata iya cin Abinci ba tayi zaton ƙaunar Yusuf haka tayi mat wannan mugun kamun ba, gaba ɗaya yanzu haushin samarin ta take ji, gani take duk cikinsu Yusuf yafi su komai dukda Kasancewarsa talaka, amma ya haɗu gashi nutsatse babu Hayaniya a tare da shi, ji tagi inama a sako Yusuf a riƙe Widad, dama itake hana ta rawar gaban hantsi, dan ta rasa wace irin Alaƙace ke tsakanin su, Widad bata da yadda kamar me, bata yadda kowa ya raɓe ta ba, amma ta yadda da Yusuf ya shiga jikinta sosai da sosai, Yusuf yasan abubuwan dasu da suke zaune da ita basu sani ba.

"Ke Amal! Tun É—azu nake miki magana amma se kace wata kurma, kinmin shiru"

Firgigit Amal ta kalli Ramlah, tayi ajiyar zuciya tace "Meye nayi min ihu kuma?"

"na dole inyi miki ihu ba, tun É—azu nake kanki ina magana amma kinyi shiru"

Amal ta miƙe zaune ta kalli Ramlah tace   "ban san kin shigo abane, dana san kin shigo ai zanyi responding"

"Wai nikam wane irin tunani haka kike yi?"

"Ramlah tunanin komai ma inayi, Abubuwa da yawa sun dameni, Amma Ramlah jiya fa maye kike kika dawo"

"Maye kuma?"

"Eh mana, wallahi jiya a buge kika dawo gidan nan, Mummy kuma a ƙule take dake, fitar da kikayi da Fahad"

Ramlah ta ɗan ɓata rai tace "ba wani maye da nake, na gaji ne kawai, sannan me Fahad ɗin kuma yayi?"

Amal tace "Eh to, kin san sunyi faÉ—a da É—an uwanta akan belin Yaya Anwar, shiyasa"

"to kuma shine seya shafi Fahad, laifin meyayi? Kuma shima bakiga yadda yake ƙoƙari akan lamarin ba, amma kin san halin babansu da kafiya"

Amal tace "wani tabacci kike da shi na yana ƙoƙarin nan, nifa kallon Fahad ɗin nan kawai nake, bakin maƙaryata ne dashi"

Ramlah tace "zaki fara ko? Karki kusakura kici masa mutunci"

Amal tace  "ke niba wannan ba, nifa naji tana cewa za'ayi uwar watsi idan ba'a fito mata da Yaya Anwar ba, karta yi wani abu daza'a zo ana da nasani daga baya"

Ramlah tace "kuma fa hakane, kin san bata iya fushi ba, bari inje É—akinta in sameta"

Amal tace "to ai ta fita"

"ta tafi ina?"

"Nima ban sani ba, ni dai tacemin zata fita"

Ramlah tace "Shikenan, bari inje kitchen in samu ɗan abunda zanci, da yamma zanje gurin wani birthday na 'yar gidan IG na ƙasa, na tura a ɗakkomin wata sabuwar motar megidan nan daga kamfani, da ita zanje, kin san gurine na manyan yara fa"

Amal tace "Mhmm yakamata kam"

"waini meke damunki ne Amal, bakya walwala fa"

"Ramlah wace walwala zanyi? Yaya Anwar a rufe, hankalin Mummy yaƙi kwanciya, ga uwa uba wallahi Ramlah Ji nake kamar inyi me saboda rashin Yusuf, na shiga damuwa wallahi ko bacci na kwanta yanzu mafarkinsa nake yi, na rasa inda zan saka raina, tun ina iya dannewa yanzu na kasa "

Wani uban dogon tsaki Ramlah taja tace " Aikin banza, shine zaki kashe kanki saboda wannan jakin"

"Karki sake kiransa da Jaki, Inda wanda za'a kira Jaki to tabbas Fahad ne, dan kunnuwansa ma irin na jakaine ga ƙaryar tsiya".

Haka abun nasa ya koma faɗa, ƙarshe sukayi baran Baran.
Chapter 80 · 0% Book details