Sashe 98
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Granny zaune akan kujera mai zaman mutun biyu rike da qaurin qafafuwanta tana mammatsawa tana runtse idanunta alamun tana jin ciwo sosai muryarta a sanyaye tace “ wayyo allah qaurin qafata, wallahi qaurin qafar nan yana damuna da ciwo sosai umma dake zaune tare da aunty hasana najin haka ta tashi daga inda take zaune ta shiga d’akinta aunty hassana ta dubeta kana tace “sannu hajiya “yauwa hassana na gode, amman mai yasa bazaki dinga kunsa lalle ba yana maganin ciwon qafa sosai “ina yi amman wani lokacin idan ya tashi dole sai na had’a da man zafi .”bata kai ga rufe bakinta ba sai ga umma ta fito daga d’akinta ahankali ta qaraso inda granny take zaune hannunta rike da man zafi “sannu hajiya bari na shafa miki man zafi nan zaki d’an ji saukin zugin da suke miki, kinsan abu idan ya had’e maka da girma sai a hankali “ai kuwa na gode allah yayi albarka daman yanzu nake son tambayrki aboniki dan nasan bakya rasawa umma na qoqarin tsugunnawa sai ga maryama ta shigo bakinta d’auke da sallama .”tana ganinsu tayi murmushi ta qaraso da sauri ta tsaya kusa da umma tana cewa “umma mai ya samu granny naga kamar bata da lafiya ?”wallahi maryama qafafuwanta ke mata ciwo shine zan shafa mata man zafi “.“ayya sannu kinji granny Allah ya baki lafiya umma kawo man na shafa ma yar tsohuwar nan dan nasan ke ahankali zaki yi mata ni kuwa da iya karfina zanyi mata amfani dashi na durza sosai man zafin ya shiga ko….”
“sannu muguwa! “Inji cewar Aunty hasana “maryama ta kalleta a natse batare da tace mata komai ba “nace sannu muguwa ko karya nayi da kike kallona a wulakance ?”daman babu abinda kika iya sai tsiya da mugunta muniyar banza kawai kin wani kafeni da wasu gwala gwalan idanuwa ko zaki cinyeni? still maryam bata ce mata komai ba idan da sabo ta rigada ta saba da halinta sai dai abinda take mata ita da mahaifiyarta yana matukar damunta koma tace ya fara isarta amman tasan duk runtse duk wuya baza ta’ba iya maida mata magana ba yadda batayi magana ba haka umma da granny basu ce ci kanki ba ,maryama ta cigaba da abinda take tana bawa granny labarai masu dadi da kwantar da hankali granny ta lumshe idanunta tana cewa “yauwa diyar albarka ya isa haka ma na gode sosai Allah yayi miki albarka allah ta jikan mahaifinki Allah ya rabaki da mahaifiyarki lafiya walalhi har naji saukin zugin da yake min allah yayi miki albarka allah yasa ki gama lafiya .”maryama ta amsa da “Ameen”. fuskarta da bayyanan ne murmushin na farinciki dan idan akwai abinda ke sakata jin farinciki da natsuwa bai wuce taji kana mata fatan alkhairi ba .”
ATA tsaye acikin office dinsa sanye da wasu hadaddun suit wondo da riga ash colour haka ma takalman dake sanye a qafafunsa ash colour ne masu kyau da tsada yayinda jikinsa ke fitar da wani sanyayyen kamshi turare mai sanyi da kwantar da hankali .muryarsa a dake ya kira sunan sectary dinsa “Some !da sauri ta amsa masa da “ yes sir!” tana mai dubanshi cike da girmamawa da tsananin tsoro bai ce mata komai ba ya cigaba da aiki a system dinsa . yayinda itama ta cigaba da tsayuwa tana kallonsa da bayyanan ne tsoro a saman fuskarta ,fuskarsa babu walwala ya sauke kwayar idanunshi akanta tare da mika mata system dinsa “gashi ki duba sakonin masu neman aiki ne yau tsawon sati d’aya kenan ban samu dama dubawa ba yanzu haka ina son na d’an huta kad’an . “okay sir angama yanzu zanyi komai na gama ,ya dawo kan kujera ya zauna yana lumshe idanunshi yayinda some ta soma abinda ya sakata tana kallonsa ya mike a kan doguwar kujera da yake zaune ya kwanta tare da yin pillow da duka hannuwansa yana kallon saman office dinsa .”
