Sashe 33
Sakar Makafi Part 2 Complete Hausa Novel · about 11 min read
By
*GARKUWAR MARUBUUTA**SAƘAR MAKAFI*
Page 58
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
Jin yadda yaja wani irin fusataccen tsaki mai tsawo ya zira wayar cikin aljihunsa tare da rumtse idanunsa.
Suna shiga gidan suka hangi motar Salim da yayi parking yanzu a tare suka fito shi da Salmanshi da tsayuwa yi musu girki yasa bata zo da wuriba.
Ido suka zubawa motar har saida sukayi parking suka fito, da sassarfa Salma ta nufi Fariyda da itama wurinta ta nufa rungume juna sukayi cikin jin dadi.
Shi kuwa Mahmoud Hafiz da ya buɗe masa ƙofa yayi saurin amsar su Zaid da Zaitoon ya rungume duka ya juya ya nufi cikin gida da sauri.
Da ido yabi shi jin yana faɗi.
“Ummi Goggo Dada sun iso”.
A hankali ya fito cikin motar yana kallon sauyin gyara da akayi wa gidan musamman pentin da aka sabunta.
Side hug Salim yayi masa.
Da sauri ya ɗan saki Mahmoud ɗin tare da zaro wayarsa data fara Vibrating.
“idaya”. Shine sunan da yake yawo a kan fuskar wayar da sauri ya kalli Mahmoud ɗin jin yadda ya sauƙe numfashi, ido ya zuba mishi cike da tuhuma ganin Idaya ke kiransa a hankali Salim ya katse kiran tare da maida wayar cikin aljihunsa.
Bayan Mahmoud ɗin yabi wanda tunu Salam da Fariyda sun shiga cikin gida.
Sulaiman dake gabansu ne ya buɗe ƙofar parlour Ummi suka shigo.
Tib parlour yake cike da su Saddiqa, Rashida, Aisha, Adda Nana, Khadija, Zainab, Humaira, Raihana, Aunty Sadiya, Amina Hafiza Samira da Jidda Abida matar Yah Ahmad da itama sun zo Kano. Da sauri ya raɓa gefe zai wuce parlour Abba saboda yadda parlour ke cike duk sun kacame da sowa Ummi na rungume da Fariyda Goggo Dada na rungume da Zaid, Aunty Saddiqa kuwa dasu Rashida Ummi dake rungume da Fariyda suka sa a tsakiyarsu cikin farin ciki.
Salim yasa hannunsa ya kamo hannun Salma tare da ɗan ɗaga mata gira.
Sulaiman kuwa gafen Ummu ya zauna.
Shi kuwa Mahmoud a hankali ya raɓa gefen bayan kujerun zai wuce parlour Abba sai kuma ya tsaya jin an rungumeshi ta baya, yasan mutum ɗaya ce zata mishi haka kab duniya haka yasa ya ɗan juyo a hankali, shima rungumeta yayi irin rungumar gefe ɗaya nan cikin tarin shaƙuwar jini Aunty Amina tace.
"Yah Salam Mahmoud wai dan Allah kaida Fariyda waya fi kyau ne kam? Kunga yadda kuka zama kuwa kamar wasu yayan ruwa”. Fuska ya tsuke saboda ganin ta jawo hankalin mutanen parlour duka kansu a hankali yace.
"Wannan ai zagine ƴaƴan ruwa kuma aljanufa kenan Maman Hafiz”. Dariya Goggo Dada tayi tare da cewa.
"Dama munyi kewar faɗanka”. Ta ƙare maganar tana miƙa masa hannunta.
Kanshi ya ɗan sunkuyar ya matso kusa da ita ya miƙa mata hannun musabaha sukayi da ita kamar yadda sukeyi duk sanda ya dawo daga tafiya.
Ganin ya shigo cikin parlour ne yasa su Aunty Saddiqa ja da baya suka koma gefen kaɗan.
