Sashe 80
Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ɗan jim Baba Malam yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, tabbas Dirankadi nada kima da kuma mutumci a idanunsa, saboda haka zai iya yimasa alfarma kuwa kowacce iri ce, saidai kuma ayanzu baisan yaya girman alfarmar take ba, cikin halin dattako da nutsuwa irin nasa yace.
"Ai Dirankadi kafi ƙarfin al'farma awajena, saidai kuma bazanyi hanzari ba, ina jinka wace al'farma ce wannan, dahar yasa ka taso da kanka kazo, ai da ko awaya kaƙira ka sanar dani zan iya yi maka ita."
Kai Dirankadi ya jinjina cikin jin daɗi yace, "Nagode ƙwarai da wannan karramawar Malam Basheer, yanzu kuwa zanyiwa abokan tafiyana magana dan su samu shigowa."
Nan ya ciro wayarsa ya turawa Saifuddeen text akan cewa.
"Su shigo."
Koda Saifuddeen ya karanta text ɗin na Dirankadi, buɗe murfin motar yayi ya fita, dan dama tuni Sule ya fito masa da wheelchair ɗinsa, ganin haka yasa Sule zagayawa ɓangaren da Zaleehan take ya buɗe mata murfin motar, asanyaye kuwa ta fito daga cikin motar, gaba ɗaya jikinta rawa yake saboda fargaba da kuma tsoro.
Haka suka nufi ɓangaren Baba Malam ɗin, Saifuddeen na gaba, ita kuma tana biye dashi abaya, da ƙyar take iya taka ƙafafunta da suka mata nauyi, ga kuma wani masifaffen tsoro haɗi da faɗuwar gaba da takeji.
Dai-dai sun kawo ƙofar shiga falon ne, tayi saurin kamo hannun sa, ɗan tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleta, wasu irin hawaye masu zafi ne suka silalo daga cikin idanunta, sosai jikinta ke rawa, harta laɓɓan bakinta ma rawa suke, idanunsa ya ɗan lumshe jin yadda ta rumtse tafin hannunshi cikin nata tana mammatse mishi hannun da jan yatsunshi cikin yanayin tsoro, ajiyan zuciya ya sauƙe tare da girgiza mata kansa, hannunta yaɗan murza sannan suka nufi cikin falon Baba Malam ɗin.
Jin an taɓa ƙofar falon yasa dukansu suka zubawa ƙofar idanu, dan ganin me shigowa, Ganin Saifuddeen Yasa Baba Malam ɗan sakin murmushi, take kuma saiga Zaleeha ta biyo baya, dan dama har yanzu Saifuddeen ɗin na riƙe da hannunta, da sauri Baba Malam ya ɗauke kansa daga kallonta, take yanayin annurin fuskarsa ya sauya, jiyayi kwata kwata ma bayason ganinta hakan yasa ya kawar da kansa gefe.
Saifuddeen na riƙe da hannunta suka ƙaraso cikin falon, har gaban Baba Malam ɗin ya ƙaraso, ita kuwa Zaleeha kanta na ƙasa, hawayene kawai keta tsiyaya daga cikin idanunta, sake hannunta Saifuddeen yayi tare da sauƙa akan wheelchair din nasa, ya yasa guiwowinsa aƙasa, itama Zaleehan zubewa tayi aƙasa, wanda hakan yasa kusan rabin jikinta ya shiga jikin Saifuddeen, gaba ɗaya idanunta sun rufe, ƙwalla ne kawai acikinsu, hawaye wani na koran wani kaman an kunna sabon famfo.
Kifa kanta tayi akan ƙafafun Baba Malam dake zaune, lokaci guda ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan tace.
"Dan Allah Baba Malam kayi haƙuri ka yafemin, kar in mutu da fushinka na tuba ka yafemin ko zan samu kekyawan rayuwa, Idan baka yafemin ba nima mutuwa zanyi, wallahi nayi nadamar abun da na aikata, na tuba Ka jiƙaina ka yafemin!!."
Taƙare maganar tana Kuka sosai kamar ranta zai fita.
Cikin fushi Baba Malam ya janye ƙafansa baya, hakanne yasa ta ɗago da kanta, tana kuka sosai haɗe hannuwanta waje ɗaya tayi alaman roƙo, cikin matsanancin kukan ta ɗaga idanu ta kalli Malam Adam, da kuma Ya Ahmad gani tayi sun kauda kansu daga kallonta, alaman har yanzu suna fushi da ita, duƙar da kanta tayi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, hakanne yasa Saifuddeen ɗaura hannunsa akan nata ya riƙe ƙam, jin haka yasa ta sake mannewa a jikinsa, tare da kama hannunsa tana jijjigawa kuka take sosai, wanda hakan yasa yakejin wani abu na taɓa zuciyarsa, kowani ɗigan hawayenta ɗaya tamkar ɗigan narkakken dalma ne, akan zuciyarsa haka yakeji.