Bayan kamar mintuna talatin ya mike ya shiga bayi ya d’auro alwala ya shiga d’akin dake cikin office dinsa domin gabatar da sallama bai fito ba sai around 2 :30 yana fitowa ya kirata da wayar office ,ta shigo da sauri still rike da system din dan sauran kad’an ta gama duba wad’an da suka cancata tace ” sir gani ! “ya ake ciki ? ta d’ago da sauri tana
dubansa sakamakon ganin sunan maryama cikin jerin masu neman aiki “sir !! na duba duka sakonin amman wannna sakon na qarshe akwai ….” kinga kiyi abinda ya dace kawai hanyar fita yayi daga office din “but sir!” kinga akwai abinda zanyi yayi saurin katseta ta hanyar fad’ar haka ya qarasa ficewa ”
D’aya bayan d’aya take bin number masu neman aiki har ta kawo Kan number maryama, ta kira number ya kusan sai uku ba’a daga ba a karo na hud’u ne ta d’auka tare da cewa “hello!daga can bangaren aka amsa mata da” hello ko muna magana da maryam hussein ne ? “Yes of course itace muna kiranki ne daga nan AGC company bisa sakon neman aiki da kika tura mana mun duba takardunki da safur din zanenki duk babu wata matsala yanzu dai sai mun ganki domin yin interview ta qarasa maganar a lokacin da ATA ya dawo office din ya zauna ya janyo system dinsa yana dubawa ”nan take maryama ta rud’e ta shiga kallon umma a rikice “aiki kuma ?”ai ni ban tura wani sakon ai …”umma ta matso kusa daita da sauri ta dafa kafad’anta “ki ce kinji ni na tura masu sako neman aiki .”
maryama tayi shiru tana duban umma tana jin wani irin bugun zuciya” ki natsu kiyi magana dasu da girmamawa” nan take maryama ta ‘bata rai amman babu yadda ta iya dan bazata iyawa umma mutsu akan komai ba ,numfashi ta sauke da karfi tace “shikenan yaushe Zanzo domin interview din ?On 28 march tana gama jin haka ta katse kiran tana duban umma “why umma wani aiki kuma nifa wallahi babu wani tsarin aiki arayuwata tunda yusira tana samo min zan dinga yi a gida “.murmushi umma tayi tana cewa “a’a maryama Kiyi shiru kiyiwa kanki fatan alkhairi karki ja da ikon allah “bazan yi jayayya da ikon allah ba amman ni wallahi umma …” kar ma ki rantse idan kika ga bakiyi aikin nan ba mutuwa nayi amman muddin ina raye sai kin ci amfanin karatunki “maryama ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace”zanje ne kawai saboda son da nake miki babu yadda zaayi kice nayi abu nakiyi “nima ina sonki maryama shiyasa ma na tura miki neman aiki domin nasan shine cikar burinki wani dalili ne dabam yasa kika ce bazakiyi aiki ba ta qarasa maganar tana riko hannun maryama cikin nata tana jin wani irin a zuciyarta yayinda idanunta suka cika da ruwan hawaye sadam dinta ta tuna .”
ahankali maryama ta zare hannunta cikin na umma ta shige dakinta da umma ta barma ta fad’a kan gado ranta duk babu dadi tunanin rayuwarta ta shig yi sannu ahankali har bacci ‘barawo yayi awon gaba daita .”