Ummi dake rungume da Fariyda tana ɗan shafa bayanta da jijjigata ganin yadda take kwallon Farin ciki. Ido ta zuba mishi ta kasa faɗin komai, ganin yadda take kallonsa da miƙo masa hannune yasa shi matsowa kusa da ita, hannun ta bashi suka gaisa sai kuma ta jawoshi jikinta gefen damanta ta rungumeshi tare da shafa bayansa yayinda Fariyda ke gefen hagunta haka yasa su fuskantar juna, yadda take lumsh ido hawaye na ɗan gamgaro ya ɗan ƙalla cikin sanyi shima ya lumshe nasa idon tare da ɗan hura mata sassayar iskar bakinshi kan fuskarta haka yasa ta buɗe ido a hankali, ido huɗu sukayi dashi, da sauri ta maida idonta ta rufe dan haka nan takejin idonsa yafi ƙarfin nata, shi kuwa Mahmoud kauda idonsa yayi jin Ummi na cewa.
“Yau sak Aminullah ka dawo da kasa Jallabiya sai nake ganinku ku duka biyu a ganganjikin ka Babana nayi kewarka”. Baki Amina ta tura tare da cewa.
"Nifa na lura kamar ba wani sona akeba, ji Ummi fa harda rungumarshi ƙato dashi da mata da yara”. Goggo Dada ne ta rungume Amina tare da cewa.
“Ai kuwa bamu da kamarki”. A hankali ya gyara zamansa yana kallon Adda Nana da Aunty Saddiqa dake ce mai.
“Appiyn Zaid barka da dawowa ya Zaid da jiki”. Fuska ba yabo ba fallasa yace. "Alhamdulillah ya warke”. Sai kuma ya ɗan kalli su Aunty Rashida da Aisha da dai duk sauran da suka ɗaga mishi gaisuwa ba tare da ya kuma kallonsu ba ya amsa fuska a ɗan sake
Sai kuma ya kalli Ummi dake cewa.
"Fariyda maza ku isa ciki, kuje Abbanku na jiran isarku shiyasa yau bai zauna a masallacin jumma'a ba har akayi la'asar ya dawo dan son ganinku”. Kai Fariyda ta gyaɗa tare da janye jikinta hannu Ummi tasa tana share mata ƙwalan tace.
"Ku ɗauki yaranku ku isa dasu, a tsaida hawayen nan kuma haka ya isa in ba so kike kisa Umminki ma ƙwalla ba”. Kai ta jinjina tana share ƙwalla , shi kuwa Mahmoud Juyawa yayi ya karɓi Zaid ita kuwa Fariyda Zaitoon ta amsa, a jere suka nufi parlour Abba Sulaiman da Salim na biye dasu a baya.
Murmushin Rashida tayi tare da cewa.
"Gayu sun shiga uku kuna ganin wata shiga ta alfarma Fariyda da Mahmoud abu maroon yana masifar musu kyau, ga yadda suke tamkar taurari, yaransu ma sun zama tamkar su shi Zaid sak Mahmoud ita Zaitoon sak Fariyda.”
Aunty Saddiqa ne tace.
“Sosai ma kam shigar tasu ma kaɗai zata nuna maka one Family ne mai tafe da kwanciyar hankali”. Amina ne tace.
“Ai dai kam naga itama Fariyda ta fara sa abu maroon da tafi son blue shi kuwa Mahmoud dama kalansa ne Maroon da fari in kin ganshi da Sky blue to zaɓin Yah Amin ne”. Ta ƙare maganar tana nufar parlour Abba da sauri Jidda ta mara mata baya.
Zaune ta samesu gaban Abba dake rungume dasu Zaid gefen Sulaiman ta zauna tare da kallon Yayan baban nata tace.
“Abba Barka da rana”. Yana ƙallonta yace.
“Barka dai Jidda kema kin zo tarɓar yaranki kenan”. Murmushin mai tafe da manufa tayi tace.
“Eh Abba nazo in ga ɗan uwana dan nayi kewar faɗansa”. Sulaiman yace.
“Kuma ba abinda kika kawo masa”. Da sauri ta miƙe tana faɗin.
“Tab ai kuwa ni na kawo masa yau tun asubafa ina kitchen saboda yi masa girki”. Ta ƙare maganar tana ɗauko basket ɗin da tazo dashi.
Tare suka shigo dasu Goggo Dada da Ummi tana faɗin.
“Amina kun bar su Saddiqa su kaɗai fa a parlour kije wurinsu”. Da sauri Amina ta miƙe sai kuma ta ɗan rusuna jin Abba na cewa.
