Sashe 27
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
nan da nan shukura tayi abinda aunty salma ta umarceta"ki lashe kije zaki ga irin tarbar da zai miki sannan zaki ga irin tarbar da zai yiwa maryama zabinsa ,matsawar kika ga tarban da yayi miki bai miki ba ko ya had'a da tozarci ko cin fuska karki 'bata ranta ki dawo kawai amman kuma wallahi wallahi sai nayi masa abinda sai ya wulaqanta akan soyayyarki sai ya dawo yana kuka akanki, ke sai yayi sambatu akanki sai ya fifitaki akan uwar data kawo shi duniya ".
"yauwa mamana shiyasa nake mugun sonki allah dai ya bar min mamana ."maza kije garesa cike da Kamala da mutuntaka da kamewa ki shirya duk wasu kalamai masu sanyi da sanyaya zuciya da zakiyi amfani dashi allah ya bamu sa'a wani irin numfashi shukura ta sauke tare da rungume aunty salma ajikinta tana furta "ameen !sannan ta saketa ta juya da sauri ta bar d'akin ta nufi d'akin da yusif yake ."
ahankali ta shiga d'akin bakinta d'auke da sallama yana nan zaune kamar yadda suka fita suka barshi sai dai idanunshi a runtse suke suna kallon saman d'akin sallamar daya ji anyi ne yasashi bud'e idanu tare da sauke idanuwanshi abakin kofar d'akin suka sauka akan shukura dake tsaye tana kallonsa fuskarta cike da fara'a do cikin ido suke kallon juna ."
Wasu abubuwa ya dinga ganin suna fitowa daga cikin kwayar idanunta suna shiga nashi nan da nan ya gyara zamansa sosai yana cigaba da kallonta cikin wani irin farinciki mara misaltuwa tamkar lokacin ya fara ganinta arayuwarsa cike da tsananin farinciki yace "ya kika tsaya qaraso gareni zuciyata Ke take muradin son gani "cike da karairaya shukura ta dinga taku har ta qaraso ta zauna kusa dashi ya zuba mata ido kawai yana sakar mata tsadadden murmushinsa cikin shukin qaunarta daya ji daga sama "yaya yusif !"
Ta kira sunansa cikin wata irin murya idanuwanshi kawai ya zuba mata batare da yace mata komai ba " akace daya daga cikinmu zata maye maka gurbin maryama a wajenka me ka gani ."?murmushi yayi kawai "gabanta ya shiga fad'uwa amman data tuna irin tarban da yayi mata a yanzu sai taji wani sabon gwarin gwiwa ya shigeta "ina son na maye gurbin maryama acikin zuciyarka me zaka iya cewa ?"ai wannan ba komai bane na amince dake dan ma kin fita dacewa dani ".
ta lumshe idanunta kana tace "amman kace domin maryama kawai kazo gidan nan ba dan wasu yan iska ba ?tayi masa tambayar tana mai kafesa da idanunta yayi shiru yana kallonta qirjinsa na wani irin bugawa da karfi "maryama kad'ai zuciyarka ke muradin son gani bamu marasa kamun kai ba ?ya kai hannusa ya riko hannunta gam cikin nashi yana matsewa "yaushe na fad'i haka ?ni babu wacce zuciyata ke muradin gani sai ke murmushi tayi kawai aranta tace "aiki yayi tasiri kanan "ta qara damke hannunsa dake cikin nashi "baka ci komai da'aka kawo maka ba".
"na koshi domin ganinki ma kawai ya kosar dani "ya fad'a a daidai lokacin da kausar ta shigo hannunta rike dana maryam ."wani irin bugu zuciyar kausar yayi da karfi sakamakon ganin yanayinsu dan ita maryama daman ta rigada ta cire samunsa acikin ranta ganinsu haka ma bai d'aga mata hankali ba ."
cikin wani salon jan hankali shukura ta tsura masa ido tana kallon kwayar idanunshi tana jin wani irin shaukin sonshi na ratsata yayinda maryama ta zame hannun ta cikin na kausar ta samu waje ta jingina bayanta da bangon d'akin Tare da sunkuyar da kanta kasa tana kallon zara zaran yatsun kafafunta dan bata son ganinsu bancin darajan kausar ma da ko hanyar d'akin bazata biyo ba ."
cike da tashin hankali kausar tace "yaya meye haka kuma ?"mai nayi kausar ?shima ya tambayeta yana jin kamar ana soka masa allura a gabad'aya ilahirin jikinsa "jikin maryama ya qara yin sanyi rauninta ya soma bayyana idanunta suka fara ciccikowa da ruwan hawaye "shikenan shima an gama dashi "ta fad'a acikin zuciyarta "dan Allah malama ki sakar masa hannu"kausar ta fad'a tana zabga mata harara shukura tayi murmushin mugunta tana zare hannunta cikin nashi tsaki kausar taja sannan ta soma zayyane masa duk abinda maryama ta fad'a ".
