Sashe 104
Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Jin motsinshi ne yasa ta rufe ida nunta,
kunna hasken wayarsa yayi gane ba bacci takeyi bane ya sashi ɗauke Adeel cak ya medashi kan gadonshi kana ya dawo a hankali ya sauƙa kan kekenshi ya hau kan gadon ya konta inda ya ɗauke Adeel ya meye gurbin shi kenan,
ya zama suna fuskantar juna.
a hankali yasa hannu ya jawota jikinshi,
da sauri taja baya tare da juyawa ta bashi baya.
Hannunsa yasanya ya rungumota ta baya, fusge jikinta tayi, ranta amatuƙar ɓace, ta matsa daga kusa dashi, idanunta wanda suka kaɗa sukai jajur ta watsa masa, cikin fushi da ƙunan zuciya tace. "Kada ka taɓani, dan bani da buƙatar hakan, bani kaɗai bace matarka ai, kana da wanda kake ɗauka kutafi resturant da garden ai, ni dama menene amfani na awajenka, tunda na riga dana haifi ɗa, sannan kuma bankaita kyau ba, hakanne yasa kake ƙoƙarin fifi tata akaina, saboda kun fita yawon shaƙatawa, kunje kun more rayuwarku, dole ai kace bazaka ci abinci ba, tunda kana da ƴar gold kunje kun wuni liƙe da juna harda wani cewanta a gajiye take,ai ba sai ta faɗa min haka zan gane ta wuni a kanka kuna aurataiya ba."
Taƙare maganan cikin matsanancin ɓacin rai, da kuma tafasar zuciya, Allah yasani kishin Saifuddeen yaci ƙarfinta, saboda hakane ma take yarda da duk wani abun da zuciyarta ta raya mata.
Shiru yayi tare da tsura mata tsumammun idanunsa, ƙwarai yanda idanunta suka rufe, take faɗan duk wani abu da yazo bakinta, shine abun dake matuƙar basa mamaki, dan gaba ɗaya lokaci guda ta sauya, ta tashi daga Ameenan da yasani ada, ta dawo wata irin mace me yawan ƙorafi, da kuma yarda da zargi bata da wani mugun abu tare da ita illa kishi dake son fin ƙarfinta, wato dama duk ilimin mace dole kishi na tsaburarta sai dai wasu na iya dannewa, wasu basa iya, a zahiri dai babu matar da bata da kishi,kuma yaji ya sani ya yarda zazzafan son da take mishine yasa take tsananin kishinsa.
Kansa ya girgiza tare da sa hannu ya kamo hannayenta, tabbas dole zaiyi mata uzuri saboda yasan zafin kishi ne ke É—awainiya da ita, a wayarshi ya rubuta mata.
"Zargi bashi da kyau, kin sani ko a addinance, meyasa Ameena? meyasa ako yaushe kike yarda da abun da zuciyarki ke faɗa miki, meyasa ba zakina ƙaryata zuciyarki ba? kada ki cigaba da bari shaiɗan yayi tasiri acikin zuciyarki, tayaya kike tunanin aranan girkinki zan ɗau Zaleeha mu tafi garden ko resturant duk dan kawai na baƙanta miki, sam ba haka nake ba, ya kamata ace ke dakanki ki zama shaida, dan bana iya tauyewa kowa haƙƙinsa, sannan da kiketa ihun cewa munje resturant, ayaushe ne mukaje resturant ɗin? ya kamata ace kina kyautata mana zato, domin kuwa ba resturant mukaje ba, gidan Baba Malam mukaje, saboda yau akayi sadakan bakwai ɗin rasuwar Adda Maryam, zargi bashi da kyau, yana lalata aure, saboda haka ya kamata kina iya controlling zuciya, kishi, da kuma fushinki sabida bana so ki lalata mana zamanmu." Hannunta dake cikin nasa ta janye, kwata-kwata maganganun da ya faɗa basuyi tasiri acikin kunnuwanta ba duk da wani sashi na zuciyarta ya yarda da batunshi, sai dai zafin kishi da takeji ya danne komai hasalima jinsa kawai take, dan ayanzu kam gaba ɗaya idanunta sun rufe, wutar kishi ne kawai kecin zuciyarta, hakan yasa ba zata gane gaskiya ko akasinta ba, ganin yanda take ta sakin huci tana fitar da numfashi cikin fushi, ya sashi girgiza kansa kawai, tabbas tana ƙoƙarin ɓarar da damar da ta samu,
gyara kwanciyarsa yayi tare da kwanciya ya juya mata baya, saboda aduniya baya tunanin akwai wata mace da ta isa, yi masa fushi babu dalili, ya kuma rarrasheta taƙi ji, shiba sakarai bane, saboda haka bazai taɓa zama wawa akan mace ba, ko Zaleeha da ta kasance zaɓinsa ne takeyi masa haka, to tabbas bazai tsaya sauraranta ba, domin yariga dayasan ko awajen Allah bashi da wani laifi, tunda dai bai aikata ba dai-dai ba. Blanket ya ja ya rufa ajikinsa, tare da lumshe idanunsa. Ameena kuwa ganin yanda yayi kwanciyarsa ba tare da ya kara ce mata komai ba, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ƙara ɓaci, can nesa dashi ta matsa tare da jawo Adeel jikinta.