“A'a su shigo mana iso dasu nan Amina dama ban gaisa da suba ai kice maza su shigo”. Da sauri Amina tace to kana ta fito Parlour ta kirasu.
A gaban Abba duk suka zauna a tsakiyar tamfatsetsen Parlour nasa da zai iya ɗaukan mutum sama da 60 haka yasa ba takura suka zauna suka fara gaidashi ɗaya bayan ɗaya cikin mmki suke amsawa da lfy sabida ganin yadda yake kiran sunansu harma da tambayar su mazanzu da kiran sunansu shaidar yasan su farin sani murmushi Saddiqa tayi ji yana faɗin.
"A'a Saddiqa har yanzu baki koma bane? Me ya ajiyeki ina shi Usman din kika barosa shi kaɗai a gida”. Kai ta gyaɗa cikin girmamawa tace.
“Abba ai baya nanne shiyasa kuma ina jiran auren Raihana ne”. Cikin girma yace.
“Auren da saura kusan wata ɗaya, to yaranki kin zo da sune ko kin barsu acan”. Tana ƙasa da kanta tace. “Suna wurin maman babansu, amman in kunce in koma zan koma Abba”. Kai ya jujjya tare da cewa.
“Ba komai tunda da yardar mijinki ne Saddiqa Allah yayi muku al'barka”.
Amin suka amsa suna kallo Jidda da ta matso gaban Mahmoud da basken ɗin tare da fidda kulolin ta zaro plate tana faɗin. "Ɗan uwa me zan sa maka”. Kauda kai yayi tamkar baya wurin.
Goggo Dada dasu Ummi kuwa shi suka zuba wa ido.
Hakama su Saddiqa duka, Rashida kuwa Fariyda ta zuba wa ido tana son ganin me zatayi ganin wata na kwarkwasa a gaban mijinta, ganin ko ta inda suke Fariyda bata kallabane yasa Rashida ɗan tureta tare da nuna mata Mahmoud ɗin da alamun ke ki kula da mijinki fa.
Kai ta kauda tare da ƙarɓa ɗan Aunty Rashida tana faɗin.
“Zo nan ɗan CS ya girmafa”. A ranta kuma tace, uhummm in dai wannan ne ku zuba ido kusha kallon tijarar da zai fesa mata yar masu nataccen zuciya da naci kamar mayya.
Kusan duk parlour kallansu suka maida kan Jidda dake cewa.
“Babe in zuba ma papper meat ne?”. Wani irin dogon tsaki yaja wanda yasa suka ɗan kalleshi har da Abba shi ya zubawa ido.
Salim kuwa kai ya jinnina cikin alamun madalla zaiyi maganinki.
“Babe in bazakaci wannan ba to ka gaya min me kake so in dafa maka”. Wani irin juyowa yayi ya watsa mata kallon da yasa Salim murmurshi ita kuwa kai ta sunkuyar jin yana faɗin.
“Kika ƙara cemin Babe sai na sumar dake, kaji yar iskar yarinya da raini wai nine ma babe nine ma babe dinki, nifa ba'a min gwaninta, dan ni tsanar mutuma nakeyi in yana min iyayi ba burgeni zakiyi ba”. Sai kuma duk suka kalli Fariyda data taɓe baki gami da sakin murmushi da sautinsa ya subce mata wai.
“shifa ba'a mishi gwaninta" wlh kalmar dariya take bata ganin rashin mutuncinsa a fili yake nuna shifa ba'a iya masa. Ita kuwa Jidda cikin kashe zuciya tace.
“To naji Yah Mahmoud me zan maka”. Mari Salim ya watsa mata tare da cewa.
“Ke fice daga nan”.
Da sauri Abba ya dakatar dasu da yin gyaran murya.
“Kai Salim Kar in sake ganin ka taɓa mace da sunan mari ai wannan zalumci ma bayyani ya tana mace zaku hantareta kai kuma ka ƙara da mari, mace fa abar tausayice sabida rauninta, bana iya jurar ganin an tauye mace. Yi haƙuri Jidda kin san yayun naki”.
