Sashe 34
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da tayi addu’a sannan ta shiga office din ta gaishe da mutumin data gani zaune mai suna wale yana duba wasu fararen takardu,ya d’ago ya kalleta a natse sannan ya sake kiran sunanta “maryama hussein !”tace yes sir ! sai daya bata izinin zama sannan ta zauna a natse tana wasa da yatsun hannunta wanda ya zame mata jiki ,ya d’an saci kallonta yana mamakin matsayin da aka bata ,domin kujera ne da suka dade suna neman wanda zai maye gurbinsa , sai dai lokacin daya fara auno mata tambayoyi akan kasuwanci da kuma matsayin da zata taka ya ajiye mamakinsa a gefe domin kuwa ta cancanci ta hau matsayin kuma irinta mai kamfanin ya dade yana nema .”
bata wani jima ba ta fito har da award aka bata sakamakon aikin da tayi dasu daman kuma sun ajiye ne domin rana irin ta yau “congratulations sauran abokan aikinta suka shiga yi mata tana amsa masu da “thank you tare da rungumar mata daga cikinsu duk wannan farinciki da take ciki bai kawo mata natsuwa ba saboda rashin ganin subai’a da batayi ba ta ciro wayarta ta soma nemanta tana tafiya ahankali har ta fito haraban ma’aikatan subai’a ta d’auka tana kuka hankalin maryama ya sake tashi sosai ciki tsanani tashin hankali tace “subai’a kina ne na shigo har an d’aukeni aiki banganki ba ? tana shirin sake yin magana ta hangota a bayan wata bishi tana qoqarin fitowa .”
Da sauri maryama ta qaraso ta tsaya tana qare mata kallo tsab hawayenta yasa zuciyar maryama tsananin bugawa “me Ke faru dake subai’a ?kukan me kike yi ?muryata cike da kuka tace “na rasa aikin nan ,da yawa wad’an da suka d’auka alfarma ne yanzu bansan ta yaya zamu cigaba da rayuwa ba daman da allah da aikin nan na dogara gashi ban samu ba muddin sai da wata alfarma zan samu aikin nasan har abada bazan samu ba .”ta riko hannunta maryama tana cigaba da kuka ta soma rokonta “dan girman allah maryama karki barni haka ki taimakeni ki bar min aikin nan nasan zaki samu wanda yafishi gabad’aya idanun subai’a sun rufe har sai da maryama ta kira sunanta sannan ta tsaigaita kukanta “ki kwantar da hankalinki ki bar kuka nan haka” amman ta yaya babu sunanki bayan ..”sai kuma tayi shiru ta janyo hannuta zuwa ciki “zo muje .”
maryama na gaba subai’a na bayanta har suka qarasa bakin office din james ta nemi izinin ganinsa aka bata damar shiga ,wanda ta samu wannan damar ne saboda ammar domin yadda yake mata yasa mutane dayawa d’aukar sonta yake maryama ta shiga tare da subai’a dake kuka har lokacin .”bayan ta gaishesa cike da ladabi tace “dan allah ina neman wata alfarma agareka ya kalleta dan shima ta burgesa yadda ma’akatan suka dinga yaba kwazonta tun kafin tazo kuma zuwanta wale ya sake tabbatar masa iri irinsu basu dayawa a duniya dan tunda ya sheida masa ya kira mai gidansa seun ya sheida masa muryarta a matukar sanyaye ta soma magana kamar zatayi kuka “dan allah sir wannan yaruwa tawa nake son ta maye gurbina ma’ana acire sunana a saka nata .”ya kalleta a tsanake domin yasan yadda ake shan wahalar neman aiki yanzu da kudinka ma baka samu “.
“Saboda allah zakayi karka tsaya tunanin komai ni inda aikin da zanyi domin tallafa rayuwata for now ,ita kuma bata dashi da wannan aiki Kawai ta dogara ga mahaifinta ya rasu ko da yake nima marainiya ce amman dai tafini bukatan aikin nan saboda tana da kanne dayawa da mahaifiya mara lafiya dake karkashin kulawarta itace komai nasu “da wannan maganar ta karyar da zuciyar James ya kalli subai’a cike da tausayawa yace “sorry oo !”zan iya miki wannan alfarma sai dai bazata maye gurbin kujerarki ba “tayi shiru tana tunani abinda zata ce kafin tayi magana ya cigaba” kujerarki ke kad’ai ake bukata sakamakon oga ammar sunanki ya bayar gashi yanzu kinzo da wata magana “karka ji komai a saka a duk inda zaa sakata nidai burina ta samu aikin ni zuwa gaba in sha allahu zanyi aiki daku amman a yanzu burina subai’a ta samu aiki .”
