Sashe 84
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"muryarsa a kasalance ya gaishe da mami ."kamar ko yaushe ta amsa masa tana mai tsura masa kwayar idanunta kamar wacce taga wani sabon halitta ,cike da kulawa tace "sannu da zuwa adamcy ya hanya ka dawo lafiya ?da sauri ya amsa mata da "lafiya !"yana qoqarin hayewa samansa hannunsa d'aya soke acikin aljihun wandonsa .bayansa tabi da kallo "shigowarsa cikin wannan yanayin yasa duk mami ta d'an rikice kasa samun kwanciyar hankali tayi ,cike da tashin hankali ta mike tsaye tabi bayansa .
ahankali ta tura kofar parlour'nsa ta shiga duhu falon dan haka ta kunna wuta nan da nan haske ya haskaka koina a parlour'n sai dai bata gansa ba dan haka ta nufi hanyar bedroom dinsa ta shiga nan ta iskeshi tsaye ya jingina jikinsa da bango d'akin yayi sama da kanshi hawaye ne kwance acikin idanunshi yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa ya rasa meke masa dadi arayuwarsa bai san ta ina zai fara ba ,komai ya rigada ya tsaya masa gabad'aya baya jin dadin rayuwarsa ,ya kasa fahimtar kansa ko kuma yace yau tazo masa da abubuwa da yawa wanda duk tarin damuwa ne akan wanda yake ciki ya dinga jin kamar ya kashe kansa ya huta da rayuwar da yake ."
lumshe tsumammun idanunshi yayi sai ga hawaye sharrr na bin kuncinsa "adamcy nah ! ".mami ta kira sunansa cikin tsananin tashin hankali har jikinta na rawa . amatukar firgice ya tsaida kwayar idanunshi dake cike da ruwan hawaye akanta qirjinsa na wani irin dokawa da sauri dan bai ji motsin shigowarta ba sai sautin muryarta wani irin zazzafan numfashi ya sauke yana sake maida kanshi sama tare da ciro hanky ya shiga d'auke hawayensa"lafiyarka kake zubar da hawaye adamcy ?ta tambayesa cikin tsananin tashin hankali dan duk abinda zai sashi zubar da hawaye baqaramin abu bane da muninsa ya wuce misali. shiru yayi ya kasa magana dan bai san me zai fad'a mata ba "kayi min magana mana adamcy dan kasa har zuciyata ta fara tsinkewa."
da yatsan hannunsa ya nuna mata daidai saitin zuciyarsa dake bugawa fiyye da kaida ."sake matsoshi tayi sosai tana cewa "meke damunka "?"zuciyata sweet.." yana kai wa nan yayi shiru ya kasa cigaba da maganar idanunshi na sake cikowa da ruwan hawaye"me ya samu zuciyarka ?" ta sake tambayarsa hankalinta na qara tashi "I don't know what's wrong with me sweetheart amman dai nasan zuciyata kullum ciwo take min"."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun " allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta "abinda mami ta shiga furtawa kenan tana sake maimaitawa " i know something is wrong with my heart wallahi sweetheart akwai ciwo mai zafi acikin zuciyata wanda zai iya kasheni nan kusa .."