Da ido Saddiqa ta rakata lokacin da Goggo Dada taja hannunta suka fita, ita har ga Allah ta ɗauka Jidda ce babba kam Salim sabida habakar jikinta sai yanzu da Abba ya faɗane ta ɗan lura da jikin fuku-fuku ne. Fitan sune yasa Abba kallon Mahmoud yace.
“To kai kuje kuci abinci ko”. Da sauri Salim yace.
“Bari in kawo maka abincin Madam yau tun safe nasa tayi maka girki kaci abincin gidana”. A hankali yace.
“Mami ta bani abinci ai, Hafiz ka ɗauko mana shi yana mota”.
Cikin mmki Fariyda da Amina da Ummi ke kallonsa.
Su kuwa su Saddiqa murmushi jin dadin yadda yayiwa Jidda sukayi har da Salma duk suka fito parlour.
Ya rage daga shi sai Ummi Amina Fariyda dasu Zaid da Sulaiman da Salim.
“Kayi wanka ne?”. Sulaiman ya tambaya.
“Eh nayi”. Ya bashi amsa a taƙaice. Fariyda da ta zauna don son ganin gudun ruwansa ne ta kalli Hafiz da ya shigo da trayn da Mami ta shirya kulolin.
A gabanshi ya ajiye, sai kuma ya fara ɗauko tray da Mamanshi ta shirya mishi abinci duk ya ajiye a tsakiyar parlour. Amina ce ta fara sawa Sulaiman da Salim da Hafiz ɗin da Huzaifa.
“Wanne zan zuba maka”. Ta tambayi Mahmoud ɗin tana kallonsa tare da buɗe wormes ɗin kan tryan Mami da kuma nata ɗin duka.
Kular farko na trayn mamaki wanda yake ɗauke da dandarerun naman rago ne mai kyau da ƙamshi sai turiri yakeyi ya ɗan nuna mata.
Ita ma Fariyda har yanzu shi take kallo ta gefen idan, ɗaya kular ta buɗe couscous ne mai kyau wanda yayi sar-sar sai karamar kulan vegetables soup ne wanda yake wadace da kifi. Cikin mmki take kallonsa jin yace.
“Samin shi”. Abba ma da mmani yake kallonsa hakama Amina da Ummi da Goggo Dada data shigo tare da Jidda. Sulaiman kam ido kawai ya zuba mishi.
Sa mishi Amina tayi couscous a plate ta sa ɗan vegetables soup ɗin a bowl ɗin plate ɗin Mami, sai ta kuma daukan ɗaya bowl ɗin ta sa mishi danderun tare da sa mishi spoon gyara zamansa yayi yana mai ɗaukar spoon ɗin ya kalli Abba yace.
“Abba yau abincin Malam Mami ta bani shiyasa zanci dan malam yace in naci zaiji daɗi naci abincinsa”. Ya ƙare maganar yana kai spoon ɗin daya yago tattausar tsokar danderun bakinsa.
Kusan duk a tare suka kalli juna ita, kam Fariyda ɗan baki ta buɗe cikin tsananin mamaki, sai kuma kawai ta miƙe tsaye jin Amina na cewa.
“Abba me zan saka maka?”. Yana murmushi yace. "Nima ɗin Abincin gidan Malam Ibrahim ɗin zanci”. Hakan da tajine yasata murmushi tare da juyawa zata fita.
“A'a Fariyda zo nan ki zauna kema muci abinci ko”. Cikin kunya da girmamawa tace.
“Abba Aunty Rashida ta kawo min ɗanwake shi zanje inci”. Da sauri Amina tace.
“Muje nima ai na kawo miki waina kuma sai kinci”. Ummi na binsu a baya tace.
“Lallai ma kam naji Salma na cewa ta miki dambu, yau to me zakici.
Daga nan duk suka fita.
A parlour ta samesu nan suka wuni zaune sukayi ta ciye-ciyen gayu da hirarsu ta yaushe gamo sai salla ke tada su, sai wuraren ƙarfe goma na dare suka watse ko wacce ta koma gidanta bayan Amina ta raba musu tsarabar da Mahmoud yayi.
Ita kuwa Amina sai karfe sha ɗaya suka tafi da Hafiz.
Tuni Fariyda tayi bacci a ɗakin Goggo Dada.
