Sashe 79
Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saifuddeen kuwa sanin cewa yau ne zaikai Zaleehan ta bawa Baba Malam haƙuri, yasa shi barin gidan ma gaba ɗaya, bashi ya dawo ba kuwa sai wajajen sallan azahar. Kaitsaye ɓangaren sa ya wuce, wanka yayi sannan ya shirya kansa cikin wata ɗanyar getzner me masifar kyau da tsada, kasancewar getzner ɗin na sa nada kalan coffee, shi yasa ya matuƙar amsar farar fatar jikinsa, yayinda akayiwa getzner ɗin dinkin half jumper da kuma wandon pencil, wata murzazziyar hula mai kalan light coffee ya ɗaura akansa, hatta takalmin dake ƙafansa me kalan dark coffee ya sanya, yayi kyau matuƙa ga kuma apple touch watch ɗinsa dake ta faman ɗauke ido, tabbas Saifuddeen yayi kyau ƙwarai, dan bazaka kallesa sau ɗaya ka ɗauke idanunka ba, haɗaɗɗiyar sajen dake kwance akan fuskarsa kuwa ta kwanta tayi lub lub, jajayen laɓɓansa kuwa sai sheƙi suke, ga wanda baisansa ba zaice wani abun ya shafa musu, amma ko ɗaya haka yake, sirrin kyau ajininsa yake. Wayoyinsa ya zura acikin aljihun rigarsa, sannan kai tsaye ya danna madannin wheelchair ɗinsa ya fita daga cikin ɗakin, sai baza ƙamshi yake.
Anan compound ɗin gidan kuwa, sanin cewa zasu fita yasa Sule driver tuni ya gama tsabtace motar da zasu fita da ita ɗin, wata haɗaɗɗiyar mercedes benz ce me kyau, sabuwa dal sai sheƙi take tana ɗauke ido, fitowarsa compound ɗin gidan ne, ya hango Sule driver, hakanne ya sashi ƙarasawa wajen Sule driver'n, cikin kulawa Sule driver'n, yayi masa barka da fitowa, da kai ya amsa masa kamar koda yaushe. Buɗe murfin motar yayi, nan ɓangaren gidan baya ya shiga, dan dama shi baicika zama agaba ba, akomansa yafison sirri, musamman ma yanzu da yake mazaunin jami'in sirri, yana shiga ya jawo murfin motar ya rufe, wayarsa ya laluɓo daga cikin aljihunsa, cikin text message ya shiga, ataƙaice ya rubuta cewa. _"Ummi kice mata tayi sauri, dan tana ɓatamin lokaci."_
yana gama rubutun yayi sending, tare da maida wayan ya ajiye, laptop É—insa ya É—auko yana dannawa.
Ummin kuwa dama tuntuni tasa Zaleehan ta shirya, tsab cikin ɗaya daga cikin sabin rigunan da tasa aka sayo mata, duk da cewa akwai yanayin damuwa mai yawa akan fuskarta, amma hakan baihana kayan yi mata kyau ba, saboda doguwar rigace irin abaya ɗinnan ta larabawa me kyau, yayinda ta yane kanta da ɗan kwalin kayan, wanda ya sauƙo har zuwa ƙirjinta.
Tunda ta gama shiryawan take zaune abakin gado, gaba ɗaya ta rasa mekeyi mata daɗi, tsoro da fargaba ne suka cika zuciyarta, ga kuma yawan faɗuwar gaba da takeji, ƙirjinta ne ke wani irin duka, gaba ɗaya atsorace take, koda tayi ƙoƙarin bawa kanta ƙarfin guiwa kuwa hakan baya yiwuwa, saboda fargaban daya cika zuciyarta.