Mr James ya saka sunan Subai’a ya cire sunan maryama “ suka fito zuwa gindin wata bishiya maryama na cewa subai’a “congratulations na tayaki murna kawata yanzu kin zama cikakkiyar maaikaciya ta fad’a tana murmushi subai’a ta rungumeta cike da farinciki “na gode na gode maryama allah ya saka miki da mafifincinsa nayi imani zaki samu aikin da yafi wannan da kika bar min tana kuka tana gode mata” haba subai ki daina kuka kawai dan na sadaukar miki da aikina kike wannan godiya da kuka haka ?” ta goge mata hawaye tana cewa ni na zan bar ki na wuce gida nasan akwai abubuwan da zaku yi kafin ku wuce ina miki fatan alkhairi allah yasa ki fara aiki a saa ta juya a hankali ta soma taku subai’a tabi bayanta da kallo hakika bazata ta’ba manta alkhairinta gareta ba .”
Da wuri maryama ta dawo gida koda ta shigo kai tsaye bangaren ummah ta shiga ta sheida mata amman ta isketa a dakinta tana bacci dan haka ta fito ta shiga bangarensu ta zauna a parlour’n tana sauke numfashi tare da dafe goshinta ko cikakken minti biyar batayi ba ,Aunty ta fito da mamaki take kallonta “lafiya naga har kin dawo ?lafiya aunty nan ta zayyane mata komai sosai ran aunty ya baci kamar ta rufeta da duka musaman data lura ko ajikin maryama dan babu alamun damuwa atare daita “me yasa zaki bada aikinki bayan Kinsan muma muna fama da kanmu ? “aunty kiyi hakuri kin sani ni zan iya cigaba da aikin zanena kafin na samun wani aikin ita fa ?bata da wani sanar hannu da zatayi kuma rokona tayita tana kuka saboda bata da hanyar da zata kula da kannenta da mahaifiyarta fatana allah yasa ya zame min alkhairi ta qarasa mgnr muryarta na rawa alamun kuka “.
Aunty ta samu waje ta zauna kusa da ita tana cewa “shikenan allah yasa ki samu wani wanda yafi shi muryarta a raunane tace “Ameen ko da ummah da habib suka ji suma abun bai masu dadi ba amman babu yadda suka iya tunda ta bayar sai hakuri da fatan alkhairi .”washegari tana zaune a parlour’n su tare da aunty kiran ammar ya shigo ta tashi ta koma dakinta sannan ta d’auka tana dauka ya rufeta da fad’a “kin kyauta saboda shakuwa da qaunar da nake miki yasa na tsaya lallai Ke zaa bawa wannan matsayin saboda ina son shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninki da Adam amman kika zuba min qasa a ido ,ina ganin idan shakuwa ta shiga tsakaninki dashi zai taimaka kwarai wajen janyo hankalin gareki shine kika bar wata .”
sanyayyen murmushi tayi kamar tana gabansa “to amman ai na fad’a maka akwai wanda zan aura .”“wanda zaki aura din banza ,wallahi ko ba dan Adam ba nan gaba kadan zaki fara gano illar abinda kika aikatawa kanki ,kuma duk abinda ya faru babu ruwana ke kar ma ki sake nemana ko da yake ma tafiya zan yi gobe kuma zan dauki lokaci ban dawo kasar ba “allah ya kaika lafiya “Ameen amman babu ruwana dake wallahi ko a hanya kika gani kika min magana sai bata miki rai “a ina ma zan ganka dole sai ma’aikata kuma babu abinda zai kaini tunda bana aiki a karkashinku tayi mgnr aranta alokacin ya katse kiran .”