Washe gari da sassafe ya Yah Mujahid ya.......
*GARKUWAR MARUBUUTA**SAƘAR MAKAFI*
Page 58
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
Jin yadda yaja wani irin fusataccen tsaki mai tsawo ya zira wayar cikin aljihunsa tare da rumtse idanunsa.
Suna shiga gidan suka hangi motar Salim da yayi parking yanzu a tare suka fito shi da Salmanshi da tsayuwa yi musu girki yasa bata zo da wuriba.
Ido suka zubawa motar har saida sukayi parking suka fito, da sassarfa Salma ta nufi Fariyda da itama wurinta ta nufa rungume juna sukayi cikin jin dadi.
Shi kuwa Mahmoud Hafiz da ya buɗe masa ƙofa yayi saurin amsar su Zaid da Zaitoon ya rungume duka ya juya ya nufi cikin gida da sauri.
Da ido yabi shi jin yana faɗi.
“Ummi Goggo Dada sun iso”.
A hankali ya fito cikin motar yana kallon sauyin gyara da akayi wa gidan musamman pentin da aka sabunta.
Side hug Salim yayi masa.
Da sauri ya ɗan saki Mahmoud ɗin tare da zaro wayarsa data fara Vibrating.
“idaya”. Shine sunan da yake yawo a kan fuskar wayar da sauri ya kalli Mahmoud ɗin jin yadda ya sauƙe numfashi, ido ya zuba mishi cike da tuhuma ganin Idaya ke kiransa a hankali Salim ya katse kiran tare da maida wayar cikin aljihunsa.
Bayan Mahmoud ɗin yabi wanda tunu Salam da Fariyda sun shiga cikin gida.
Sulaiman dake gabansu ne ya buɗe ƙofar parlour Ummi suka shigo.
Tib parlour yake cike da su Saddiqa, Rashida, Aisha, Adda Nana, Khadija, Zainab, Humaira, Raihana, Aunty Sadiya, Amina Hafiza Samira da Jidda Abida matar Yah Ahmad da itama sun zo Kano. Da sauri ya raɓa gefe zai wuce parlour Abba saboda yadda parlour ke cike duk sun kacame da sowa Ummi na rungume da Fariyda Goggo Dada na rungume da Zaid, Aunty Saddiqa kuwa dasu Rashida Ummi dake rungume da Fariyda suka sa a tsakiyarsu cikin farin ciki.
Salim yasa hannunsa ya kamo hannun Salma tare da ɗan ɗaga mata gira.
Sulaiman kuwa gafen Ummu ya zauna.
Shi kuwa Mahmoud a hankali ya raɓa gefen bayan kujerun zai wuce parlour Abba sai kuma ya tsaya jin an rungumeshi ta baya, yasan mutum ɗaya ce zata mishi haka kab duniya haka yasa ya ɗan juyo a hankali, shima rungumeta yayi irin rungumar gefe ɗaya nan cikin tarin shaƙuwar jini Aunty Amina tace.
"Yah Salam Mahmoud wai dan Allah kaida Fariyda waya fi kyau ne kam? Kunga yadda kuka zama kuwa kamar wasu yayan ruwa”. Fuska ya tsuke saboda ganin ta jawo hankalin mutanen parlour duka kansu a hankali yace.
"Wannan ai zagine ƴaƴan ruwa kuma aljanufa kenan Maman Hafiz”. Dariya Goggo Dada tayi tare da cewa.
"Dama munyi kewar faɗanka”. Ta ƙare maganar tana miƙa masa hannunta.
Kanshi ya ɗan sunkuyar ya matso kusa da ita ya miƙa mata hannun musabaha sukayi da ita kamar yadda sukeyi duk sanda ya dawo daga tafiya.
Ganin ya shigo cikin parlour ne yasa su Aunty Saddiqa ja da baya suka koma gefen kaɗan.