“sir ina son nace wani abu shiru yayi bai amsa mata ba sai qarar daddana system dinsa kawai akeji sai data maimaita maganarta sannan yace “okay ina jinki na gama duk abinda kasani na kira wad’an da suka cancata “nasan zasuyi matukar murna dan babu wanda zai samu kiran daga kamfanin AGC bai ji dadi ba “sai wacan banzar yarinyar ba .” ya fad’a aciki ransa amman a zahiri cewa yayi “okay !sectary dai tayi shiru taso ya bata dama tun kafin ta kira number maryama amman yaki ,alamarin mai gidan nasu ne sai hakuri shi kawai zaiyi abinda yake so kuma alokacin da ya ga dama amman wani bai isa ba .”parlour’n mami dauke yake da manyan baki domin kuwa baba qarami ne tare da uncle jay da mami da aunty shahida har ma da aunty abida tare da sultana ,table din gabansu cike yake da kayan motsa baki wanda mami tasa aka kawo masu hira tayi dadi sosai inda aunty abida ta sako batun aikin sultana nan take baba qarami yace “ kai diyata karki damu ta shirya kawai ta fara zuwa aiki bama ita ba idan kina da masu bukatar son aiki akarkashinmu ki kawo muna maraba dasu “.
“wani irin murna tayi tana mai jin dadin maganarsa ita dai mami bata ce uffan ba aka cigaba da hira har sanda ATA ya shigo mami na ganin shigowarsa ta mike zuwa kusa dashi dan tasan baya son azo acika masu gida da hayaniya kuma baqaramin aikinsa bane yayi abinda zai korasu gabadaya “abinda ya bawa mami mamaki bai wuce yadda sultana ta mike tazo ta tsaya gabansa ba tana wani irin rausaya da lumshe masa ido “thank you so much for giving me the job ,gsky naji dadi sosai zanyi aiki a qarqashin AGC company “what ?ya fad’a a matukar tsawace yana kallonta kafin ahankali ya motsa lip’s dinsa “ina ganin kamar kin fara shaye shaye wa ya baki aiki a company “?baba qarami !”tayi mgnr tana duban inda baba qarami yake zaune”ni na bata kuma zatayi aiki alokacin dataso saboda itama uwarta nada ‘yanci acikin AGC “gsky baba qarami kana da matukar kirki amman shi wannan d’an naka ya fiyye jin kai ya manta cewar ni dashi asalin mu d’aya “to ai shi Adam bai da wannan kirki kuma duk cikin zuriarmu babu mara mutunci kamarsa amman wannan karon ko yana so ko bai so yarinya dole kiyi aiki a kamfani kwana nan ma zan dawo na cigaba da kula da kamfani dan nasan kan kamfani fiyye da wannan gatalallen yaron mara kunya idan ma naga dama zan iya dakatar dashi dan dama bai iya tafiyar da kasuwanci ba hauka da shirme kawai yasa a gaba saboda rashin sanin kan kasuwanci komai cikin zafin rai da fushi yake.”
“sannu muguwa! “Inji cewar Aunty hasana “maryama ta kalleta a natse batare da tace mata komai ba “nace sannu muguwa ko karya nayi da kike kallona a wulakance ?”daman babu abinda kika iya sai tsiya da mugunta muniyar banza kawai kin wani kafeni da wasu gwala gwalan idanuwa ko zaki cinyeni? still maryam bata ce mata komai ba idan da sabo ta rigada ta saba da halinta sai dai abinda take mata ita da mahaifiyarta yana matukar damunta koma tace ya fara isarta amman tasan duk runtse duk wuya baza ta’ba iya maida mata magana ba yadda batayi magana ba haka umma da granny basu ce ci kanki ba ,maryama ta cigaba da abinda take tana bawa granny labarai masu dadi da kwantar da hankali granny ta lumshe idanunta tana cewa “yauwa diyar albarka ya isa haka ma na gode sosai Allah yayi miki albarka allah ta jikan mahaifinki Allah ya rabaki da mahaifiyarki lafiya walalhi har naji saukin zugin da yake min allah yayi miki albarka allah yasa ki gama lafiya .”maryama ta amsa da “Ameen”. fuskarta da bayyanan ne murmushin na farinciki dan idan akwai abinda ke sakata jin farinciki da natsuwa bai wuce taji kana mata fatan alkhairi ba .”