Saifuddeen kuwa dama baji yake ba, kuma gashi ya bata baya, hakan yasa baimasan tanayi ba, dan baccin gajiya ne ma keneman É—aukarsa.
Saida tayi kuka sosai kafun take maida ajiyar zuciya, jitake inama da ace Zaleeha bata dawo gidan ba, inama da ace Saifuddeen baikasance mijin Zaleeha ba, da duk hakan baifaru akanta ba, dan tanajin zata iya jure kishi da kowacce mace amma banda Zaleeha, ta jima sosai tana sheshsheƙan
Washegari da asuba kuwa antashi da ruwa, hakan yasa bai samu zuwa masallaci ba, nan cikin toilet ya shiga ya É—auro alwala, tare da shumfuÉ—a darduma ya tada sallah.
Itama Ameenan miƙewa tayi, ta shige toilet ruwa ta ɗan watsa ajikinta, saboda ta tashi taji zuciyarta wasai, acikin kaso ɗari na damuwarta kaso saba'in ya ragu, hakanan taji cewar abun da tayi masa daren jiyan bata kyauta masa ba, sauda dama takanyi regreting abubuwan da takeyi mai, dan kuwa ita kanta tasan baiyi mata laifin komai ba hakama Zaleeha bata tare mata komai ba, kawai dai zafin kishi ne ke ɗawainiya da ita wanda kuma tana addu'an ALLAH ya yaye matashi tajin son Zaleeha koda al'barkacin son da takewa Adeel, nan kusa dashi ta shumfuɗa wani darduman, tare da ta da sallah, zuwa lokacin kuwa shikam ma harya idar, zaune yake akan guiwowinsa, yana gabatar da azkar, yana nan azaune harta idar da sallan itama azkar ɗin tayi, sannan ahankali ta ɗago ta kalleshi, gaba ɗaya jikinta asanyaye yake, ga kuma wani irin fitinannen ƙaunarsa da kuma sha'awarsa da takeji, hannunta takai ta dafa kafaɗansa, sarai yajita amma sai yayi kaman ma baisan tanayi ba, ganin haka yasa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, ganin yana kallonta yasa taɗan sunkuyar da kanta, asanyaye tace.
"Ina kwana."
Kansa ya jinjina mata alaman.
"Lafiya." ƙoƙarin hawa wheelchair ɗinsa yasomayi, ganin haka yasa ta faɗa jikinsa, cikin sanyin guiwa tace.
"Dan Allah Abban Adeel kayi haƙuri, nima bansan meyasa nakejin wasu abubuwa akanku wani lokaci ba, kasan inasonka wannan dalilin yasa nakejin kishinka sosai araina, amman in sha Allah zan bari dan nacewa Mamana taita min Addu'a Allah ya yaye min kaima kaita min Addu'a kuma nima inayi." Idanunsa ya zuba mata, shi mutum ne me saurin fahimta da kuma uzuri, musamman ma ita da yasan cewa kishine ke ɗawainiya da zuciyarta. Ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da jinjina mata kai alaman.