ranar yau din jinsa maryama tayi dabam wani irin damuwa ta tsinci kanta ciki ita kanta tana jin mai yasa tayi abinda tayi kowa ya kalli fuskarta zai ga canji laifin kanta ta gani me yasa ma ta bar wayarta a kunne bata kashe ba da wata killa bai qara mata damuwa akan wanda take ciki ba tayi shiru yayinda a cikin zuciyarta takewa kanta fatan alkhairi .”awanni sukai ta zuwa suna wucewa amman maryama bata daina jin damuwa dan haka fito ta nufi bangaren ummah tana shiga ta isketa tana tsinke ewedu “sannu da aiki ummah!Yauwa maryama ya zaman gida ?gamu dai yanzu zamu fara ummah tayi murmushi “zaki samu wani aiki nan kusa ta zauna kusa daita ta d’auki gayen ewedu ta fara tsinkewa “gobe nan ma zan fara nema ssi ku tayani da addua,in sha allahu alkhairi zamu ji .”
Ahankali sukai ta hirarsu daga nan umma ta sako mata maganar sadam “maryama kin dai san komai daga Ke har sadam baku kawowa zuciyarku zaku zama abu d’aya ba sai gashi allah yayi ikonsa dan haka ki saki jikinki dashi karki tsaya sai yajaki ajiki ai kin fahimceni ina ganin nan da wata biyu masu zuwa zaa daura maku aure” maryama tayi shiru ba dan bazata aikata abinda take butaka ba bata da option dole zata jashi ajiki tuni ma ta sadaukar da rayuwarta garesa ko ba dan shi umma ta wuce komai gareta nan ta garasa yininta tare sukai komai a kitchen har karfe shida da rabi ta buga ta fito parlour’n inda ta iske yaya sadam zaune shiru a falon da alamun yayi zurfi cikin tunani maryama ta qaraso idanunta akanshi kallon minti goma tayi masa sannan tace “meke damunka yaya sadam kayi shiru haka ? “
Ya sauke numfashi tare da sauke kwayar idanunshi akanta a natse ta samu waje ta zauna kusa dashi tana cewa “ya wurin aikin naka ? babu komai aiki kuma alhamd wasu abubuwa né suka sha min kai amman in sha allahu zan shawo kan komai na gode sosai da kulawarki “no karka damu yaya sadam , sukai shiru na kusan minti goma sannan ya kira sunanta “.marayam! ta tsura masa ido kawai tana kallonsa “ya batun aikin da kika fita nema ?”naje na samu amman na bawar qawata subai’a aikin “why ?!ya tamvayeta yana dubanta. “saboda tafini bukata aikin itace komai na gidansu gashi mamanta bata da lafiya ga rashin mahaifi da sukai yaya sadam wallahi ina tausaya mata “gsky abar tausayi ce kin kyauta sosai da kika bar mata .”
bata wani jima ba ta fito har da award aka bata sakamakon aikin da tayi dasu daman kuma sun ajiye ne domin rana irin ta yau “congratulations sauran abokan aikinta suka shiga yi mata tana amsa masu da “thank you tare da rungumar mata daga cikinsu duk wannan farinciki da take ciki bai kawo mata natsuwa ba saboda rashin ganin subai’a da batayi ba ta ciro wayarta ta soma nemanta tana tafiya ahankali har ta fito haraban ma’aikatan subai’a ta d’auka tana kuka hankalin maryama ya sake tashi sosai ciki tsanani tashin hankali tace “subai’a kina ne na shigo har an d’aukeni aiki banganki ba ? tana shirin sake yin magana ta hangota a bayan wata bishi tana qoqarin fitowa .”
Da sauri maryama ta qaraso ta tsaya tana qare mata kallo tsab hawayenta yasa zuciyar maryama tsananin bugawa “me Ke faru dake subai’a ?kukan me kike yi ?muryata cike da kuka tace “na rasa aikin nan ,da yawa wad’an da suka d’auka alfarma ne yanzu bansan ta yaya zamu cigaba da rayuwa ba daman da allah da aikin nan na dogara gashi ban samu ba muddin sai da wata alfarma zan samu aikin nasan har abada bazan samu ba .”ta riko hannunta maryama tana cigaba da kuka ta soma rokonta “dan girman allah maryama karki barni haka ki taimakeni ki bar min aikin nan nasan zaki samu wanda yafishi gabad’aya idanun subai’a sun rufe har sai da maryama ta kira sunanta sannan ta tsaigaita kukanta “ki kwantar da hankalinki ki bar kuka nan haka” amman ta yaya babu sunanki bayan ..”sai kuma tayi shiru ta janyo hannuta zuwa ciki “zo muje .”