ATA tsaye acikin office dinsa sanye da wasu hadaddun suit wondo da riga ash colour haka ma takalman dake sanye a qafafunsa ash colour ne masu kyau da tsada yayinda jikinsa ke fitar da wani sanyayyen kamshi turare mai sanyi da kwantar da hankali .muryarsa a dake ya kira sunan sectary dinsa “Some !da sauri ta amsa masa da “ yes sir!” tana mai dubanshi cike da girmamawa da tsananin tsoro bai ce mata komai ba ya cigaba da aiki a system dinsa . yayinda itama ta cigaba da tsayuwa tana kallonsa da bayyanan ne tsoro a saman fuskarta ,fuskarsa babu walwala ya sauke kwayar idanunshi akanta tare da mika mata system dinsa “gashi ki duba sakonin masu neman aiki ne yau tsawon sati d’aya kenan ban samu dama dubawa ba yanzu haka ina son na d’an huta kad’an . “okay sir angama yanzu zanyi komai na gama ,ya dawo kan kujera ya zauna yana lumshe idanunshi yayinda some ta soma abinda ya sakata tana kallonsa ya mike a kan doguwar kujera da yake zaune ya kwanta tare da yin pillow da duka hannuwansa yana kallon saman office dinsa .”
Bayan kamar mintuna talatin ya mike ya shiga bayi ya d’auro alwala ya shiga d’akin dake cikin office dinsa domin gabatar da sallama bai fito ba sai around 2 :30 yana fitowa ya kirata da wayar office ,ta shigo da sauri still rike da system din dan sauran kad’an ta gama duba wad’an da suka cancata tace ” sir gani ! “ya ake ciki ? ta d’ago da sauri tana
dubansa sakamakon ganin sunan maryama cikin jerin masu neman aiki “sir !! na duba duka sakonin amman wannna sakon na qarshe akwai ….” kinga kiyi abinda ya dace kawai hanyar fita yayi daga office din “but sir!” kinga akwai abinda zanyi yayi saurin katseta ta hanyar fad’ar haka ya qarasa ficewa ”
D’aya bayan d’aya take bin number masu neman aiki har ta kawo Kan number maryama, ta kira number ya kusan sai uku ba’a daga ba a karo na hud’u ne ta d’auka tare da cewa “hello!daga can bangaren aka amsa mata da” hello ko muna magana da maryam hussein ne ? “Yes of course itace muna kiranki ne daga nan AGC company bisa sakon neman aiki da kika tura mana mun duba takardunki da safur din zanenki duk babu wata matsala yanzu dai sai mun ganki domin yin interview ta qarasa maganar a lokacin da ATA ya dawo office din ya zauna ya janyo system dinsa yana dubawa ”nan take maryama ta rud’e ta shiga kallon umma a rikice “aiki kuma ?”ai ni ban tura wani sakon ai …”umma ta matso kusa daita da sauri ta dafa kafad’anta “ki ce kinji ni na tura masu sako neman aiki .”
maryama tayi shiru tana duban umma tana jin wani irin bugun zuciya” ki natsu kiyi magana dasu da girmamawa” nan take maryama ta ‘bata rai amman babu yadda ta iya dan bazata iyawa umma mutsu akan komai ba ,numfashi ta sauke da karfi tace “shikenan yaushe Zanzo domin interview din ?On 28 march tana gama jin haka ta katse kiran tana duban umma “why umma wani aiki kuma nifa wallahi babu wani tsarin aiki arayuwata tunda yusira tana samo min zan dinga yi a gida “.murmushi umma tayi tana cewa “a’a maryama Kiyi shiru kiyiwa kanki fatan alkhairi karki ja da ikon allah “bazan yi jayayya da ikon allah ba amman ni wallahi umma …” kar ma ki rantse idan kika ga bakiyi aikin nan ba mutuwa nayi amman muddin ina raye sai kin ci amfanin karatunki “maryama ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace”zanje ne kawai saboda son da nake miki babu yadda zaayi kice nayi abu nakiyi “nima ina sonki maryama shiyasa ma na tura miki neman aiki domin nasan shine cikar burinki wani dalili ne dabam yasa kika ce bazakiyi aiki ba ta qarasa maganar tana riko hannun maryama cikin nata tana jin wani irin a zuciyarta yayinda idanunta suka cika da ruwan hawaye sadam dinta ta tuna .”