nan da nan fuskar mami ta qara sauyawa hankalinta a matukar tashe tace "ka dinga sausautawa kanka adamcy da yawon tunani ,ka dinga addua akan duk abinda ya dameka addua tana canzawa bawa qaddararsa kuma tana saka natsuwa acikin zuciyar bawa "numfashi ya sauke da karfi yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ,magana yake son yi amman zafin da zuciyarsa keyi ya hana shi cewa uffan "kasamu natsuwa adamcy ka dinga furta wannan adduar zaka samu natsuwa da sausauci a wajen Allah zai yaye maka dukkanin damuwarka "allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta ahankali ya sauke idanuwanshi ya tsura ma mami kawai yana kallonta cikin yanayi na tsanani damuwa "ka sani idan wani abu ya sameka nice farkon wacce zata fara shiga damuwa ga kuma d'an cikin jikin maryam wanda bamu san abinda zata haifa ba karka bari muyi maraicinka. adamcy kasan yadda nake sonka idan na rasaka zan shiga damuwa a kullum adduata na mutu na barka a duniya ba ka mutu ka barni ba tunda ta fara magana bai ce mata uffan ba sai ma ciro wayarsa da yayi ya soma neman layin likitansa muryarsa ce ta katse mami daga maganar da take masa ahankali yake magana tamkar mara lafiya "doctor kazo ka dubani please ".daga haka bai sake cewa komai ba ya katse kiran d'akin yayi tsit tamkar babu mutane acikinsa ."
Ahankali ya soma d'aga kafafunsa zuwa Kan gado ya fad'a ya kwanta flat ransa duk babu dadi yayinda idanunshi na kallon saman d'akin babu abinda yake gani sai kwayar idanun maryama da yatsun hannun ta da sautin zazzakar muryarta mami tazo ta zauna kusa dashi tana daura hannunta saman kansa tana masa sannu "bayan mintuna shabiyar sai ga doctor ya shigo tare da sallama tashi yayi ya zauna ya jingina bayansa da abun gado yana sauke numfashi da kyar tare da yiwa doctor bayanin yadda yake ji batare da 'bata lokaci ba doctor ya fara masa gwaje gwaje bayan doctor ya gama yayi masa allura sannan yace "ranka ya dade jininka ne ya hau kad'an yana da kyau ka dinga saukakawa kanka wasu abubuwa dan zuciyarka na bukatar hud'u yanzu dai nayi maka allurar bacci in sha allahu kana tashi zakaji daidai Allah ya baka lafiya ya ajiye masa magunguna yace zai wuce ."mami tayi masa godiya adaidai lokacin da doctor ke had'a kayansa yayi mata sallama ya wuce ."
"Ka tashi kayi sallah magriba kafin bacci ya d'aukeka sannan me za'a kawo maka coffe ko tea "any one sweetheart." ya furta tare da mikewa da kyar ya shiga bathroom ita kuma mami ta fita kawo masa coffe dan tasan shi yafi bukata wanka ya fara sannan yayi alwala ya fito ya cire kayan jikinsa ya canza zuwa jallabiya brown colour mai ratsin baki ya isa inda abun sallarsa yake ya gabatar da sallah bayan ya idar ya koma Kan gado ya kwanta lamo tare da janyo bargo ya rufe jikinsa koda mami ta dawo d'akin ATA na bacci ta zauna gefensa tare da zuba masa idanunta tana jin wani irin qaunar d'anta na ratsata bata iya dogon fushi dashi hakazalika bata son ta rasa shi. hawaye ne ya fara bin kuncinta ji take a duniya data rasashi gara ta rasa komai dan idan ta rasashi ta ina zata cigaba da rayuwa?" ina bazata iya ba bazata iya jurar rasashi ba gara ita ta bar duniyar tun kafin taga mutuwarsa ahankali ta mike tana goge hawayen idanunta ta qarasa ta rage masa karfin ac sannan ta canza masa wutar d'akin zuwa mara haske ta duka daidai fuskarsa tayi masa addua sannan ta fita daga d'akin ."