"Me zata tarar agidan Baba Malam? wata ƙila ma yaƙi yafe mata ya kuma sake koranta." Wannan abun shine abun daya tsaya mata arai, duk yanda taso jin sauƙi azuciyarta abun yaci tura, hakanne yasa kawai ta fashe da kuka, dai-dai lokacin Ummi ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, ganin Zaleehan na kuka yasa ta ɗan dafe kanta, sam batason yawan kukan na Zaleeha, jin an shigo ɗakin ne yasata ɗago kanta, ganin Ummi yasa cikin hanzari ta tashi tare da ƙarasa gareta, cikin muryarta dake rawa tace.
"Wallahi Ummi tsoro nakeji , idan mukaje Baba Malam ya koreni sannan yaƙi yafemin ya zanyi? shikenan nikam rayuwata tana cikin garari." taƙare maganar hawaye na silalowa daga cikin idanunta, Ɗan bubbuga bayanta Ummi tayi, cikin son kwantar mata da hankali tace. "Kada ki faɗi haka Zaleeha, share hawayenki, insha Allah Baba Malam zai yafe miki, nasan nanda ƴan wasu awanni zaki kasance cikin farincikin yafiyar Baba Malam, yanzu taho muje Hammanku nacan mota yana jiranki."
Idanunta ta ɗan lumshe, ahankali taɗan gƴaɗa kanta kamar wata ƙaramar yarinya, haka hawaye ke tsiyaya daga cikin cikin idanunta, hannunta Ummi ta kama suka fice daga cikin ɗakin, anan falo suka samu Raleeya tsaye. Ummi na riƙe da hannunta, yayinda Raleeya ka biye dasu abaya, haka suka fito zuwa compound ɗin gidan, har jikin motar tasa suka ƙarasa, still hawaye Zaleeha take, Ummi kuwa na riƙe da hannunta, murfin motar Ummi ta buɗe tare da sanya Zaleehan aciki, ganin ankawo masa ita kusa dashi ne, ya sashi ɗago kansa ya dubi Ummi, amatuƙar shagwaɓe ya ɓata fuska, cikin body language ɗinsa yace wa Ummi da ke kallonsa,
"Ni Ummi me yasa zaki kawomin ita kusa dani, baganan gidan gaba ba, dan Allah Ummi kisata agaba, ni banason ta zauna akusa dani." Daƙuwa Ummi tayi masa, tare da kama haɓanta, sosai take mamakinsa itakam, musamman ma yanzu da ya ari halin da ba nasa ba ya yafa. Sake ƙara shagwaɓe fuska yayi, cikin ransa yake ta ƙunƙuni, wanda ko bakin zuciyarsa bai je ba, dan duk abun da yakeyi pretending ne kawai, sam baisa azuciyar sa ba.
Allah ya kiyaye Ummi tayi musu sannan Sule driver yaja motar suka fita daga gidan. Saida su Ummi suka ga, fitansu kafun suke komawa cikin gida.
Koda tafiyan nasu tayi nisa, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi, saboda sanyin AC'n dake tashi acikin motar yaso ya yiwa jikinta yawa, gaba ɗaya bata wani cikin nutsuwarta, domin suna fita daga cikin gidan na Ummi taji gaba ɗaya zuciyarta ya karye, haka hawaye keta fita daga cikin idanunta, yana sauƙa akan fuskarta, daga gefe guda kuwa daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya gauraye numfashinta, haka take ta sakin sheshsheƙan kuka ahankali.
Saifuddeen kuwa, duk da kasancewar bai ɗago kai ya kalleta ba, amma duk wani abu da takeyi, yana lure da ita, amma azahirance yi yayi kamar baisan da wata halitta agefensa ba, itakuwa gaba ɗaya damuwa ya cika mata zuciya, hakanan taji tana son kallonsa, amma wani irin abu me kama da tsoro ya hanata kallon sa, wanda kuma tunda take dashi bata taɓa jin irin hakan a dangane dashi ba.
Cusa kanta atsakankanun cinyoyinta tayi, tana me sake sakin sheshsheƙa, can cikin zuciyarta kuwa sunan Allah. take ta faman ambato.