ahankali maryama ta zare hannunta cikin na umma ta shige dakinta da umma ta barma ta fad’a kan gado ranta duk babu dadi tunanin rayuwarta ta shig yi sannu ahankali har bacci ‘barawo yayi awon gaba daita .”
“sir ina son nace wani abu shiru yayi bai amsa mata ba sai qarar daddana system dinsa kawai akeji sai data maimaita maganarta sannan yace “okay ina jinki na gama duk abinda kasani na kira wad’an da suka cancata “nasan zasuyi matukar murna dan babu wanda zai samu kiran daga kamfanin AGC bai ji dadi ba “sai wacan banzar yarinyar ba .” ya fad’a aciki ransa amman a zahiri cewa yayi “okay !sectary dai tayi shiru taso ya bata dama tun kafin ta kira number maryama amman yaki ,alamarin mai gidan nasu ne sai hakuri shi kawai zaiyi abinda yake so kuma alokacin da ya ga dama amman wani bai isa ba .”parlour’n mami dauke yake da manyan baki domin kuwa baba qarami ne tare da uncle jay da mami da aunty shahida har ma da aunty abida tare da sultana ,table din gabansu cike yake da kayan motsa baki wanda mami tasa aka kawo masu hira tayi dadi sosai inda aunty abida ta sako batun aikin sultana nan take baba qarami yace “ kai diyata karki damu ta shirya kawai ta fara zuwa aiki bama ita ba idan kina da masu bukatar son aiki akarkashinmu ki kawo muna maraba dasu “.
“wani irin murna tayi tana mai jin dadin maganarsa ita dai mami bata ce uffan ba aka cigaba da hira har sanda ATA ya shigo mami na ganin shigowarsa ta mike zuwa kusa dashi dan tasan baya son azo acika masu gida da hayaniya kuma baqaramin aikinsa bane yayi abinda zai korasu gabadaya “abinda ya bawa mami mamaki bai wuce yadda sultana ta mike tazo ta tsaya gabansa ba tana wani irin rausaya da lumshe masa ido “thank you so much for giving me the job ,gsky naji dadi sosai zanyi aiki a qarqashin AGC company “what ?ya fad’a a matukar tsawace yana kallonta kafin ahankali ya motsa lip’s dinsa “ina ganin kamar kin fara shaye shaye wa ya baki aiki a company “?baba qarami !”tayi mgnr tana duban inda baba qarami yake zaune”ni na bata kuma zatayi aiki alokacin dataso saboda itama uwarta nada ‘yanci acikin AGC “gsky baba qarami kana da matukar kirki amman shi wannan d’an naka ya fiyye jin kai ya manta cewar ni dashi asalin mu d’aya “to ai shi Adam bai da wannan kirki kuma duk cikin zuriarmu babu mara mutunci kamarsa amman wannan karon ko yana so ko bai so yarinya dole kiyi aiki a kamfani kwana nan ma zan dawo na cigaba da kula da kamfani dan nasan kan kamfani fiyye da wannan gatalallen yaron mara kunya idan ma naga dama zan iya dakatar dashi dan dama bai iya tafiyar da kasuwanci ba hauka da shirme kawai yasa a gaba saboda rashin sanin kan kasuwanci komai cikin zafin rai da fushi yake.”