Sashe 61
Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Tun afaɗan maganganunsa na farko, ta dainajin komai, duk wani abu najikinta tsayawa yayi, wayar hannunta ne ta sulale inda ta faɗi ƙasa, wani irin ƙara ta saki take kuma ta faɗi awajen sumammiya, cikin matsanancin tashin hankali, Aisha tayi kanta tana jijjigata, haɗi da ƙiran sunanta, ihunta da su Elizabet sukaji ne yasasu shigowa aguje, ganin Zaleehan asume yasa Elizabet dafe ƙirji cikin ɗaga murya tace.
"Innalillahi, a madadin tace Oh jesus meya ke faruwa?" Uncle solomon ne ya fita da gudu, bajimawa ya shigo hannunsa riƙe da kofin ruwa, ƙarasowa yayi inda ya ɗan yayyafawa Zaleehan ruwa afuskarta.
Azabure tatashi, cikin wani irin tashin hankali, damƙo Aisha tayi tana me jujjuya kanta, take kuma sai ta fashe da wani irin kuka mai matuƙar tada hankali, cikin kukan take ja da baya, tana me sake girgiza kanta, hankalinta amatuƙar tashe tace.
"Aisha Adda Maryam, Adda Maryam ɗina ta rasu, Adda Maryam tabar duniya batare da na sake sanyata a idanuna ba, wayyo Allah na wayyo ni, kaicon rayuwata, kaicona !!!" Wani irin azababben kuka ta saka kukane mai cushe zuciya da numfashi, lokaci ɗaya ta miƙe tsaye wayarta kawai ta ɗauka tare da buɗe jakanta, kuɗi ta ɗauko wanda batamasan ko nawa bane, takalmi ta zura aƙafafunta, ƙoƙarin fita daga cikin ɗakin take Elizabet ta riƙota cikin kulawa tace.
"Zaleeha ina zakije, dan Allah kitsaya ki nutsu tukun"
FaÉ—awa jikin Aishan tayi tana wani irin kuka, kanta ta girgiza cikin kuka tace.
"Adda Maryam É—ina Uncle Solomo Addana, Adda Maryam É—ina ta rasu"
Hawayen tausayin Zaleehan ne suka kwaranyo daga cikin idanun baki É—ayansu cikin sanyin murya Aisha tace.
"Muje to na rakaki ki hau mota, amma kafun nan ki kimtsa tukunna."
Kai Zaleeha ta girgiza cikin matsanancin kukan dake neman shiÉ—ar da ita ya tafi da rants.
Hannunta Aisha ta kama suka nufi ƙofar fita daga gidan Solo da martasa na biye dasu a baya.
Gaba É—aya Zaleeha bata cikin hayyacinta, hakanne yasa Aisha mannata da jikinta, domin kukan da Zaleehan keyi yasa bata ko iya ganin gabanta.
Suna kawo bakin titi kuwa sukai sa'a nan suka samu wata mota, wanda kaitsaye Gombe zata taho, da kwai ma mutane cike acikinta, Aisha ce tayi mata komai, tasata acikin motar, hannun Zaleehan dake kuka ta kamo, nan ta É—an É—aga mata hannu, itama hawayene ke zuba akan fuskarta, murya asanyaye tace.
"Allah yajiƙanta yasa al'janna tazamo makoma agareta, kiyi haƙuri kinji Zaleeha, dukkan me rai dama mamaci ne, kowa lokacinsa yake jira, dayazo kuma babu jinkiri."
Kai Zaleeha ta jinjina, tare da sakin sabon kuka, nandai Me motar yaja suka tafi, kowa dake cikin motar kallon yanda Zaleeha ke kuka suke, wasu kukan nata ya damesu, wasu kuwa matsanancin tausayinta ne ya kamasu, domin kukan da take irin kukan nanne me karÆ´ar da zuciya, kukan da take, kukane me fitar da irin tsananin tashin hankalin da take ciki, kukane da duk me imani dole zaiji tausayinta.
Littafina na kuɗine in kin gashi yana yawoma na satane, in kina buƙatan saya ga no ɗina 09097853276
By
*GARKUWAR FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: *(heart touching)*
"Innalillahi, a madadin tace Oh jesus meya ke faruwa?" Uncle solomon ne ya fita da gudu, bajimawa ya shigo hannunsa riƙe da kofin ruwa, ƙarasowa yayi inda ya ɗan yayyafawa Zaleehan ruwa afuskarta.
Azabure tatashi, cikin wani irin tashin hankali, damƙo Aisha tayi tana me jujjuya kanta, take kuma sai ta fashe da wani irin kuka mai matuƙar tada hankali, cikin kukan take ja da baya, tana me sake girgiza kanta, hankalinta amatuƙar tashe tace.
"Aisha Adda Maryam, Adda Maryam ɗina ta rasu, Adda Maryam tabar duniya batare da na sake sanyata a idanuna ba, wayyo Allah na wayyo ni, kaicon rayuwata, kaicona !!!" Wani irin azababben kuka ta saka kukane mai cushe zuciya da numfashi, lokaci ɗaya ta miƙe tsaye wayarta kawai ta ɗauka tare da buɗe jakanta, kuɗi ta ɗauko wanda batamasan ko nawa bane, takalmi ta zura aƙafafunta, ƙoƙarin fita daga cikin ɗakin take Elizabet ta riƙota cikin kulawa tace.
"Zaleeha ina zakije, dan Allah kitsaya ki nutsu tukun"
FaÉ—awa jikin Aishan tayi tana wani irin kuka, kanta ta girgiza cikin kuka tace.
"Adda Maryam É—ina Uncle Solomo Addana, Adda Maryam É—ina ta rasu"
Hawayen tausayin Zaleehan ne suka kwaranyo daga cikin idanun baki É—ayansu cikin sanyin murya Aisha tace.
"Muje to na rakaki ki hau mota, amma kafun nan ki kimtsa tukunna."
Kai Zaleeha ta girgiza cikin matsanancin kukan dake neman shiÉ—ar da ita ya tafi da rants.
Hannunta Aisha ta kama suka nufi ƙofar fita daga gidan Solo da martasa na biye dasu a baya.
Gaba É—aya Zaleeha bata cikin hayyacinta, hakanne yasa Aisha mannata da jikinta, domin kukan da Zaleehan keyi yasa bata ko iya ganin gabanta.
Suna kawo bakin titi kuwa sukai sa'a nan suka samu wata mota, wanda kaitsaye Gombe zata taho, da kwai ma mutane cike acikinta, Aisha ce tayi mata komai, tasata acikin motar, hannun Zaleehan dake kuka ta kamo, nan ta É—an É—aga mata hannu, itama hawayene ke zuba akan fuskarta, murya asanyaye tace.
"Allah yajiƙanta yasa al'janna tazamo makoma agareta, kiyi haƙuri kinji Zaleeha, dukkan me rai dama mamaci ne, kowa lokacinsa yake jira, dayazo kuma babu jinkiri."
Kai Zaleeha ta jinjina, tare da sakin sabon kuka, nandai Me motar yaja suka tafi, kowa dake cikin motar kallon yanda Zaleeha ke kuka suke, wasu kukan nata ya damesu, wasu kuwa matsanancin tausayinta ne ya kamasu, domin kukan da take irin kukan nanne me karÆ´ar da zuciya, kukan da take, kukane me fitar da irin tsananin tashin hankalin da take ciki, kukane da duk me imani dole zaiji tausayinta.
Littafina na kuɗine in kin gashi yana yawoma na satane, in kina buƙatan saya ga no ɗina 09097853276
By
*GARKUWAR FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: *(heart touching)*