Shikuwa Saifuddeen text message ya turawa Dirankadi kan cewa. "Yana neman al'farma idan yana gida, yanaso yazo ya ɗaukesa, akan maganan Zaleeha, dan suje su bawa Baba Malam haƙuri, saboda yana fushi da'ita sosai, sannan kuma idan yaje shi kaɗai baisan mezai faɗawa Baba Malam ɗin ba, wataƙila ma balallai Baba Malam ɗin ya sauraresu ba."
Cikin fahimta kuwa Dirankadi yace masa. "Babu damuwa Sai sunzo É—in, dama fita zaiyi, amma zaijirayi zuwansu.."
Sosai kuwa Saifuddeen yaji daɗi, hakan yasa ya ɗan taɓa Sule driver, Juyowa Sule driver'n yayi yana fuskantar sa, miƙawa Sule driver'n wayarsa wanda yayi rubutu akan screen ɗin Yayi,
koda Sule driver ya karanta saƙon jinjina kansa yayi, cikin kulawa yace.
"Angama ranka ya daÉ—e."
Nan take kuwa ya karkata akalar motar suka nufi gidansu Ishaq.
Koda suka ƙarasa gidan nasu Ishaq kuwa, nan suka samu harma Dirankadi'n ya shirya, su kawai yake jira, koda Saifuddeen ɗin ya buƙaci da Dirankadi'n ya shiga motarsa, cewa yayi dashi.
"A'a zaije da tasa motar, saboda daga gidan su Zaleehan zai wuce wajen aiki, saboda haka amotarsa zai tafi." Saifuddeen ne yayiwa Sule driver, alamar cewa ya yiwa Zaleehan magana tazo ta gaida Dirankadi ɗin, haka kuwa akayi Sule driver da kansa ya buɗe mata murfin motar ta fito, har ƙasa kuwa ta durƙusa ta gaishe da Dirankadi'n. Fuska asake ya amsa mata, tare dayi mata ta'aziyyan rasuwar Adda Maryam, haka ta amsa masa cikin yanayin sanyi, dan aɗan kukan nan da tayi, har muryarta ta dashe.
Haka dai Dirankadi ya shiga motarsa, itakuma Zaleehan ta koma motar su ta zauna tare dayin jigum, saboda zuciyarta dake ƙara tsinkewa, Nan dai suka kama hanyar gidansu Zaleehan, inda motar Dirankadi ce agaba. Basuyi wani tafiya me nisaba suka iso gidan, jin motar ta tsaya ne yasata ɗago kanta amasifar tsorace, aikuwa ganinta acikin compound ɗin gidansu yasa gaba ɗaya duk wani kuzarinta ya kau, yanayin yanda zuciyarta ke bugawa kuwa, idan kaji zakai tunanin cewa faso ƙirjinta zatayi ta fito waje, sosai jikinta ya ɗauki rawa, tsoro ne yagama lulluɓeta, makomarta kawai take tunawa. Dirankadi ne yafara fitowa daga cikin motarsa, ƙarasowa jikin motar Saifuddeen ɗin yayi, cikin kulawa yace. "Saifuddeen ku zauna kada ku fito, duk yanda ake ciki zan maka text sai ku shigo."
Kai Saifuddeen ya jinjina masa alamar gamsuwa, Nan Dirankadi ya nufi cikin gidan, kaitsaye ɓangaren Baba Malam ya nufa.
Acikin falon Baba Malam kuwa, shi da Ya Ahmad, da kuma Malam Adam ne zaune, gefe dasu kuwa Ya Ameenu ne wanda ayanzu ya zama kamar wani mutum mutumi, komai nasa ya sanja, ya zama wani mutum me sanyi, magana kuwa inbanda "Eh, da kuma A'a."
ba bu abun da yake iya fitawo daga bakinsa, sosai mutuwar Adda Maryam É—in ya maidashi wani silently, hakanne ma yasa gaba É—aya dangim suke masifar jin tausayinsa.