Washgari tun da yayi sallah ya koma bacci har karfe goma bai tashi ba yana kwnace yana sharar bacci shigowar mami yafi sau uku dubashi yana bacci sai dai ta kalli fuskarsa ta fita sai wajen shadaya da wasu mintuna ya tashi hanyar bathroom ya nufa ya fad'a yayi wanka ya fito yana goge sansar jikinsa ya sanya kananan kaya masu matukar kyau he look very attractive kullum ka kallesa qara kyau yake ya d'auki kwalbar turare yana feshe jikinsa yana fesa turare kwakwaluwarsa na tunanin maryama da sauri ya ajiye kwalban turaren hannunsa ya qarasa inda ya ajiye kayansa na jiya daya cire ya dauki dogon wondonsa ya shiga laluba wondon cikin kankanin lokaci ya ciro agogon sarkarta .yayi shiru yana kallon agogon yana ganin tsinysiyar hannunta aciki "mai yasa zuciyata ta damu akanki ? zuciyarsa tace "kasani ko ubangiji ne ya turo maka ita cikin rayuwarka da wata manufa a boye kayi duk yadda zakayi tayi aiki akarkashinka sosai ya dinga jin damuwa akan abinda yayi mata abu ne da bai tabayi ba .wai ya kai hanunsa jikin wata mace da sunan ta burgeshi ya dauki kusan mintuna goma yana kallon agogon tsarkar sannan ya bud'e durowarsa ya jefa ciki ya fito yana taku . "
cike da isa yake taka step, tun daga kan step yake jiyo sautin muryar baba qarami yana tafiya da kyar har ya sauko kasa ya tarar da mami zaune a inda ta saba zaman a parlour'n gabanta kuma baba qarami ne zaune yana magana cikin tsananin fushi tunda yayi masa kallo d'aya ya dauke kanshi bai sake kallon inda suke ba ya wuce dining ya dibi abinci da kanshi ya a zauna akan kujerar dake kallon step bayansa kawai zasu iya hangowa haka zalika duk abinda suke fad'a yana jinsu bayan ya gama cin abinci ya d'aga kanshi yana kallon agogon dake manne a parlour'n dake walwalin haske karfe 12:00 na safe ne yanzu mikewa yayi ya qarasa gurin mami yace "sweetheart ni zan fita mami tace "kai da baka da lafiya ina kuma zaka ka dinga hutawa dan Allah ?" numfashi kawai ya sauke batare da yace komai ba "ka zauna akwai maganar da babanka yazo dashi shiru yayi yaki zama "banason musu kayi abinda nace "a natse ya samu waje ta zauna still bai kalli inda baba qarami yake ba bare ya gaishesa "magana ce yazo daita akan hindu me kasani akai ?zuciyar ata a dake ya fad'a mata komai game da abinda ta aikata ."
ahankali ta tura kofar parlour'nsa ta shiga duhu falon dan haka ta kunna wuta nan da nan haske ya haskaka koina a parlour'n sai dai bata gansa ba dan haka ta nufi hanyar bedroom dinsa ta shiga nan ta iskeshi tsaye ya jingina jikinsa da bango d'akin yayi sama da kanshi hawaye ne kwance acikin idanunshi yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa ya rasa meke masa dadi arayuwarsa bai san ta ina zai fara ba ,komai ya rigada ya tsaya masa gabad'aya baya jin dadin rayuwarsa ,ya kasa fahimtar kansa ko kuma yace yau tazo masa da abubuwa da yawa wanda duk tarin damuwa ne akan wanda yake ciki ya dinga jin kamar ya kashe kansa ya huta da rayuwar da yake ."
lumshe tsumammun idanunshi yayi sai ga hawaye sharrr na bin kuncinsa "adamcy nah ! ".mami ta kira sunansa cikin tsananin tashin hankali har jikinta na rawa . amatukar firgice ya tsaida kwayar idanunshi dake cike da ruwan hawaye akanta qirjinsa na wani irin dokawa da sauri dan bai ji motsin shigowarta ba sai sautin muryarta wani irin zazzafan numfashi ya sauke yana sake maida kanshi sama tare da ciro hanky ya shiga d'auke hawayensa"lafiyarka kake zubar da hawaye adamcy ?ta tambayesa cikin tsananin tashin hankali dan duk abinda zai sashi zubar da hawaye baqaramin abu bane da muninsa ya wuce misali. shiru yayi ya kasa magana dan bai san me zai fad'a mata ba "kayi min magana mana adamcy dan kasa har zuciyata ta fara tsinkewa."