maryama na gaba subai’a na bayanta har suka qarasa bakin office din james ta nemi izinin ganinsa aka bata damar shiga ,wanda ta samu wannan damar ne saboda ammar domin yadda yake mata yasa mutane dayawa d’aukar sonta yake maryama ta shiga tare da subai’a dake kuka har lokacin .”bayan ta gaishesa cike da ladabi tace “dan allah ina neman wata alfarma agareka ya kalleta dan shima ta burgesa yadda ma’akatan suka dinga yaba kwazonta tun kafin tazo kuma zuwanta wale ya sake tabbatar masa iri irinsu basu dayawa a duniya dan tunda ya sheida masa ya kira mai gidansa seun ya sheida masa muryarta a matukar sanyaye ta soma magana kamar zatayi kuka “dan allah sir wannan yaruwa tawa nake son ta maye gurbina ma’ana acire sunana a saka nata .”ya kalleta a tsanake domin yasan yadda ake shan wahalar neman aiki yanzu da kudinka ma baka samu “.
“Saboda allah zakayi karka tsaya tunanin komai ni inda aikin da zanyi domin tallafa rayuwata for now ,ita kuma bata dashi da wannan aiki Kawai ta dogara ga mahaifinta ya rasu ko da yake nima marainiya ce amman dai tafini bukatan aikin nan saboda tana da kanne dayawa da mahaifiya mara lafiya dake karkashin kulawarta itace komai nasu “da wannan maganar ta karyar da zuciyar James ya kalli subai’a cike da tausayawa yace “sorry oo !”zan iya miki wannan alfarma sai dai bazata maye gurbin kujerarki ba “tayi shiru tana tunani abinda zata ce kafin tayi magana ya cigaba” kujerarki ke kad’ai ake bukata sakamakon oga ammar sunanki ya bayar gashi yanzu kinzo da wata magana “karka ji komai a saka a duk inda zaa sakata nidai burina ta samu aikin ni zuwa gaba in sha allahu zanyi aiki daku amman a yanzu burina subai’a ta samu aiki .”
Mr James ya saka sunan Subai’a ya cire sunan maryama “ suka fito zuwa gindin wata bishiya maryama na cewa subai’a “congratulations na tayaki murna kawata yanzu kin zama cikakkiyar maaikaciya ta fad’a tana murmushi subai’a ta rungumeta cike da farinciki “na gode na gode maryama allah ya saka miki da mafifincinsa nayi imani zaki samu aikin da yafi wannan da kika bar min tana kuka tana gode mata” haba subai ki daina kuka kawai dan na sadaukar miki da aikina kike wannan godiya da kuka haka ?” ta goge mata hawaye tana cewa ni na zan bar ki na wuce gida nasan akwai abubuwan da zaku yi kafin ku wuce ina miki fatan alkhairi allah yasa ki fara aiki a saa ta juya a hankali ta soma taku subai’a tabi bayanta da kallo hakika bazata ta’ba manta alkhairinta gareta ba .”
Da wuri maryama ta dawo gida koda ta shigo kai tsaye bangaren ummah ta shiga ta sheida mata amman ta isketa a dakinta tana bacci dan haka ta fito ta shiga bangarensu ta zauna a parlour’n tana sauke numfashi tare da dafe goshinta ko cikakken minti biyar batayi ba ,Aunty ta fito da mamaki take kallonta “lafiya naga har kin dawo ?lafiya aunty nan ta zayyane mata komai sosai ran aunty ya baci kamar ta rufeta da duka musaman data lura ko ajikin maryama dan babu alamun damuwa atare daita “me yasa zaki bada aikinki bayan Kinsan muma muna fama da kanmu ? “aunty kiyi hakuri kin sani ni zan iya cigaba da aikin zanena kafin na samun wani aikin ita fa ?bata da wani sanar hannu da zatayi kuma rokona tayita tana kuka saboda bata da hanyar da zata kula da kannenta da mahaifiyarta fatana allah yasa ya zame min alkhairi ta qarasa mgnr muryarta na rawa alamun kuka “.