Amman da mamakinta sai ji tayi yace "sai me idan ta fad'a miki haka ?ta sake kallonsa a matukar tsorace tana cewa "yaya me kake nufi da fad'ar haka ?ina nufin yanzu shukura nike so kuma ita zan aura "ya salam yaushe wannan alamarin ya faru ?amman ko akan hanyarmu ta zuwa nan babu wannan tsarin a zuciyarka ? maganar maryama kake tayi babu tsarin auren wata shukura arayuwarka "to yanzu na canza raayina ita nake so kuma ita zan aura " a kan me ma zan auri wannan yarinyar? ya fad'a yana nuna maryama da babban yatsan hannunsa ."
"kausar ta rikice ta gigice ta waiga ta kalli maryama dake tsaye shiru tana ciza lips dinta na kasa "haba yaya me yasa zakayi haka ?me yasa zaka sa'ba alkwarin da kayiwa mumy ?me yasa ka furtawa maryama cewar kana sonta zaka aureta yanzu kuma kazo da wata magana da hankali bazai d'auka ba "why why !!? yaya dan allah karkayi haka,ka dawo haiyacinka karka yiwa maryama haka tayi maganar cike da tashin hankali idanunta na kawo ruwan hawaye ."
"Duk yanzu na daina jin komai akanta sai dai ko a cikin masu mana aiki a gidanmu zan bawa wani shawarar ya auri wannan yarinya,amman yanzu sai shukura itace zabina a halin yanzu ma na kagauta na d'auketa daga wannan gidan dan ta fi karfin zamansa ita din ta dabance acikin zuciyata Ina kallonta ina jin farinciki araina "
hawaye dake makale acikin idanunta maryama suka zubo akan kuncin tayi sauri tasa hannunta ta goge yayinda zuciyar shukura tayi mata sanyi ta qara tabbatarwa kanta aikinsu yayi tasiri akanshi ta d'auko ruwan lemu ta tsiyaya a cup ta mikawa yusif tana cewa "ungo sha kaji sanyi aranka "yasa hannu ya kar'ba yana sakar mata murmushi cikin tsananin tashin hankali kausar tace "karka sa'ba alkwarin daka d'auka ,da maryama kawai kafi dacewa ba da wata shukura ba ka bud'e idanunka da kyau please ."
cikin wata irin murya mai sanyi da tausasawa maryama tace "kausar karki d'aga hankalinki dan baya cikin hankalinsa da natsuwarsa hasalima bazai ta'ba fahimtarki ba a halin yanzu ,kiyiwa danuwanki addua dani da shukura duk abu d'aya ne bazan ta'ba bakinciki dan yusif ya canza ni da shukura ba fatana allah ya basu zaman lafiya tana cikin fad'ar haka taji an fasa kuka abayanta mai kukan tana fadin" lahaula wala kuwwata inna lillahi wa inna ilahi rajiun wannan wani irin massefa ne haka ?
Duk suka juya umma suka gani tsaye cikin matsanancin tashin hankali "Shukura me maryama tayi miki kike shiga rayuwarta ?amman Kisani allah baya bacci kuma zai saka mata da kyakkyawan sakayya Ke kuma zaki ga muguwar sakayya dake da uwarki "idanu kawai yusif ya zuba mata ya kasa cewa komai "kiyi mata na malam yahuza ta hakura ta bar miki shi yanzu kuma yusif din kike so ?".
"umma gashi nan ki tambayesa bani nace ina sonshi ba shine da kanshi ya canza dani " yi min shiru munafukar allah daga Ke har uwarki zaku girba abinda kuka shauka ,da izinin allah sai maryama ta samu wanda yafi yusif komai kausar ta bukaci umma tayi mata qarin bayani akan mlm yahuza batare da 'bata lokaci ba ta zayyane mata komai ."
