← Book details Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 154

Sashe 11

Nakasa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

a cikin motocin kuwa text Saifuddeen ya turawa Aziz na numbers É—in motocin da suke zargi,
amsa ya tura mishi da cewa.
"Ba matsala duk nabisu na sace iskar tayun bayansu, sai ta motar dake kusa damu nan na barta amman naja tamu mutar na matsesu basuma da damar motsawa, na kuma gayawa Ahmad ya fito cikin motar taku yayiwa amarya jagora ,zakaga gefen hagu da daman ku akwai mata uku uku sojojine cikin farin kaya."
murmushi mai cike da nasara Saifuddeen yayi.

Shi kuwa Ahmad yana ganin fitowarsu yayi saurin ƙarasawa garesu, shiyayi musu jagora zuwa motar da za'a sanya amarya wato wanda Saifuddeen ke ciki, shida kansa Ahmad ya buɗe mata ƙofar motar, Aunty Lubna ne ta sata cikin motar, ganin Saifuddeen zaune acikin motar yayinda hankalinsa gaba ɗaya kekan laptop ɗinsa, yasanyata sakin murmushi, lallai tajinjinawa ƙauna irin na Saifuddeen da sauri ta kamo hannun goggo Maryama dake shirin shiga tace.
"Tsaya Goggo angon yana ciki, shi yazo É—aukan amaryarshi da kanshi."
Ahmad ne ya É—anyi murmushi tare da cewa.
"Sabida tsarone babbar yaya ba don tsoro ba."
dariya sukayi cikin happy Balkeesu ne tay kamar bata jisuba tasoma ƙoƙarin shiga motar, da sauri ta ɗan dawo da baya ganin Saifuddeen hakimce acikin motar haibarsa da kimarsa da kwarjinta sun bugi zuciyarta shakkarshi mai yawa ta rufeta, bisa ɗole taja da baya,
Ya Ahmad da Adda Maryam ma dake gefensu murmushin jin daɗi sukayi sabida sunga tarin so da kulawar Saifuddeen a kan ƙanwar tasi, dan ya gayawa ya Ahmad duk abinda ke faruwa na son sace amarya, ya faɗa mishine da kashedin karfa wasu suzo su basu amarya su jira sai sunzo da kansu
.Su Bilkeesu kuwa bisa dolensu suka shiga wata mota ta daban.

Ahankali duka motocin ke tafiya a jere a jere.

Sosai hankalin yaran Dalla yayi matuƙar tashi ganin duk motocin sun fice sun barsu sai nasu kawai ,nasun kuma duk sunyi faci, sai ƙwaya ɗayar nan,
koda suka shaidawa Dalla hankalinshi yayi masifar tashi to waya gano shirinsu, waya ɓata mishi tsarin sace matar wannan gurgun kurman,
dole a tsorace suka fita da motocin a haka suka lallaɓa suka isa wurin mai sa iska,
yayinda duk abinda sukeyi Saifuddeen na ganinsu a system ɗinshi ta sanadin na'urar bibiya da ya bawa Hayatuddeen ya liƙa musu a jikin motar da take irin tasa.

