← Book details Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 154

Sashe 67

Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Fuska Malam Adam ya haÉ—e, cikin cushewar murya yace.
"Babu abun da zan iya miki, ba haƙurin kuma da zan bashi, abun da kika shuka shikike girba."
Daga haka yasa kai ya wuce cikin falon, baƙin nasa suka rufa masa baya.
Cikin kuka Zaleeha ta miƙe tsaye, duban Zakariyya tayi, sai kawai ta faɗa jikinsa ta saki wani irin fitinannen kuka, shima Zakariyyan kuka ya saka, tare da rungume ta, jin tausayinta yake kamar zai fasa masa zuciya.
Saida tayi kuka sosai kafun Zakariyya ya janyeta daga jikinsa, cikin sheshsheƙan kuka yace.
"Lokaci yana daɗa ƙurewa ki tafi kawai."
Juyawa yayi cikin sauri yana kuka ya nufi boys guater.
Cikin kuka haka ta nufi ƙofar fita daga gidan, kasancewar wajen gidan cike yake da jama'a, hakan yasa tabi ta ƙofar baya, tana cire ƙafanta daga cikin gidan tasaki wani irin kuka, haka ta miƙi titi, ta fiya take tana gauraya hanya, hawaye kuwa wani na koran wani akan fuskarta, gaba ɗaya ta fita hayyacinta, tayi wani wujiga-wujiga da ita, batasan inda zataje ba, bata da kowa aduniya bayansu da Adda Maryam na raye nema tasan ko duk zasu tsaneta ita bazata tsaneta ba, kuma tasan ko Ya Ameenu baya so zata bata mafaka kuma da Adda Maryam ta roƙa mata gafara wurin mahaifinsu, sukaɗaine gatan ta, gefe guda kuwa ga ƙafanta wanda taji ciwo har ta ɗan kumbura, ga wani busashshen jini da ya zauna akan fatarta.
Tafiya kawai take batare da ta san inda ta dosa ba, Jin an riƙe hijabinta ta baya yasanyata juyowa, Zakariyya ta gani hakan yasa ta fashe masa da wani sabon kuka, hannunta Zakariyya'n ya kama, suka ci gaba da tafiya, kasancewar unguwar tasu ta masu kuɗi ce, hakan yasa ko masu abun hawa irin na hayan nan basu cika shigowa sosai ba, sun ɗanyi tafiya, kafun Zakariyya ya hango wani mai adai-dai-ta sahu, wanda ya kawo wata mata, hannu Zakariyya yasa ya tare mai adai-dai-ta sahun, mai adai-dai-ta sahun na ƙarasowa gabansu, Zakariyya ya shiga cikin napep ɗin, tare da jawota itama ta shigo, har zuwa lokacin kuka take, sannan kuma yana riƙe da hannunta, duban me napep ɗin Zakariyya yayi asanyaye yace.
"Malam Shango estate zaka kaimu."
Kai me napep ɗin ya jinjina, sannan ya tada keken suka tafi. Ɗaura kanta akan kafaɗan Zakariyyan tayi, tare da sanya hannu ta dafe ƙirjinta dake mata zafi, nunfashinta nata ƙoƙarin yankewa saboda kukan da tayi har ta godewa Allah.
Koda suka ƙarasa Shango Estate ɗin anan ƙofar haɗaɗɗen sabon gidan Hajja Inna aka sauƙesu, Zakariyya ne ya ciro kuɗi ya bawa me napep ɗin, yana riƙe da hannun Zaleeha ya tura ƙofar gate ɗin gidan ya shiga, jin motsin buɗe ƙofa yasa me gadi dake kishingiɗe ya taso da sauri, ganin Zakariyya ne yasashi sakin numfashi ya koma ya zauna, Zakariyya kuwa yana riƙe da hannun Zaleehan har zuwa jikin bakin ƙofar da zata sadasu da babban falon gidan, key yaciro daga cikin aljihunsa ya buɗe ƙofar, sannan yaja Zaleehan suka shiga ciki. Akan kujera ya zaunar da ita, tare da ƙarasawa gaban fridge, goran ruwa me sanyi ya ɗauko sannan yazo ya aje mata agabanta, dubanta yayi cikin sanyi yace.
"Ki zauna anan, tunda Hajja Inna batanan tana can gida, wata ƙila gobe idan kika koma Baba Malam zaiyi haƙuri ya yafe miki".
Kuka ta fashe dashi tare da faÉ—awa jikin Zakariyya'n, cikin kuka tace.
"Na cuci kaina Zakariyya, nadasawa ƴan uwana baƙin ciki da ɓacin rai, nayi nesa da ku gashi har Adda Maryam tarasu batare da mun sake ganawa ba, lokacin dana tafi taƙira wayana, yafi sau 20 amma ban taɓa ɗagawa ba, kowa yaƙini sai bayan nayi wata biyu a can na fara amsa kiranta Zakariyya kai kaɗaine kaji tausayina, ya zanyi Zakariyya idan Baba Malam be yafemin ba, ya zanyi?".
Kukane yaci ƙarfinta sosai.
Zakariyya ma kukan yake. Zamewa yayi ya zauna tare da ɗaura kanta akan cinyarsa, ganin haka yasa ta takure jikinta waje ɗaya, nan tashiga rera sabon kuka, ita tanayi Zakariyya nayi, an rasa me rarrashin wani acikinsu, tayi kuka kam bana wasa ba, ita kanta bazata iya faɗin yaushe ne kuma tayaya ne, bacci ya ɗauketa ba, haka tayi bacci kanta nakan cinyan Zakariyya, yin baccin nata kuwa bairasa nasaba da irin kukan da tasha ta ƙoshiba, saboda yawan kuka nasanya mutum bacci, batare daya shiryawa hakan ba.
Ganin tayi bacci yasa Zakariyya zame jikinsa, pillown kujera ya ɗauka ya ɗora mata kanta akai, dubanta yayi, bacci take amma kuma sheshsheƙan kuka take tayi, hawayen da suka zubo daga cikin idanunsa ya goge, sannan ya tashi ya fita daga falon, kaitsaye ya koma gida.