"uhmm lallai maryam kina cikin tashin hankali allah ya fitar dake kawai zan iya cewa sannan ta cire wayarta daga cikin fost dinta ta kar6i mukullin mota daga hannun yusif ta fice waje tana neman layin mumy yusif ya cigaba da yin shiru maryama ta juya jiki a sanyaye ta bar d'akin tana goge hawaye haka zalika umma kasa cigaba da tsayuwa tayi zuciyarta na tafarfasa ta shige d'akanta tana kuka ."
yaya sadam dake tsaye yana waya ya hango fitowar maryama tana tafiya tana goge hawaye ya bita da kallo Kamar ya tsaidaita yaji damuwarta sai kuma ya rabu daita da zumar zai nemeta daga baya ya cigaba da wayar da yake cikin haka kiran umma ya shigo wayarsa daman what's app call yake ."ya katse kiran domin ya d'auki kiran ummah kiran ya katse ya lalubo qaramar wayarsa yayi mamakin ganin missed call dinta dayawa ashe a silet yake "
ya kirata dan baya son ya shiga sai ya gama wayar da yake ,tana d'auka yaji muryarta can qasa tana kiran sunansa ya amsa yana tambayarta "lafiya ummah naji muryarki haka ?tace sadam kana ina ne ?ina cikin gida " tace ka shigo yanzu yanzu "okay! kawai ya fad'a ya soma tafiya cikin sauri ya shigo d'akinta."ya garasa inda take zaune yana cewa "lafiya umma meke damunki kamar ma kinyi kuka ?."
wani sabon kukan ta fashe masa dashi tana zayyane masa abinda ya faru yace "ikon allah anya kuwa lafiya ?ina fa lafiya sadam kai ma kasan ba lafiya ba ,"yanzu dai sai a kira abba aji me zai ce ,ai wad'an nan mutanen abun nasu babu imani ai bazasu bar iyayensa ma haka ba duk abinda zasuyi dan su juyar da hankularsu zasuyi ."
jikin yaya sadam yayi sanyi ya kasa cigaba da magana "wallahi da ina da inda zan kai maryama ta cigaba da rayuwarta da nayi dan ina son taji dadi, maryama tasha wahala a hannun mutanen gidan nan sam sam basa son ganin cigabanta .""Kiyi hakuri umma komai zai wace babu abinda yafi karfin addua maryama malama ce nasan zatayi addua ."ban ta'ba shiga tashin hankali irin na yau ba domin har ga allah naso auren maryama da yusif amman da izinin allah bazasu ci bulus ba duk abinda sukai mata bazai tafi a banza ba sai allah yayi mana maganinsa ."
"yauwa mamana shiyasa nake mugun sonki allah dai ya bar min mamana ."maza kije garesa cike da Kamala da mutuntaka da kamewa ki shirya duk wasu kalamai masu sanyi da sanyaya zuciya da zakiyi amfani dashi allah ya bamu sa'a wani irin numfashi shukura ta sauke tare da rungume aunty salma ajikinta tana furta "ameen !sannan ta saketa ta juya da sauri ta bar d'akin ta nufi d'akin da yusif yake ."
ahankali ta shiga d'akin bakinta d'auke da sallama yana nan zaune kamar yadda suka fita suka barshi sai dai idanunshi a runtse suke suna kallon saman d'akin sallamar daya ji anyi ne yasashi bud'e idanu tare da sauke idanuwanshi abakin kofar d'akin suka sauka akan shukura dake tsaye tana kallonsa fuskarta cike da fara'a do cikin ido suke kallon juna ."
Wasu abubuwa ya dinga ganin suna fitowa daga cikin kwayar idanunta suna shiga nashi nan da nan ya gyara zamansa sosai yana cigaba da kallonta cikin wani irin farinciki mara misaltuwa tamkar lokacin ya fara ganinta arayuwarsa cike da tsananin farinciki yace "ya kika tsaya qaraso gareni zuciyata Ke take muradin son gani "cike da karairaya shukura ta dinga taku har ta qaraso ta zauna kusa dashi ya zuba mata ido kawai yana sakar mata tsadadden murmushinsa cikin shukin qaunarta daya ji daga sama "yaya yusif !"