"Shikenan komai ya wuce."
murmushi ta sakar masa tare da sake shigewa jikinsa, bakinta har rawa yake haka ta shiga kissing ɗinsa tako ta ina, sam bai hanata ba, dan baiso ya tauye mata haƙƙi, jikinta na rawa haka ta taimaka masa ya kwanta akan gado, bin bayansa itama tayi, tare da haɗe jikinsu waje ɗaya.
Duk wani abun da takeso baiƙi yi mata ba sabida shima yana buƙatarta, haka ya bata duk wani haƙƙinta dake kansa, after 22 minute gaba ɗaya jikinsa yayi weak, gajiya ne keta damunsa, da ƙyar ya iya tashi yayi wanka, fita yayi inda yaje ya gaishe da Umminsa, yana dawo wa kuwa nan kan gadon ya kwanta yana me da numfashi, ahaka har bacci ya ɗaukesa.
Ameena kuwa jin ranta take fari ƙal, wani annushuwa takeji acikin ranta, koda ta fito daga wankan, mai kawai ta shafa sannan ta yiwa Adeel wanka, saida ta fara shirya Adeel ɗin, kafun ta shirya kanta cikin kayanta na zuwa aiki.
Ganin Saifuddeen ɗin na bacci ne yasa taɗan ranƙwafo tare da yi masa kiss agoshinsa, Adeel na ɗauke akan kafaɗanta ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye sashin Ummi ta nufa, anan falo ta iske su azaune, yayinda Zaleeha ke zaune anan ƙasan sofa, tasha kyau cikin simple riga da sket ɗin dake jikinta, anutse ta gaishe da Ummi sannan Zaleeha ta miƙa hannu ta amshi Adeel, yau ko breakfast ma bata tsaya tayi ba, saboda taɗan makara.
kuma tana son yau ɗin ta keɓe da ƙawarta, Samira tasan zata ƙara kwantar mata da hankali kuma zata bata shawarwarin yadda zata samu ta yaƙi wannan zazzafan kishin ta zauna da ƴar uwarta lfy.
kunna hasken wayarsa yayi gane ba bacci takeyi bane ya sashi ɗauke Adeel cak ya medashi kan gadonshi kana ya dawo a hankali ya sauƙa kan kekenshi ya hau kan gadon ya konta inda ya ɗauke Adeel ya meye gurbin shi kenan,
ya zama suna fuskantar juna.
a hankali yasa hannu ya jawota jikinshi,
da sauri taja baya tare da juyawa ta bashi baya.
Hannunsa yasanya ya rungumota ta baya, fusge jikinta tayi, ranta amatuƙar ɓace, ta matsa daga kusa dashi, idanunta wanda suka kaɗa sukai jajur ta watsa masa, cikin fushi da ƙunan zuciya tace. "Kada ka taɓani, dan bani da buƙatar hakan, bani kaɗai bace matarka ai, kana da wanda kake ɗauka kutafi resturant da garden ai, ni dama menene amfani na awajenka, tunda na riga dana haifi ɗa, sannan kuma bankaita kyau ba, hakanne yasa kake ƙoƙarin fifi tata akaina, saboda kun fita yawon shaƙatawa, kunje kun more rayuwarku, dole ai kace bazaka ci abinci ba, tunda kana da ƴar gold kunje kun wuni liƙe da juna harda wani cewanta a gajiye take,ai ba sai ta faɗa min haka zan gane ta wuni a kanka kuna aurataiya ba."
Taƙare maganan cikin matsanancin ɓacin rai, da kuma tafasar zuciya, Allah yasani kishin Saifuddeen yaci ƙarfinta, saboda hakane ma take yarda da duk wani abun da zuciyarta ta raya mata.