Ummi dake rungume da Fariyda tana ɗan shafa bayanta da jijjigata ganin yadda take kwallon Farin ciki. Ido ta zuba mishi ta kasa faɗin komai, ganin yadda take kallonsa da miƙo masa hannune yasa shi matsowa kusa da ita, hannun ta bashi suka gaisa sai kuma ta jawoshi jikinta gefen damanta ta rungumeshi tare da shafa bayansa yayinda Fariyda ke gefen hagunta haka yasa su fuskantar juna, yadda take lumsh ido hawaye na ɗan gamgaro ya ɗan ƙalla cikin sanyi shima ya lumshe nasa idon tare da ɗan hura mata sassayar iskar bakinshi kan fuskarta haka yasa ta buɗe ido a hankali, ido huɗu sukayi dashi, da sauri ta maida idonta ta rufe dan haka nan takejin idonsa yafi ƙarfin nata, shi kuwa Mahmoud kauda idonsa yayi jin Ummi na cewa.
“Yau sak Aminullah ka dawo da kasa Jallabiya sai nake ganinku ku duka biyu a ganganjikin ka Babana nayi kewarka”. Baki Amina ta tura tare da cewa.
"Nifa na lura kamar ba wani sona akeba, ji Ummi fa harda rungumarshi ƙato dashi da mata da yara”. Goggo Dada ne ta rungume Amina tare da cewa.
“Ai kuwa bamu da kamarki”. A hankali ya gyara zamansa yana kallon Adda Nana da Aunty Saddiqa dake ce mai.
“Appiyn Zaid barka da dawowa ya Zaid da jiki”. Fuska ba yabo ba fallasa yace. "Alhamdulillah ya warke”. Sai kuma ya ɗan kalli su Aunty Rashida da Aisha da dai duk sauran da suka ɗaga mishi gaisuwa ba tare da ya kuma kallonsu ba ya amsa fuska a ɗan sake
Sai kuma ya kalli Ummi dake cewa.
"Fariyda maza ku isa ciki, kuje Abbanku na jiran isarku shiyasa yau bai zauna a masallacin jumma'a ba har akayi la'asar ya dawo dan son ganinku”. Kai Fariyda ta gyaɗa tare da janye jikinta hannu Ummi tasa tana share mata ƙwalan tace.
"Ku ɗauki yaranku ku isa dasu, a tsaida hawayen nan kuma haka ya isa in ba so kike kisa Umminki ma ƙwalla ba”. Kai ta jinjina tana share ƙwalla , shi kuwa Mahmoud Juyawa yayi ya karɓi Zaid ita kuwa Fariyda Zaitoon ta amsa, a jere suka nufi parlour Abba Sulaiman da Salim na biye dasu a baya.
Murmushin Rashida tayi tare da cewa.
"Gayu sun shiga uku kuna ganin wata shiga ta alfarma Fariyda da Mahmoud abu maroon yana masifar musu kyau, ga yadda suke tamkar taurari, yaransu ma sun zama tamkar su shi Zaid sak Mahmoud ita Zaitoon sak Fariyda.”
Aunty Saddiqa ne tace.
“Sosai ma kam shigar tasu ma kaɗai zata nuna maka one Family ne mai tafe da kwanciyar hankali”. Amina ne tace.
“Ai dai kam naga itama Fariyda ta fara sa abu maroon da tafi son blue shi kuwa Mahmoud dama kalansa ne Maroon da fari in kin ganshi da Sky blue to zaɓin Yah Amin ne”. Ta ƙare maganar tana nufar parlour Abba da sauri Jidda ta mara mata baya.
Zaune ta samesu gaban Abba dake rungume dasu Zaid gefen Sulaiman ta zauna tare da kallon Yayan baban nata tace.
“Abba Barka da rana”. Yana ƙallonta yace.
“Barka dai Jidda kema kin zo tarɓar yaranki kenan”. Murmushin mai tafe da manufa tayi tace.
“Eh Abba nazo in ga ɗan uwana dan nayi kewar faɗansa”. Sulaiman yace.
“Kuma ba abinda kika kawo masa”. Da sauri ta miƙe tana faɗin.
“Tab ai kuwa ni na kawo masa yau tun asubafa ina kitchen saboda yi masa girki”. Ta ƙare maganar tana ɗauko basket ɗin da tazo dashi.
Tare suka shigo dasu Goggo Dada da Ummi tana faɗin.
“Amina kun bar su Saddiqa su kaɗai fa a parlour kije wurinsu”. Da sauri Amina ta miƙe sai kuma ta ɗan rusuna jin Abba na cewa.