Ta kira sunansa cikin wata irin murya idanuwanshi kawai ya zuba mata batare da yace mata komai ba " akace daya daga cikinmu zata maye maka gurbin maryama a wajenka me ka gani ."?murmushi yayi kawai "gabanta ya shiga fad'uwa amman data tuna irin tarban da yayi mata a yanzu sai taji wani sabon gwarin gwiwa ya shigeta "ina son na maye gurbin maryama acikin zuciyarka me zaka iya cewa ?"ai wannan ba komai bane na amince dake dan ma kin fita dacewa dani ".
ta lumshe idanunta kana tace "amman kace domin maryama kawai kazo gidan nan ba dan wasu yan iska ba ?tayi masa tambayar tana mai kafesa da idanunta yayi shiru yana kallonta qirjinsa na wani irin bugawa da karfi "maryama kad'ai zuciyarka ke muradin son gani bamu marasa kamun kai ba ?ya kai hannusa ya riko hannunta gam cikin nashi yana matsewa "yaushe na fad'i haka ?ni babu wacce zuciyata ke muradin gani sai ke murmushi tayi kawai aranta tace "aiki yayi tasiri kanan "ta qara damke hannunsa dake cikin nashi "baka ci komai da'aka kawo maka ba".
"na koshi domin ganinki ma kawai ya kosar dani "ya fad'a a daidai lokacin da kausar ta shigo hannunta rike dana maryam ."wani irin bugu zuciyar kausar yayi da karfi sakamakon ganin yanayinsu dan ita maryama daman ta rigada ta cire samunsa acikin ranta ganinsu haka ma bai d'aga mata hankali ba ."
cikin wani salon jan hankali shukura ta tsura masa ido tana kallon kwayar idanunshi tana jin wani irin shaukin sonshi na ratsata yayinda maryama ta zame hannun ta cikin na kausar ta samu waje ta jingina bayanta da bangon d'akin Tare da sunkuyar da kanta kasa tana kallon zara zaran yatsun kafafunta dan bata son ganinsu bancin darajan kausar ma da ko hanyar d'akin bazata biyo ba ."
cike da tashin hankali kausar tace "yaya meye haka kuma ?"mai nayi kausar ?shima ya tambayeta yana jin kamar ana soka masa allura a gabad'aya ilahirin jikinsa "jikin maryama ya qara yin sanyi rauninta ya soma bayyana idanunta suka fara ciccikowa da ruwan hawaye "shikenan shima an gama dashi "ta fad'a acikin zuciyarta "dan Allah malama ki sakar masa hannu"kausar ta fad'a tana zabga mata harara shukura tayi murmushin mugunta tana zare hannunta cikin nashi tsaki kausar taja sannan ta soma zayyane masa duk abinda maryama ta fad'a ".
Amman da mamakinta sai ji tayi yace "sai me idan ta fad'a miki haka ?ta sake kallonsa a matukar tsorace tana cewa "yaya me kake nufi da fad'ar haka ?ina nufin yanzu shukura nike so kuma ita zan aura "ya salam yaushe wannan alamarin ya faru ?amman ko akan hanyarmu ta zuwa nan babu wannan tsarin a zuciyarka ? maganar maryama kake tayi babu tsarin auren wata shukura arayuwarka "to yanzu na canza raayina ita nake so kuma ita zan aura " a kan me ma zan auri wannan yarinyar? ya fad'a yana nuna maryama da babban yatsan hannunsa ."
"kausar ta rikice ta gigice ta waiga ta kalli maryama dake tsaye shiru tana ciza lips dinta na kasa "haba yaya me yasa zakayi haka ?me yasa zaka sa'ba alkwarin da kayiwa mumy ?me yasa ka furtawa maryama cewar kana sonta zaka aureta yanzu kuma kazo da wata magana da hankali bazai d'auka ba "why why !!? yaya dan allah karkayi haka,ka dawo haiyacinka karka yiwa maryama haka tayi maganar cike da tashin hankali idanunta na kawo ruwan hawaye ."
"Duk yanzu na daina jin komai akanta sai dai ko a cikin masu mana aiki a gidanmu zan bawa wani shawarar ya auri wannan yarinya,amman yanzu sai shukura itace zabina a halin yanzu ma na kagauta na d'auketa daga wannan gidan dan ta fi karfin zamansa ita din ta dabance acikin zuciyata Ina kallonta ina jin farinciki araina "
hawaye dake makale acikin idanunta maryama suka zubo akan kuncin tayi sauri tasa hannunta ta goge yayinda zuciyar shukura tayi mata sanyi ta qara tabbatarwa kanta aikinsu yayi tasiri akanshi ta d'auko ruwan lemu ta tsiyaya a cup ta mikawa yusif tana cewa "ungo sha kaji sanyi aranka "yasa hannu ya kar'ba yana sakar mata murmushi cikin tsananin tashin hankali kausar tace "karka sa'ba alkwarin daka d'auka ,da maryama kawai kafi dacewa ba da wata shukura ba ka bud'e idanunka da kyau please ."