Dirankadi ne ya gyara zama zuciyar sa cike da tausayin Zaleehan, saboda yanda take kuka, wanda dagani kasan daga cikin ƙarƙashin zuciyarta da kuma ranta yake fitowa.
Asanyaye yace.
"Yafiya ga Zaleeha itace al'farmar da nake nema awajenka Malam Basheer, haƙiƙa Zaleeha ta aikata ba dai-dai ba, wanda alokacin ni kaina saida naji babu daɗi, amma ayanzu tabbas ta gane kuskurenta kuma tayi na dama, shikansa wanda ta gudawa ɗin na tabbatar da cewa ya yafe mata, tunda gashi shida kansa ya ɗaukota dan su zo su baka haƙuri, dan Allah Malam Basheer ku yafe mata, kada ku manta fa cewa ita macece me raunin zuciya, rashin yafe mata zai iya haifar da wata sabuwar matsalan, abun zaiyi mata yawa, har yanzu Zaleeha yarinyace ƙara ma, damuwa kaɗan zai iya haifar mata da matsala, da wanne ɗaya zataji? da rashin ƴar uwarta ko kuwa da fushin da kukeyi da ita, ayanzu Al'barkarku take nema, bawai ɓacin rai da fushi ba, nidai ina roƙa mata al'farma dan Allah ayafe mata."
Kai Baba Malam ya girgiza, tare da miƙewa tsaye, sam bayajin zai yafewa Zaleeha'n, saboda har yanzu akwai ƙunci da baƙin cikin da ta shayar dashi kwance acikin zuciyarsa, kuma ma baisan niyartaba dole yayi wani abu dan gano meke cikin ranta.
Juyawa yayi da niyar barin falon, cikin bazata yaji an riƙe hannunsa, ɗan juyowa yayi afusace dan yasan cewa Zaleehan ce kawai zatayi mishi haka, amma ga mamakinsa sai yaga Saifuddeen ne, wanda idanunsa gaba ɗaya sun ciko da ƙwalla, sannan sunyi jajir, sakin hannu Baba Malam ɗin yayi, tare da haɗe hannuwansa waje ɗaya alaman roƙo, kansa ya rinƙa jujjuya wa yayinda wayenshi ke gab da zubowa.
Zaleeha kuwa sake shigewa jikin Saifuddeen ɗin tayi, tare da ɗaura kanta akan kafaɗansa, tana wani irin kuka me matuƙar tsuma zuciya, kukanta kuwa shikesa Saifuddeen yaji kansa kamar zai fashe, haka kuma har cikin ransa yakejin kukan nata, ci gaba yayi da jijjigawa Baba Malam kai, alaman yayi haƙuri yayi musu afuwa.
"Ai Dirankadi kafi ƙarfin al'farma awajena, saidai kuma bazanyi hanzari ba, ina jinka wace al'farma ce wannan, dahar yasa ka taso da kanka kazo, ai da ko awaya kaƙira ka sanar dani zan iya yi maka ita."
Kai Dirankadi ya jinjina cikin jin daɗi yace, "Nagode ƙwarai da wannan karramawar Malam Basheer, yanzu kuwa zanyiwa abokan tafiyana magana dan su samu shigowa."
Nan ya ciro wayarsa ya turawa Saifuddeen text akan cewa.
"Su shigo."
Koda Saifuddeen ya karanta text ɗin na Dirankadi, buɗe murfin motar yayi ya fita, dan dama tuni Sule ya fito masa da wheelchair ɗinsa, ganin haka yasa Sule zagayawa ɓangaren da Zaleehan take ya buɗe mata murfin motar, asanyaye kuwa ta fito daga cikin motar, gaba ɗaya jikinta rawa yake saboda fargaba da kuma tsoro.
Haka suka nufi ɓangaren Baba Malam ɗin, Saifuddeen na gaba, ita kuma tana biye dashi abaya, da ƙyar take iya taka ƙafafunta da suka mata nauyi, ga kuma wani masifaffen tsoro haɗi da faɗuwar gaba da takeji.
Dai-dai sun kawo ƙofar shiga falon ne, tayi saurin kamo hannun sa, ɗan tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleta, wasu irin hawaye masu zafi ne suka silalo daga cikin idanunta, sosai jikinta ke rawa, harta laɓɓan bakinta ma rawa suke, idanunsa ya ɗan lumshe jin yadda ta rumtse tafin hannunshi cikin nata tana mammatse mishi hannun da jan yatsunshi cikin yanayin tsoro, ajiyan zuciya ya sauƙe tare da girgiza mata kansa, hannunta yaɗan murza sannan suka nufi cikin falon Baba Malam ɗin.
Jin an taɓa ƙofar falon yasa dukansu suka zubawa ƙofar idanu, dan ganin me shigowa, Ganin Saifuddeen Yasa Baba Malam ɗan sakin murmushi, take kuma saiga Zaleeha ta biyo baya, dan dama har yanzu Saifuddeen ɗin na riƙe da hannunta, da sauri Baba Malam ya ɗauke kansa daga kallonta, take yanayin annurin fuskarsa ya sauya, jiyayi kwata kwata ma bayason ganinta hakan yasa ya kawar da kansa gefe.