da yatsan hannunsa ya nuna mata daidai saitin zuciyarsa dake bugawa fiyye da kaida ."sake matsoshi tayi sosai tana cewa "meke damunka "?"zuciyata sweet.." yana kai wa nan yayi shiru ya kasa cigaba da maganar idanunshi na sake cikowa da ruwan hawaye"me ya samu zuciyarka ?" ta sake tambayarsa hankalinta na qara tashi "I don't know what's wrong with me sweetheart amman dai nasan zuciyata kullum ciwo take min"."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun " allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta "abinda mami ta shiga furtawa kenan tana sake maimaitawa " i know something is wrong with my heart wallahi sweetheart akwai ciwo mai zafi acikin zuciyata wanda zai iya kasheni nan kusa .."
nan da nan fuskar mami ta qara sauyawa hankalinta a matukar tashe tace "ka dinga sausautawa kanka adamcy da yawon tunani ,ka dinga addua akan duk abinda ya dameka addua tana canzawa bawa qaddararsa kuma tana saka natsuwa acikin zuciyar bawa "numfashi ya sauke da karfi yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ,magana yake son yi amman zafin da zuciyarsa keyi ya hana shi cewa uffan "kasamu natsuwa adamcy ka dinga furta wannan adduar zaka samu natsuwa da sausauci a wajen Allah zai yaye maka dukkanin damuwarka "allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta ahankali ya sauke idanuwanshi ya tsura ma mami kawai yana kallonta cikin yanayi na tsanani damuwa "ka sani idan wani abu ya sameka nice farkon wacce zata fara shiga damuwa ga kuma d'an cikin jikin maryam wanda bamu san abinda zata haifa ba karka bari muyi maraicinka. adamcy kasan yadda nake sonka idan na rasaka zan shiga damuwa a kullum adduata na mutu na barka a duniya ba ka mutu ka barni ba tunda ta fara magana bai ce mata uffan ba sai ma ciro wayarsa da yayi ya soma neman layin likitansa muryarsa ce ta katse mami daga maganar da take masa ahankali yake magana tamkar mara lafiya "doctor kazo ka dubani please ".daga haka bai sake cewa komai ba ya katse kiran d'akin yayi tsit tamkar babu mutane acikinsa ."
Ahankali ya soma d'aga kafafunsa zuwa Kan gado ya fad'a ya kwanta flat ransa duk babu dadi yayinda idanunshi na kallon saman d'akin babu abinda yake gani sai kwayar idanun maryama da yatsun hannun ta da sautin zazzakar muryarta mami tazo ta zauna kusa dashi tana daura hannunta saman kansa tana masa sannu "bayan mintuna shabiyar sai ga doctor ya shigo tare da sallama tashi yayi ya zauna ya jingina bayansa da abun gado yana sauke numfashi da kyar tare da yiwa doctor bayanin yadda yake ji batare da 'bata lokaci ba doctor ya fara masa gwaje gwaje bayan doctor ya gama yayi masa allura sannan yace "ranka ya dade jininka ne ya hau kad'an yana da kyau ka dinga saukakawa kanka wasu abubuwa dan zuciyarka na bukatar hud'u yanzu dai nayi maka allurar bacci in sha allahu kana tashi zakaji daidai Allah ya baka lafiya ya ajiye masa magunguna yace zai wuce ."mami tayi masa godiya adaidai lokacin da doctor ke had'a kayansa yayi mata sallama ya wuce ."