cikin wata irin murya mai sanyi da tausasawa maryama tace "kausar karki d'aga hankalinki dan baya cikin hankalinsa da natsuwarsa hasalima bazai ta'ba fahimtarki ba a halin yanzu ,kiyiwa danuwanki addua dani da shukura duk abu d'aya ne bazan ta'ba bakinciki dan yusif ya canza ni da shukura ba fatana allah ya basu zaman lafiya tana cikin fad'ar haka taji an fasa kuka abayanta mai kukan tana fadin" lahaula wala kuwwata inna lillahi wa inna ilahi rajiun wannan wani irin massefa ne haka ?
Duk suka juya umma suka gani tsaye cikin matsanancin tashin hankali "Shukura me maryama tayi miki kike shiga rayuwarta ?amman Kisani allah baya bacci kuma zai saka mata da kyakkyawan sakayya Ke kuma zaki ga muguwar sakayya dake da uwarki "idanu kawai yusif ya zuba mata ya kasa cewa komai "kiyi mata na malam yahuza ta hakura ta bar miki shi yanzu kuma yusif din kike so ?".
"umma gashi nan ki tambayesa bani nace ina sonshi ba shine da kanshi ya canza dani " yi min shiru munafukar allah daga Ke har uwarki zaku girba abinda kuka shauka ,da izinin allah sai maryama ta samu wanda yafi yusif komai kausar ta bukaci umma tayi mata qarin bayani akan mlm yahuza batare da 'bata lokaci ba ta zayyane mata komai ."
"uhmm lallai maryam kina cikin tashin hankali allah ya fitar dake kawai zan iya cewa sannan ta cire wayarta daga cikin fost dinta ta kar6i mukullin mota daga hannun yusif ta fice waje tana neman layin mumy yusif ya cigaba da yin shiru maryama ta juya jiki a sanyaye ta bar d'akin tana goge hawaye haka zalika umma kasa cigaba da tsayuwa tayi zuciyarta na tafarfasa ta shige d'akanta tana kuka ."
yaya sadam dake tsaye yana waya ya hango fitowar maryama tana tafiya tana goge hawaye ya bita da kallo Kamar ya tsaidaita yaji damuwarta sai kuma ya rabu daita da zumar zai nemeta daga baya ya cigaba da wayar da yake cikin haka kiran umma ya shigo wayarsa daman what's app call yake ."ya katse kiran domin ya d'auki kiran ummah kiran ya katse ya lalubo qaramar wayarsa yayi mamakin ganin missed call dinta dayawa ashe a silet yake "
ya kirata dan baya son ya shiga sai ya gama wayar da yake ,tana d'auka yaji muryarta can qasa tana kiran sunansa ya amsa yana tambayarta "lafiya ummah naji muryarki haka ?tace sadam kana ina ne ?ina cikin gida " tace ka shigo yanzu yanzu "okay! kawai ya fad'a ya soma tafiya cikin sauri ya shigo d'akinta."ya garasa inda take zaune yana cewa "lafiya umma meke damunki kamar ma kinyi kuka ?."
wani sabon kukan ta fashe masa dashi tana zayyane masa abinda ya faru yace "ikon allah anya kuwa lafiya ?ina fa lafiya sadam kai ma kasan ba lafiya ba ,"yanzu dai sai a kira abba aji me zai ce ,ai wad'an nan mutanen abun nasu babu imani ai bazasu bar iyayensa ma haka ba duk abinda zasuyi dan su juyar da hankularsu zasuyi ."
jikin yaya sadam yayi sanyi ya kasa cigaba da magana "wallahi da ina da inda zan kai maryama ta cigaba da rayuwarta da nayi dan ina son taji dadi, maryama tasha wahala a hannun mutanen gidan nan sam sam basa son ganin cigabanta .""Kiyi hakuri umma komai zai wace babu abinda yafi karfin addua maryama malama ce nasan zatayi addua ."ban ta'ba shiga tashin hankali irin na yau ba domin har ga allah naso auren maryama da yusif amman da izinin allah bazasu ci bulus ba duk abinda sukai mata bazai tafi a banza ba sai allah yayi mana maganinsa ."