Saifuddeen na riƙe da hannunta suka ƙaraso cikin falon, har gaban Baba Malam ɗin ya ƙaraso, ita kuwa Zaleeha kanta na ƙasa, hawayene kawai keta tsiyaya daga cikin idanunta, sake hannunta Saifuddeen yayi tare da sauƙa akan wheelchair din nasa, ya yasa guiwowinsa aƙasa, itama Zaleehan zubewa tayi aƙasa, wanda hakan yasa kusan rabin jikinta ya shiga jikin Saifuddeen, gaba ɗaya idanunta sun rufe, ƙwalla ne kawai acikinsu, hawaye wani na koran wani kaman an kunna sabon famfo.
Kifa kanta tayi akan ƙafafun Baba Malam dake zaune, lokaci guda ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan tace.
"Dan Allah Baba Malam kayi haƙuri ka yafemin, kar in mutu da fushinka na tuba ka yafemin ko zan samu kekyawan rayuwa, Idan baka yafemin ba nima mutuwa zanyi, wallahi nayi nadamar abun da na aikata, na tuba Ka jiƙaina ka yafemin!!."
Taƙare maganar tana Kuka sosai kamar ranta zai fita.
Cikin fushi Baba Malam ya janye ƙafansa baya, hakanne yasa ta ɗago da kanta, tana kuka sosai haɗe hannuwanta waje ɗaya tayi alaman roƙo, cikin matsanancin kukan ta ɗaga idanu ta kalli Malam Adam, da kuma Ya Ahmad gani tayi sun kauda kansu daga kallonta, alaman har yanzu suna fushi da ita, duƙar da kanta tayi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, hakanne yasa Saifuddeen ɗaura hannunsa akan nata ya riƙe ƙam, jin haka yasa ta sake mannewa a jikinsa, tare da kama hannunsa tana jijjigawa kuka take sosai, wanda hakan yasa yakejin wani abu na taɓa zuciyarsa, kowani ɗigan hawayenta ɗaya tamkar ɗigan narkakken dalma ne, akan zuciyarsa haka yakeji.
Dirankadi ne ya gyara zama zuciyar sa cike da tausayin Zaleehan, saboda yanda take kuka, wanda dagani kasan daga cikin ƙarƙashin zuciyarta da kuma ranta yake fitowa.
Asanyaye yace.
"Yafiya ga Zaleeha itace al'farmar da nake nema awajenka Malam Basheer, haƙiƙa Zaleeha ta aikata ba dai-dai ba, wanda alokacin ni kaina saida naji babu daɗi, amma ayanzu tabbas ta gane kuskurenta kuma tayi na dama, shikansa wanda ta gudawa ɗin na tabbatar da cewa ya yafe mata, tunda gashi shida kansa ya ɗaukota dan su zo su baka haƙuri, dan Allah Malam Basheer ku yafe mata, kada ku manta fa cewa ita macece me raunin zuciya, rashin yafe mata zai iya haifar da wata sabuwar matsalan, abun zaiyi mata yawa, har yanzu Zaleeha yarinyace ƙara ma, damuwa kaɗan zai iya haifar mata da matsala, da wanne ɗaya zataji? da rashin ƴar uwarta ko kuwa da fushin da kukeyi da ita, ayanzu Al'barkarku take nema, bawai ɓacin rai da fushi ba, nidai ina roƙa mata al'farma dan Allah ayafe mata."
Kai Baba Malam ya girgiza, tare da miƙewa tsaye, sam bayajin zai yafewa Zaleeha'n, saboda har yanzu akwai ƙunci da baƙin cikin da ta shayar dashi kwance acikin zuciyarsa, kuma ma baisan niyartaba dole yayi wani abu dan gano meke cikin ranta.
Juyawa yayi da niyar barin falon, cikin bazata yaji an riƙe hannunsa, ɗan juyowa yayi afusace dan yasan cewa Zaleehan ce kawai zatayi mishi haka, amma ga mamakinsa sai yaga Saifuddeen ne, wanda idanunsa gaba ɗaya sun ciko da ƙwalla, sannan sunyi jajir, sakin hannu Baba Malam ɗin yayi, tare da haɗe hannuwansa waje ɗaya alaman roƙo, kansa ya rinƙa jujjuya wa yayinda wayenshi ke gab da zubowa.
Zaleeha kuwa sake shigewa jikin Saifuddeen ɗin tayi, tare da ɗaura kanta akan kafaɗansa, tana wani irin kuka me matuƙar tsuma zuciya, kukanta kuwa shikesa Saifuddeen yaji kansa kamar zai fashe, haka kuma har cikin ransa yakejin kukan nata, ci gaba yayi da jijjigawa Baba Malam kai, alaman yayi haƙuri yayi musu afuwa.