Dirankadi ne ya shigo cikin falon bakinsa É—auke da sallama, amutunce su Baba Malam da kuma Malam Adam suka amsa masa, cikin mutum tawa Baba Malam ya taso ya tarosa, tare da basa hannu sukayi musabaha, kujera Baba Malam ya nuna masa, zama yayi tare da bawa su Yaya Ameenu hannu suka gaisa, sake musu sabon gaisuwa yayi, tare da sake bawa Baba Malam hannu suka gaisa amutunce, hira kaÉ—an sukayi, kafun Dirankadi ya gyara zamansa, cikin nutsuwa ya dubi Baba Malam, a mutumce yace.
"Kayi haƙuri Malam Bashir, domin ba haka kawai nake tafe ba, alfarma muka zo nema awajenka, wanda kuma nake saka ran cewa Insha Allah, zaka mana ita."
Anan compound ɗin gidan kuwa, sanin cewa zasu fita yasa Sule driver tuni ya gama tsabtace motar da zasu fita da ita ɗin, wata haɗaɗɗiyar mercedes benz ce me kyau, sabuwa dal sai sheƙi take tana ɗauke ido, fitowarsa compound ɗin gidan ne, ya hango Sule driver, hakanne ya sashi ƙarasawa wajen Sule driver'n, cikin kulawa Sule driver'n, yayi masa barka da fitowa, da kai ya amsa masa kamar koda yaushe. Buɗe murfin motar yayi, nan ɓangaren gidan baya ya shiga, dan dama shi baicika zama agaba ba, akomansa yafison sirri, musamman ma yanzu da yake mazaunin jami'in sirri, yana shiga ya jawo murfin motar ya rufe, wayarsa ya laluɓo daga cikin aljihunsa, cikin text message ya shiga, ataƙaice ya rubuta cewa. _"Ummi kice mata tayi sauri, dan tana ɓatamin lokaci."_
yana gama rubutun yayi sending, tare da maida wayan ya ajiye, laptop É—insa ya É—auko yana dannawa.
Ummin kuwa dama tuntuni tasa Zaleehan ta shirya, tsab cikin ɗaya daga cikin sabin rigunan da tasa aka sayo mata, duk da cewa akwai yanayin damuwa mai yawa akan fuskarta, amma hakan baihana kayan yi mata kyau ba, saboda doguwar rigace irin abaya ɗinnan ta larabawa me kyau, yayinda ta yane kanta da ɗan kwalin kayan, wanda ya sauƙo har zuwa ƙirjinta.
Tunda ta gama shiryawan take zaune abakin gado, gaba ɗaya ta rasa mekeyi mata daɗi, tsoro da fargaba ne suka cika zuciyarta, ga kuma yawan faɗuwar gaba da takeji, ƙirjinta ne ke wani irin duka, gaba ɗaya atsorace take, koda tayi ƙoƙarin bawa kanta ƙarfin guiwa kuwa hakan baya yiwuwa, saboda fargaban daya cika zuciyarta.
"Me zata tarar agidan Baba Malam? wata ƙila ma yaƙi yafe mata ya kuma sake koranta." Wannan abun shine abun daya tsaya mata arai, duk yanda taso jin sauƙi azuciyarta abun yaci tura, hakanne yasa kawai ta fashe da kuka, dai-dai lokacin Ummi ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, ganin Zaleehan na kuka yasa ta ɗan dafe kanta, sam batason yawan kukan na Zaleeha, jin an shigo ɗakin ne yasata ɗago kanta, ganin Ummi yasa cikin hanzari ta tashi tare da ƙarasa gareta, cikin muryarta dake rawa tace.
"Wallahi Ummi tsoro nakeji , idan mukaje Baba Malam ya koreni sannan yaƙi yafemin ya zanyi? shikenan nikam rayuwata tana cikin garari." taƙare maganar hawaye na silalowa daga cikin idanunta, Ɗan bubbuga bayanta Ummi tayi, cikin son kwantar mata da hankali tace. "Kada ki faɗi haka Zaleeha, share hawayenki, insha Allah Baba Malam zai yafe miki, nasan nanda ƴan wasu awanni zaki kasance cikin farincikin yafiyar Baba Malam, yanzu taho muje Hammanku nacan mota yana jiranki."