Ita kuwa Zaleeha ko mintuna 20 batayi tana baccin ba, azabure tatashi, ganin bataga Zakariyyan ba, yasata dasa wani sabon kukan.
Tayi kukan tayi kukan harsaida taji kamar ma ba aduniya ta ke ba, ciwon kai kuwa ba'a magana, domin saboda tsabar ciwon da kanta keyi mata, har wani dishi dishi take gani

Haka dai ta zauna agidan idan tayi shiru yanzu anjima kuwa tayi kuka, da ƙyar ma ta iya tashi tayi sallah.
Tana nan tana kuka har dare ya rufa, yanda taga rana kuwa haka taga dare, ko lumshewa idanunta batayi ba, balle bacci ya É—auketa, batun ciwon kai kuwa sai abun da yayi gaba, dan kuwa zuwa yanzu harwani ji take kaman kannata ya kumbura, saboda tsabar ciwo da yakeyi mata.
Haka ta kwana azaune tana karatu qur'an da kuka har gari yayi haske.
Nan dai daga falon babu inda ta gusa, banda toilet da ta shiga ta ɗauro alwala, tana nan zaune Zakariyya ya buɗe kofar falon ya shigo, ganin yanda idanunta suka kumbura kana sukai jajur yasa shi ɗan zaro idanunsa, cikin sauri ya ƙaraso cikin falon, agabanta ya zauna tare da aje ƴar ƙaramar kulan dake hannunsa, hankalinsa amatuƙar tashe yace.
"Kwana kikayi kina kuka ko?."
Yafaɗa yana me sanya hannunsa ya share mata hawayen dake kan fuskarta, kulan da ya shigo dashi ya buɗe, soyayyen dankali da ƙwai ne, sai sauce ɗin egg, turo mata kulan gabanta yayi, cikin tausayawa yace.
"Waima rabonki da abinci tun yaushe ne Adda Zaleeha? kici wannan abincin kinji." Kanta ta girgiza masa, cikin da shashshiyar muryarta tace.
"Banajin zan iyacin wani abu Zakariyya, bana buƙatar komai yanzu a duniya sai yafiyan Baba Malam, tayaya kake tunanin zan iya sakawa cikina abinci a airin wannan halin da nake ciki? bazan iya ba, ka kaini kawai naje nasake bawa Baba Malam haƙuri, hakanne kaɗai zaisa naji sanyi araina."
Hawayen tausayinta ya share, sannan ya kamo hannunta, cikin sanyin murya yace.
"Taso muje." Nan ta miƙe yana riƙe da hannunta yazama kaman shine yayanta ita kuma ƙanwarsa, haka suka fita daga gidan, tafiya kaɗan sukayi suka samu napep.
Chapter 67 · 0% Book details