Tunda tashiga cikin motar ta cusa kanta atsakankanun cinyoyinta kuka take sosai har kaman zata shide, samma batasan dawa take tare ba acikin motarba, ta gefen ido yake kallonta, hakan ne ya tabbatar mishi kuka takeyi.
Sosai yakejin kukan nata na taɓa masa zuciya da jiki dan jikinshi ya bashi kuka take ga kuma alamu yana ganin yadda ta takure tana shessheƙa, saidai kuma tun shigowarta motar ko ɗago kansa baiyi ba, gaba ɗaya ya maida idanunsa akan system na laptop ɗinsa, saidai kuma duka hankalinsa na gareta, ɗan ɗagowa yayi tare da numfasawa, cikin nutsuwa ya rufe laptop ɗin bayan ya saita abinda zai naɗe mishi diddigin yaran Dalla sai dai akasi kaɗan da aka samu lokacin da yasa yayi ƙarancin binsu har inda zasu isa,
ido ya zuba mata cikin jin tausayinta yasan halinda mata kan shiga lokacin da suke barin gidan iyayensu zuwa gidan mazansu, dan bai mance auren Raihana ba da Adda Rahma ke badu labarin daga cikin gombe har suka isa Kaduna Raihana bata bar kukaba sai ta É—anyi shiru sai kuma taci gaba har suna mata dariya wai hutawa takeyi bare da dama sun san Raihana saurin kuka gareta,
ido ya lumshe tare da buÉ—esu ya zuba mata su, ahankali ya sanya duka hannuwansa akan kafaÉ—unta, É—an É—agota yayi kaÉ—an,
ita kuwa Zaleeha jin anriƙe kafaɗunta ne yasanyata yin tunanin Aunty Lubna ce, hakan yasa batare data buɗe idanunta ba, haka bata yaye mayafin dake kanta ba, tafaɗa jikinsa, sakin sabon kuka tayi tare da sanya hannuwanta duka ta zagaye cikinsa, cikin kukan fitar hayyaci tace.
"Dan Allah Aunty Lubna ku maidani gida, wallahi bana son barin gida,karku kaini cikin bare ban sansuba basu sanniba, wlh bana sonsa, natsanesa, ko ganinsa banason yi, mutuwa zanyi matuƙar kuka kaini gidansa, dan Allah Aunty ki taimakeni, taƙare maganar tana me cusa kanta cikin ajikinsa.
Ahankali ya lumshe idanunsa, tare da sanya duka hannuwansa ya ƙara jawota jikinsa, wasu irin tagwayen ajiyar zuciya ya rinƙa sauƙewa take wani irin zazzafan shauƙi ya shiga ratsa zuciyarsa da jikinsa.
Jin wani masifaffen ƙamshi mai azabar daɗin ji da shaƙa wanda bata taɓa jin irinsa ba na shiga cikin hancinta wanda ba ƙamshin Aunty Lubna bane yasanyata ɗan jan jikinta baya, ahankali ta ɗago kanta, azabure tawani irin jan jikinta baya, kallon fuskarsa da yayi masifar kyau wanda ita da kanta sauda ta ganshi kamar balarabe, ganin shinne yasanya komai ya ƙwace mata, wani irin baƙin ciki ne ya cika zuciyarta take tasaki kuka tare da maida kanta ƙasa, wani irin tafasa zuciyarta keyi mata.
Ƙawataccen murmushi Saifuddeen yayi tare da maida bayansa ya jingina da jikin kujeran, lumshe idanunsa yayi yayinda yake shaƙan dadaaɗan ƙamshinta, runguman da tayi masa yasanya yaji wani abu na tsargawa ta cikin jikinsa, sam baiyi yunƙurin sake taɓa ta ba, haka kuma bai hanata kukan da takeyi ba, ahaka har suka iso cikin katafaren gidannasu.

Nan fa Æ´an kawo amarya kowa yacika da mamakin haÉ—uwar gida, masu son auren sai masha Allah kawai suketa cewa,
Goggo Maryama ce ta riƙeta inda tace tashiga gidan da ƙafar dama haɗi da bismillah, ranta aƙuntace haka tayi bismillah duk da cewa bawai ganin gabanta takeyi ba, zuwa yanzu tama daina kukan, jira kawai take Saifuddeen yace da ita wani abu ta sauƙe masa kwandon bala'i.
Baƙaramin mamaki kyan ɓanagaren na Zaleeha ƴan uwanta sukayi ba, don kuwa komai yayi harma ya zarcewa tunaninsu, koda Balkeesu taga uwar dukiyar da aka kashewa Zaleeha, dakuma irin tsaruwan gidan al'afarma part ɗin nata, saida taji wani abu kaman mashi ya caki zuciyarta, sam bata ɗauka haɗuwar wajen zaikai har haka ba.
Acan cikin É—aki aka zaunar da Zaleeha.
Sannu ahankali jama'a ke watsewa don nan da wasu awanni za a gudanar da diner, Rasheda ma tatafi don zuwa taho da me meckup ɗin da zatayiwa amarya, hakanne yabawa Balkeesu daman ƙara hurewa Zaleehan kunne, sam tace da ita tadaina asaran hawayenta, tabari idan hidiman biki ya kammala plant ɗinsu da suka haɗa sai ya fara aiki, sosai Zaleeha kuwa tahau kan maganan na Balkeesu ta zauna wanda zugan bilkeesu da asirin mma yazo iri ɗaya.