Shiru yayi tare da tsura mata tsumammun idanunsa, ƙwarai yanda idanunta suka rufe, take faɗan duk wani abu da yazo bakinta, shine abun dake matuƙar basa mamaki, dan gaba ɗaya lokaci guda ta sauya, ta tashi daga Ameenan da yasani ada, ta dawo wata irin mace me yawan ƙorafi, da kuma yarda da zargi bata da wani mugun abu tare da ita illa kishi dake son fin ƙarfinta, wato dama duk ilimin mace dole kishi na tsaburarta sai dai wasu na iya dannewa, wasu basa iya, a zahiri dai babu matar da bata da kishi,kuma yaji ya sani ya yarda zazzafan son da take mishine yasa take tsananin kishinsa.
Kansa ya girgiza tare da sa hannu ya kamo hannayenta, tabbas dole zaiyi mata uzuri saboda yasan zafin kishi ne ke É—awainiya da ita, a wayarshi ya rubuta mata.
"Zargi bashi da kyau, kin sani ko a addinance, meyasa Ameena? meyasa ako yaushe kike yarda da abun da zuciyarki ke faɗa miki, meyasa ba zakina ƙaryata zuciyarki ba? kada ki cigaba da bari shaiɗan yayi tasiri acikin zuciyarki, tayaya kike tunanin aranan girkinki zan ɗau Zaleeha mu tafi garden ko resturant duk dan kawai na baƙanta miki, sam ba haka nake ba, ya kamata ace ke dakanki ki zama shaida, dan bana iya tauyewa kowa haƙƙinsa, sannan da kiketa ihun cewa munje resturant, ayaushe ne mukaje resturant ɗin? ya kamata ace kina kyautata mana zato, domin kuwa ba resturant mukaje ba, gidan Baba Malam mukaje, saboda yau akayi sadakan bakwai ɗin rasuwar Adda Maryam, zargi bashi da kyau, yana lalata aure, saboda haka ya kamata kina iya controlling zuciya, kishi, da kuma fushinki sabida bana so ki lalata mana zamanmu." Hannunta dake cikin nasa ta janye, kwata-kwata maganganun da ya faɗa basuyi tasiri acikin kunnuwanta ba duk da wani sashi na zuciyarta ya yarda da batunshi, sai dai zafin kishi da takeji ya danne komai hasalima jinsa kawai take, dan ayanzu kam gaba ɗaya idanunta sun rufe, wutar kishi ne kawai kecin zuciyarta, hakan yasa ba zata gane gaskiya ko akasinta ba, ganin yanda take ta sakin huci tana fitar da numfashi cikin fushi, ya sashi girgiza kansa kawai, tabbas tana ƙoƙarin ɓarar da damar da ta samu,
gyara kwanciyarsa yayi tare da kwanciya ya juya mata baya, saboda aduniya baya tunanin akwai wata mace da ta isa, yi masa fushi babu dalili, ya kuma rarrasheta taƙi ji, shiba sakarai bane, saboda haka bazai taɓa zama wawa akan mace ba, ko Zaleeha da ta kasance zaɓinsa ne takeyi masa haka, to tabbas bazai tsaya sauraranta ba, domin yariga dayasan ko awajen Allah bashi da wani laifi, tunda dai bai aikata ba dai-dai ba. Blanket ya ja ya rufa ajikinsa, tare da lumshe idanunsa. Ameena kuwa ganin yanda yayi kwanciyarsa ba tare da ya kara ce mata komai ba, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ƙara ɓaci, can nesa dashi ta matsa tare da jawo Adeel jikinta.
Saifuddeen kuwa dama baji yake ba, kuma gashi ya bata baya, hakan yasa baimasan tanayi ba, dan baccin gajiya ne ma keneman É—aukarsa.
Saida tayi kuka sosai kafun take maida ajiyar zuciya, jitake inama da ace Zaleeha bata dawo gidan ba, inama da ace Saifuddeen baikasance mijin Zaleeha ba, da duk hakan baifaru akanta ba, dan tanajin zata iya jure kishi da kowacce mace amma banda Zaleeha, ta jima sosai tana sheshsheƙan
Washegari da asuba kuwa antashi da ruwa, hakan yasa bai samu zuwa masallaci ba, nan cikin toilet ya shiga ya É—auro alwala, tare da shumfuÉ—a darduma ya tada sallah.