Aunty ta samu waje ta zauna kusa da ita tana cewa “shikenan allah yasa ki samu wani wanda yafi shi muryarta a raunane tace “Ameen ko da ummah da habib suka ji suma abun bai masu dadi ba amman babu yadda suka iya tunda ta bayar sai hakuri da fatan alkhairi .”washegari tana zaune a parlour’n su tare da aunty kiran ammar ya shigo ta tashi ta koma dakinta sannan ta d’auka tana dauka ya rufeta da fad’a “kin kyauta saboda shakuwa da qaunar da nake miki yasa na tsaya lallai Ke zaa bawa wannan matsayin saboda ina son shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninki da Adam amman kika zuba min qasa a ido ,ina ganin idan shakuwa ta shiga tsakaninki dashi zai taimaka kwarai wajen janyo hankalin gareki shine kika bar wata .”
sanyayyen murmushi tayi kamar tana gabansa “to amman ai na fad’a maka akwai wanda zan aura .”“wanda zaki aura din banza ,wallahi ko ba dan Adam ba nan gaba kadan zaki fara gano illar abinda kika aikatawa kanki ,kuma duk abinda ya faru babu ruwana ke kar ma ki sake nemana ko da yake ma tafiya zan yi gobe kuma zan dauki lokaci ban dawo kasar ba “allah ya kaika lafiya “Ameen amman babu ruwana dake wallahi ko a hanya kika gani kika min magana sai bata miki rai “a ina ma zan ganka dole sai ma’aikata kuma babu abinda zai kaini tunda bana aiki a karkashinku tayi mgnr aranta alokacin ya katse kiran .”
ranar yau din jinsa maryama tayi dabam wani irin damuwa ta tsinci kanta ciki ita kanta tana jin mai yasa tayi abinda tayi kowa ya kalli fuskarta zai ga canji laifin kanta ta gani me yasa ma ta bar wayarta a kunne bata kashe ba da wata killa bai qara mata damuwa akan wanda take ciki ba tayi shiru yayinda a cikin zuciyarta takewa kanta fatan alkhairi .”awanni sukai ta zuwa suna wucewa amman maryama bata daina jin damuwa dan haka fito ta nufi bangaren ummah tana shiga ta isketa tana tsinke ewedu “sannu da aiki ummah!Yauwa maryama ya zaman gida ?gamu dai yanzu zamu fara ummah tayi murmushi “zaki samu wani aiki nan kusa ta zauna kusa daita ta d’auki gayen ewedu ta fara tsinkewa “gobe nan ma zan fara nema ssi ku tayani da addua,in sha allahu alkhairi zamu ji .”
Ahankali sukai ta hirarsu daga nan umma ta sako mata maganar sadam “maryama kin dai san komai daga Ke har sadam baku kawowa zuciyarku zaku zama abu d’aya ba sai gashi allah yayi ikonsa dan haka ki saki jikinki dashi karki tsaya sai yajaki ajiki ai kin fahimceni ina ganin nan da wata biyu masu zuwa zaa daura maku aure” maryama tayi shiru ba dan bazata aikata abinda take butaka ba bata da option dole zata jashi ajiki tuni ma ta sadaukar da rayuwarta garesa ko ba dan shi umma ta wuce komai gareta nan ta garasa yininta tare sukai komai a kitchen har karfe shida da rabi ta buga ta fito parlour’n inda ta iske yaya sadam zaune shiru a falon da alamun yayi zurfi cikin tunani maryama ta qaraso idanunta akanshi kallon minti goma tayi masa sannan tace “meke damunka yaya sadam kayi shiru haka ? “
Ya sauke numfashi tare da sauke kwayar idanunshi akanta a natse ta samu waje ta zauna kusa dashi tana cewa “ya wurin aikin naka ? babu komai aiki kuma alhamd wasu abubuwa né suka sha min kai amman in sha allahu zan shawo kan komai na gode sosai da kulawarki “no karka damu yaya sadam , sukai shiru na kusan minti goma sannan ya kira sunanta “.marayam! ta tsura masa ido kawai tana kallonsa “ya batun aikin da kika fita nema ?”naje na samu amman na bawar qawata subai’a aikin “why ?!ya tamvayeta yana dubanta. “saboda tafini bukata aikin itace komai na gidansu gashi mamanta bata da lafiya ga rashin mahaifi da sukai yaya sadam wallahi ina tausaya mata “gsky abar tausayi ce kin kyauta sosai da kika bar mata .”