Kamar yanda al'adan Gombawa yake aduk sanda aka kawo amarya gidansu ango, to fa akan tarbesu da kayan ciye ciye dana shaye shaye, hakance takasance agidansu Saifuddeen dan kuwa sosai aka cikawa su Zaleeha kayan ciye ciye, komai cikin wadata akayisa, abun ma har mamaki yake bawa wasu daga cikin dangin Zaleeha don kuwa kuɗi sosae gidan su Saifuddeen ɗin ke kashewa wajen ƙawata komai nasu, kamar basajin ciwon kuɗin.
Ya Habu kuwa da ya Aminu har cikin É—akin suka shigo suka gargaÉ—eta akan batun diner muddin tayi abinda zai kunya tasu Habu yace.
"Wlh rabaki gida biyu zanyi kin sanni ba mutun cine da niba, ni ba irin ya Ahmad bane."
Dolenta ta nitsu koda suka tafi ko motsin kirki bata kuma yiba.

Kasancewar ƙarfe 8:00 pm dai-dai za a fara gudanar da diner'n hakan yasa amarya Zaleeha tana idar da sallan isha aka soma tsantsara mata meckup akan fuskarta, musamman aka ɗauko ƙwararriyar meyin meckup inda tazo ta baje basirarta akan fuskar Zaleeha, wani irin haɗaɗɗen meckup aka tsantsara akan fuskar Zaleeha wanda yayi bala'in fito da kyawun fuskarta,
dakanta ta zura wata haɗaɗɗiyar fitted weeding gown mai azabar kyau, jifa jifa aka sanya ratsin fari ajikin rigar, rigace irin doguwa ɗinnan wanda har sharan ƙasa take, sosai rigan takama jikinta tazauna ɗas, inda gefe da gefen waist ɗin rigar aka sanya wani irin yadi mai sharara wanda yake da masifar tsawo, haɗuwar rigar ya zarce misali, musamman ma yanda ya zauna ajikinta yayi ɗas, tabbas ko ba a faɗaba kallo ɗaya zakaiwa rigar kasan da cewa taja maƙudan kuɗaɗe wajen tsarata,
haɗaɗɗen ɗaurin ɗan kwali irin na amare aka kafa mata akanta, bayan anyi parking dogon gashinta atsakiyar kanta, inda aka sanya mata wani haɗaɗɗen sarƙan gold mai tsananin kyau da tsada, dagakan ɗankunne har zoben dake hannunta duka na gold ne, masu masifar tsada da kyau, wani irin takalmi mai masifar tsini ta sanya aƙafafunta, bakaɗanba tayi kyau nafitar hankali, harwani ɗauke ido take, turare kuwa kamar ɓarinsa akayi ajikinta, sosai Zaleeha tayi kyau cikin shigarta ta diner, inda kowa ke yabawa da tsantsar kyawun da Allah yayiwa Zaleeha, ita kanta Zaleeha tasan cewa ayau ɗin tayi kyau.

Gombe International Hotel

Sosai aka ƙawata babban falon wanda ananne za a gudanar da diner ɗin, anyiwa wajen ƙawa naban mamaki tare da haɗaɗɗen decoration na peach and white, sannan kuma daga sama adon decoration blue akayi mai masifar kyau, gurin acike yake da jama'a , inda kowani team da kalan shigarsu, gabaki ɗaya abokan Saifuddeen shigar shadda blue colour ce ajikinsu, inda gefe guda kuwa su Hayatuddeen ke sanye da peach colour ɗin shadda, daga gefe kuwa su Adda Rahama suka tsantsara ado cikin wani tsadadden farin lace mai adon blue, gurin tuni yacika da jama'a zuwan ango da amarya kawai ake jira.

Ɓangaren Zaleeha kuwa ana gama tsantsara mata kwalliya Rasheeda ta sanar dasu zuwan ango, hakan yasa aka ƙara ƙawata mata adon nata, Balkeesu da Rasheeda na riƙe da ƙasan rigarta dake jan ƙasa suka nufi compound ɗin gidan.

Saifuddeen ne zaune acikin wata rantsatstsiyar mota yabala'in yin kyau acikin farar shadda mai peach colour ɗin aiki dake jikinsa, yayi kyau fiye daduk wani tunani mai tunani, idanunsane suka sauƙa akan tauraruwar amaryarsa wanda tsananin kyawun da tayi yaso zautar dashi.
A hankali suke taku tamkar wahainiyoyi, suna isa gab ɓakin motar Saifuddeen ya...!

Littafin nan na kuɗine in kika ganshi a woje to na satane kuma yaseeen doguwa aradu in kina buƙata turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko kuma kimin transfer ta 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.
Chapter 11 · 0% Book details