Idanunta ta ɗan lumshe, ahankali taɗan gƴaɗa kanta kamar wata ƙaramar yarinya, haka hawaye ke tsiyaya daga cikin cikin idanunta, hannunta Ummi ta kama suka fice daga cikin ɗakin, anan falo suka samu Raleeya tsaye. Ummi na riƙe da hannunta, yayinda Raleeya ka biye dasu abaya, haka suka fito zuwa compound ɗin gidan, har jikin motar tasa suka ƙarasa, still hawaye Zaleeha take, Ummi kuwa na riƙe da hannunta, murfin motar Ummi ta buɗe tare da sanya Zaleehan aciki, ganin ankawo masa ita kusa dashi ne, ya sashi ɗago kansa ya dubi Ummi, amatuƙar shagwaɓe ya ɓata fuska, cikin body language ɗinsa yace wa Ummi da ke kallonsa,
"Ni Ummi me yasa zaki kawomin ita kusa dani, baganan gidan gaba ba, dan Allah Ummi kisata agaba, ni banason ta zauna akusa dani." Daƙuwa Ummi tayi masa, tare da kama haɓanta, sosai take mamakinsa itakam, musamman ma yanzu da ya ari halin da ba nasa ba ya yafa. Sake ƙara shagwaɓe fuska yayi, cikin ransa yake ta ƙunƙuni, wanda ko bakin zuciyarsa bai je ba, dan duk abun da yakeyi pretending ne kawai, sam baisa azuciyar sa ba.
Allah ya kiyaye Ummi tayi musu sannan Sule driver yaja motar suka fita daga gidan. Saida su Ummi suka ga, fitansu kafun suke komawa cikin gida.
Koda tafiyan nasu tayi nisa, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi, saboda sanyin AC'n dake tashi acikin motar yaso ya yiwa jikinta yawa, gaba ɗaya bata wani cikin nutsuwarta, domin suna fita daga cikin gidan na Ummi taji gaba ɗaya zuciyarta ya karye, haka hawaye keta fita daga cikin idanunta, yana sauƙa akan fuskarta, daga gefe guda kuwa daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya gauraye numfashinta, haka take ta sakin sheshsheƙan kuka ahankali.
Saifuddeen kuwa, duk da kasancewar bai ɗago kai ya kalleta ba, amma duk wani abu da takeyi, yana lure da ita, amma azahirance yi yayi kamar baisan da wata halitta agefensa ba, itakuwa gaba ɗaya damuwa ya cika mata zuciya, hakanan taji tana son kallonsa, amma wani irin abu me kama da tsoro ya hanata kallon sa, wanda kuma tunda take dashi bata taɓa jin irin hakan a dangane dashi ba.
Cusa kanta atsakankanun cinyoyinta tayi, tana me sake sakin sheshsheƙa, can cikin zuciyarta kuwa sunan Allah. take ta faman ambato.
Shikuwa Saifuddeen text message ya turawa Dirankadi kan cewa. "Yana neman al'farma idan yana gida, yanaso yazo ya ɗaukesa, akan maganan Zaleeha, dan suje su bawa Baba Malam haƙuri, saboda yana fushi da'ita sosai, sannan kuma idan yaje shi kaɗai baisan mezai faɗawa Baba Malam ɗin ba, wataƙila ma balallai Baba Malam ɗin ya sauraresu ba."
Cikin fahimta kuwa Dirankadi yace masa. "Babu damuwa Sai sunzo É—in, dama fita zaiyi, amma zaijirayi zuwansu.."
Sosai kuwa Saifuddeen yaji daɗi, hakan yasa ya ɗan taɓa Sule driver, Juyowa Sule driver'n yayi yana fuskantar sa, miƙawa Sule driver'n wayarsa wanda yayi rubutu akan screen ɗin Yayi,
koda Sule driver ya karanta saƙon jinjina kansa yayi, cikin kulawa yace.