"Ka tashi kayi sallah magriba kafin bacci ya d'aukeka sannan me za'a kawo maka coffe ko tea "any one sweetheart." ya furta tare da mikewa da kyar ya shiga bathroom ita kuma mami ta fita kawo masa coffe dan tasan shi yafi bukata wanka ya fara sannan yayi alwala ya fito ya cire kayan jikinsa ya canza zuwa jallabiya brown colour mai ratsin baki ya isa inda abun sallarsa yake ya gabatar da sallah bayan ya idar ya koma Kan gado ya kwanta lamo tare da janyo bargo ya rufe jikinsa koda mami ta dawo d'akin ATA na bacci ta zauna gefensa tare da zuba masa idanunta tana jin wani irin qaunar d'anta na ratsata bata iya dogon fushi dashi hakazalika bata son ta rasa shi. hawaye ne ya fara bin kuncinta ji take a duniya data rasashi gara ta rasa komai dan idan ta rasashi ta ina zata cigaba da rayuwa?" ina bazata iya ba bazata iya jurar rasashi ba gara ita ta bar duniyar tun kafin taga mutuwarsa ahankali ta mike tana goge hawayen idanunta ta qarasa ta rage masa karfin ac sannan ta canza masa wutar d'akin zuwa mara haske ta duka daidai fuskarsa tayi masa addua sannan ta fita daga d'akin ."
Washgari tun da yayi sallah ya koma bacci har karfe goma bai tashi ba yana kwnace yana sharar bacci shigowar mami yafi sau uku dubashi yana bacci sai dai ta kalli fuskarsa ta fita sai wajen shadaya da wasu mintuna ya tashi hanyar bathroom ya nufa ya fad'a yayi wanka ya fito yana goge sansar jikinsa ya sanya kananan kaya masu matukar kyau he look very attractive kullum ka kallesa qara kyau yake ya d'auki kwalbar turare yana feshe jikinsa yana fesa turare kwakwaluwarsa na tunanin maryama da sauri ya ajiye kwalban turaren hannunsa ya qarasa inda ya ajiye kayansa na jiya daya cire ya dauki dogon wondonsa ya shiga laluba wondon cikin kankanin lokaci ya ciro agogon sarkarta .yayi shiru yana kallon agogon yana ganin tsinysiyar hannunta aciki "mai yasa zuciyata ta damu akanki ? zuciyarsa tace "kasani ko ubangiji ne ya turo maka ita cikin rayuwarka da wata manufa a boye kayi duk yadda zakayi tayi aiki akarkashinka sosai ya dinga jin damuwa akan abinda yayi mata abu ne da bai tabayi ba .wai ya kai hanunsa jikin wata mace da sunan ta burgeshi ya dauki kusan mintuna goma yana kallon agogon tsarkar sannan ya bud'e durowarsa ya jefa ciki ya fito yana taku . "
cike da isa yake taka step, tun daga kan step yake jiyo sautin muryar baba qarami yana tafiya da kyar har ya sauko kasa ya tarar da mami zaune a inda ta saba zaman a parlour'n gabanta kuma baba qarami ne zaune yana magana cikin tsananin fushi tunda yayi masa kallo d'aya ya dauke kanshi bai sake kallon inda suke ba ya wuce dining ya dibi abinci da kanshi ya a zauna akan kujerar dake kallon step bayansa kawai zasu iya hangowa haka zalika duk abinda suke fad'a yana jinsu bayan ya gama cin abinci ya d'aga kanshi yana kallon agogon dake manne a parlour'n dake walwalin haske karfe 12:00 na safe ne yanzu mikewa yayi ya qarasa gurin mami yace "sweetheart ni zan fita mami tace "kai da baka da lafiya ina kuma zaka ka dinga hutawa dan Allah ?" numfashi kawai ya sauke batare da yace komai ba "ka zauna akwai maganar da babanka yazo dashi shiru yayi yaki zama "banason musu kayi abinda nace "a natse ya samu waje ta zauna still bai kalli inda baba qarami yake ba bare ya gaishesa "magana ce yazo daita akan hindu me kasani akai ?zuciyar ata a dake ya fad'a mata komai game da abinda ta aikata ."