“A'a su shigo mana iso dasu nan Amina dama ban gaisa da suba ai kice maza su shigo”. Da sauri Amina tace to kana ta fito Parlour ta kirasu.
A gaban Abba duk suka zauna a tsakiyar tamfatsetsen Parlour nasa da zai iya ɗaukan mutum sama da 60 haka yasa ba takura suka zauna suka fara gaidashi ɗaya bayan ɗaya cikin mmki suke amsawa da lfy sabida ganin yadda yake kiran sunansu harma da tambayar su mazanzu da kiran sunansu shaidar yasan su farin sani murmushi Saddiqa tayi ji yana faɗin.
"A'a Saddiqa har yanzu baki koma bane? Me ya ajiyeki ina shi Usman din kika barosa shi kaɗai a gida”. Kai ta gyaɗa cikin girmamawa tace.
“Abba ai baya nanne shiyasa kuma ina jiran auren Raihana ne”. Cikin girma yace.
“Auren da saura kusan wata ɗaya, to yaranki kin zo da sune ko kin barsu acan”. Tana ƙasa da kanta tace. “Suna wurin maman babansu, amman in kunce in koma zan koma Abba”. Kai ya jujjya tare da cewa.
“Ba komai tunda da yardar mijinki ne Saddiqa Allah yayi muku al'barka”.
Amin suka amsa suna kallo Jidda da ta matso gaban Mahmoud da basken ɗin tare da fidda kulolin ta zaro plate tana faɗin. "Ɗan uwa me zan sa maka”. Kauda kai yayi tamkar baya wurin.
Goggo Dada dasu Ummi kuwa shi suka zuba wa ido.
Hakama su Saddiqa duka, Rashida kuwa Fariyda ta zuba wa ido tana son ganin me zatayi ganin wata na kwarkwasa a gaban mijinta, ganin ko ta inda suke Fariyda bata kallabane yasa Rashida ɗan tureta tare da nuna mata Mahmoud ɗin da alamun ke ki kula da mijinki fa.
Kai ta kauda tare da ƙarɓa ɗan Aunty Rashida tana faɗin.
“Zo nan ɗan CS ya girmafa”. A ranta kuma tace, uhummm in dai wannan ne ku zuba ido kusha kallon tijarar da zai fesa mata yar masu nataccen zuciya da naci kamar mayya.
Kusan duk parlour kallansu suka maida kan Jidda dake cewa.
“Babe in zuba ma papper meat ne?”. Wani irin dogon tsaki yaja wanda yasa suka ɗan kalleshi har da Abba shi ya zubawa ido.
Salim kuwa kai ya jinnina cikin alamun madalla zaiyi maganinki.
“Babe in bazakaci wannan ba to ka gaya min me kake so in dafa maka”. Wani irin juyowa yayi ya watsa mata kallon da yasa Salim murmurshi ita kuwa kai ta sunkuyar jin yana faɗin.
“Kika ƙara cemin Babe sai na sumar dake, kaji yar iskar yarinya da raini wai nine ma babe nine ma babe dinki, nifa ba'a min gwaninta, dan ni tsanar mutuma nakeyi in yana min iyayi ba burgeni zakiyi ba”. Sai kuma duk suka kalli Fariyda data taɓe baki gami da sakin murmushi da sautinsa ya subce mata wai.
“shifa ba'a mishi gwaninta" wlh kalmar dariya take bata ganin rashin mutuncinsa a fili yake nuna shifa ba'a iya masa. Ita kuwa Jidda cikin kashe zuciya tace.
“To naji Yah Mahmoud me zan maka”. Mari Salim ya watsa mata tare da cewa.
“Ke fice daga nan”.
Da sauri Abba ya dakatar dasu da yin gyaran murya.
“Kai Salim Kar in sake ganin ka taɓa mace da sunan mari ai wannan zalumci ma bayyani ya tana mace zaku hantareta kai kuma ka ƙara da mari, mace fa abar tausayice sabida rauninta, bana iya jurar ganin an tauye mace. Yi haƙuri Jidda kin san yayun naki”.