"Angama ranka ya daÉ—e."
Nan take kuwa ya karkata akalar motar suka nufi gidansu Ishaq.
Koda suka ƙarasa gidan nasu Ishaq kuwa, nan suka samu harma Dirankadi'n ya shirya, su kawai yake jira, koda Saifuddeen ɗin ya buƙaci da Dirankadi'n ya shiga motarsa, cewa yayi dashi.
"A'a zaije da tasa motar, saboda daga gidan su Zaleehan zai wuce wajen aiki, saboda haka amotarsa zai tafi." Saifuddeen ne yayiwa Sule driver, alamar cewa ya yiwa Zaleehan magana tazo ta gaida Dirankadi ɗin, haka kuwa akayi Sule driver da kansa ya buɗe mata murfin motar ta fito, har ƙasa kuwa ta durƙusa ta gaishe da Dirankadi'n. Fuska asake ya amsa mata, tare dayi mata ta'aziyyan rasuwar Adda Maryam, haka ta amsa masa cikin yanayin sanyi, dan aɗan kukan nan da tayi, har muryarta ta dashe.
Haka dai Dirankadi ya shiga motarsa, itakuma Zaleehan ta koma motar su ta zauna tare dayin jigum, saboda zuciyarta dake ƙara tsinkewa, Nan dai suka kama hanyar gidansu Zaleehan, inda motar Dirankadi ce agaba. Basuyi wani tafiya me nisaba suka iso gidan, jin motar ta tsaya ne yasata ɗago kanta amasifar tsorace, aikuwa ganinta acikin compound ɗin gidansu yasa gaba ɗaya duk wani kuzarinta ya kau, yanayin yanda zuciyarta ke bugawa kuwa, idan kaji zakai tunanin cewa faso ƙirjinta zatayi ta fito waje, sosai jikinta ya ɗauki rawa, tsoro ne yagama lulluɓeta, makomarta kawai take tunawa. Dirankadi ne yafara fitowa daga cikin motarsa, ƙarasowa jikin motar Saifuddeen ɗin yayi, cikin kulawa yace. "Saifuddeen ku zauna kada ku fito, duk yanda ake ciki zan maka text sai ku shigo."
Kai Saifuddeen ya jinjina masa alamar gamsuwa, Nan Dirankadi ya nufi cikin gidan, kaitsaye ɓangaren Baba Malam ya nufa.
Acikin falon Baba Malam kuwa, shi da Ya Ahmad, da kuma Malam Adam ne zaune, gefe dasu kuwa Ya Ameenu ne wanda ayanzu ya zama kamar wani mutum mutumi, komai nasa ya sanja, ya zama wani mutum me sanyi, magana kuwa inbanda "Eh, da kuma A'a."
ba bu abun da yake iya fitawo daga bakinsa, sosai mutuwar Adda Maryam É—in ya maidashi wani silently, hakanne ma yasa gaba É—aya dangim suke masifar jin tausayinsa.
Dirankadi ne ya shigo cikin falon bakinsa É—auke da sallama, amutunce su Baba Malam da kuma Malam Adam suka amsa masa, cikin mutum tawa Baba Malam ya taso ya tarosa, tare da basa hannu sukayi musabaha, kujera Baba Malam ya nuna masa, zama yayi tare da bawa su Yaya Ameenu hannu suka gaisa, sake musu sabon gaisuwa yayi, tare da sake bawa Baba Malam hannu suka gaisa amutunce, hira kaÉ—an sukayi, kafun Dirankadi ya gyara zamansa, cikin nutsuwa ya dubi Baba Malam, a mutumce yace.
"Kayi haƙuri Malam Bashir, domin ba haka kawai nake tafe ba, alfarma muka zo nema awajenka, wanda kuma nake saka ran cewa Insha Allah, zaka mana ita."