Itama Ameenan miƙewa tayi, ta shige toilet ruwa ta ɗan watsa ajikinta, saboda ta tashi taji zuciyarta wasai, acikin kaso ɗari na damuwarta kaso saba'in ya ragu, hakanan taji cewar abun da tayi masa daren jiyan bata kyauta masa ba, sauda dama takanyi regreting abubuwan da takeyi mai, dan kuwa ita kanta tasan baiyi mata laifin komai ba hakama Zaleeha bata tare mata komai ba, kawai dai zafin kishi ne ke ɗawainiya da ita wanda kuma tana addu'an ALLAH ya yaye matashi tajin son Zaleeha koda al'barkacin son da takewa Adeel, nan kusa dashi ta shumfuɗa wani darduman, tare da ta da sallah, zuwa lokacin kuwa shikam ma harya idar, zaune yake akan guiwowinsa, yana gabatar da azkar, yana nan azaune harta idar da sallan itama azkar ɗin tayi, sannan ahankali ta ɗago ta kalleshi, gaba ɗaya jikinta asanyaye yake, ga kuma wani irin fitinannen ƙaunarsa da kuma sha'awarsa da takeji, hannunta takai ta dafa kafaɗansa, sarai yajita amma sai yayi kaman ma baisan tanayi ba, ganin haka yasa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, ganin yana kallonta yasa taɗan sunkuyar da kanta, asanyaye tace.
"Ina kwana."
Kansa ya jinjina mata alaman.
"Lafiya." ƙoƙarin hawa wheelchair ɗinsa yasomayi, ganin haka yasa ta faɗa jikinsa, cikin sanyin guiwa tace.
"Dan Allah Abban Adeel kayi haƙuri, nima bansan meyasa nakejin wasu abubuwa akanku wani lokaci ba, kasan inasonka wannan dalilin yasa nakejin kishinka sosai araina, amman in sha Allah zan bari dan nacewa Mamana taita min Addu'a Allah ya yaye min kaima kaita min Addu'a kuma nima inayi." Idanunsa ya zuba mata, shi mutum ne me saurin fahimta da kuma uzuri, musamman ma ita da yasan cewa kishine ke ɗawainiya da zuciyarta. Ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da jinjina mata kai alaman.
"Shikenan komai ya wuce."
murmushi ta sakar masa tare da sake shigewa jikinsa, bakinta har rawa yake haka ta shiga kissing ɗinsa tako ta ina, sam bai hanata ba, dan baiso ya tauye mata haƙƙi, jikinta na rawa haka ta taimaka masa ya kwanta akan gado, bin bayansa itama tayi, tare da haɗe jikinsu waje ɗaya.
Duk wani abun da takeso baiƙi yi mata ba sabida shima yana buƙatarta, haka ya bata duk wani haƙƙinta dake kansa, after 22 minute gaba ɗaya jikinsa yayi weak, gajiya ne keta damunsa, da ƙyar ya iya tashi yayi wanka, fita yayi inda yaje ya gaishe da Umminsa, yana dawo wa kuwa nan kan gadon ya kwanta yana me da numfashi, ahaka har bacci ya ɗaukesa.
Ameena kuwa jin ranta take fari ƙal, wani annushuwa takeji acikin ranta, koda ta fito daga wankan, mai kawai ta shafa sannan ta yiwa Adeel wanka, saida ta fara shirya Adeel ɗin, kafun ta shirya kanta cikin kayanta na zuwa aiki.
Ganin Saifuddeen ɗin na bacci ne yasa taɗan ranƙwafo tare da yi masa kiss agoshinsa, Adeel na ɗauke akan kafaɗanta ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye sashin Ummi ta nufa, anan falo ta iske su azaune, yayinda Zaleeha ke zaune anan ƙasan sofa, tasha kyau cikin simple riga da sket ɗin dake jikinta, anutse ta gaishe da Ummi sannan Zaleeha ta miƙa hannu ta amshi Adeel, yau ko breakfast ma bata tsaya tayi ba, saboda taɗan makara.
kuma tana son yau ɗin ta keɓe da ƙawarta, Samira tasan zata ƙara kwantar mata da hankali kuma zata bata shawarwarin yadda zata samu ta yaƙi wannan zazzafan kishin ta zauna da ƴar uwarta lfy.