Da ido Saddiqa ta rakata lokacin da Goggo Dada taja hannunta suka fita, ita har ga Allah ta ɗauka Jidda ce babba kam Salim sabida habakar jikinta sai yanzu da Abba ya faɗane ta ɗan lura da jikin fuku-fuku ne. Fitan sune yasa Abba kallon Mahmoud yace.
“To kai kuje kuci abinci ko”. Da sauri Salim yace.
“Bari in kawo maka abincin Madam yau tun safe nasa tayi maka girki kaci abincin gidana”. A hankali yace.
“Mami ta bani abinci ai, Hafiz ka ɗauko mana shi yana mota”.
Cikin mmki Fariyda da Amina da Ummi ke kallonsa.
Su kuwa su Saddiqa murmushi jin dadin yadda yayiwa Jidda sukayi har da Salma duk suka fito parlour.
Ya rage daga shi sai Ummi Amina Fariyda dasu Zaid da Sulaiman da Salim.
“Kayi wanka ne?”. Sulaiman ya tambaya.
“Eh nayi”. Ya bashi amsa a taƙaice. Fariyda da ta zauna don son ganin gudun ruwansa ne ta kalli Hafiz da ya shigo da trayn da Mami ta shirya kulolin.
A gabanshi ya ajiye, sai kuma ya fara ɗauko tray da Mamanshi ta shirya mishi abinci duk ya ajiye a tsakiyar parlour. Amina ce ta fara sawa Sulaiman da Salim da Hafiz ɗin da Huzaifa.
“Wanne zan zuba maka”. Ta tambayi Mahmoud ɗin tana kallonsa tare da buɗe wormes ɗin kan tryan Mami da kuma nata ɗin duka.
Kular farko na trayn mamaki wanda yake ɗauke da dandarerun naman rago ne mai kyau da ƙamshi sai turiri yakeyi ya ɗan nuna mata.
Ita ma Fariyda har yanzu shi take kallo ta gefen idan, ɗaya kular ta buɗe couscous ne mai kyau wanda yayi sar-sar sai karamar kulan vegetables soup ne wanda yake wadace da kifi. Cikin mmki take kallonsa jin yace.
“Samin shi”. Abba ma da mmani yake kallonsa hakama Amina da Ummi da Goggo Dada data shigo tare da Jidda. Sulaiman kam ido kawai ya zuba mishi.
Sa mishi Amina tayi couscous a plate ta sa ɗan vegetables soup ɗin a bowl ɗin plate ɗin Mami, sai ta kuma daukan ɗaya bowl ɗin ta sa mishi danderun tare da sa mishi spoon gyara zamansa yayi yana mai ɗaukar spoon ɗin ya kalli Abba yace.
“Abba yau abincin Malam Mami ta bani shiyasa zanci dan malam yace in naci zaiji daɗi naci abincinsa”. Ya ƙare maganar yana kai spoon ɗin daya yago tattausar tsokar danderun bakinsa.
Kusan duk a tare suka kalli juna ita, kam Fariyda ɗan baki ta buɗe cikin tsananin mamaki, sai kuma kawai ta miƙe tsaye jin Amina na cewa.
“Abba me zan saka maka?”. Yana murmushi yace. "Nima ɗin Abincin gidan Malam Ibrahim ɗin zanci”. Hakan da tajine yasata murmushi tare da juyawa zata fita.
“A'a Fariyda zo nan ki zauna kema muci abinci ko”. Cikin kunya da girmamawa tace.
“Abba Aunty Rashida ta kawo min ɗanwake shi zanje inci”. Da sauri Amina tace.
“Muje nima ai na kawo miki waina kuma sai kinci”. Ummi na binsu a baya tace.
“Lallai ma kam naji Salma na cewa ta miki dambu, yau to me zakici.
Daga nan duk suka fita.
A parlour ta samesu nan suka wuni zaune sukayi ta ciye-ciyen gayu da hirarsu ta yaushe gamo sai salla ke tada su, sai wuraren ƙarfe goma na dare suka watse ko wacce ta koma gidanta bayan Amina ta raba musu tsarabar da Mahmoud yayi.
Ita kuwa Amina sai karfe sha ɗaya suka tafi da Hafiz.
Tuni Fariyda tayi bacci a ɗakin Goggo Dada.
Washe gari da sassafe ya Yah Mujahid ya.......