← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 102

Sashe 87

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

        Shabiyu ne na rana yana tsaye acikin office dinsa sanye da t shirt long sleeve light puppy da wondo baki sai tie baki zagaye da wuyansa ya tura hannuwansa  duka cikin aljihun wondonsa wani irin kamshi jikinsa ke fitarwa mai sanya natsuwa da kwantar da hankali fuskar nan tashi  a murtuke  zariya ya soma yi acikin office din yana tunanin maryama wanda  bai san dalili ba tunaninta yaki barinsa babu abinda zuciyarsa yake kwadayin sake gani kamarta  kafin ahankali yayi burki a daidai mazauninsa turo kofar office din akayi batare da an nemi izinin shigowa ba ya kalli kofar ammar ya gani  yanayin yadda yaga fuskarsa ya dan fahimci akwai wani abu  yana gama shigowa ya soma magana cikin tsananin fushi "burinka ya cika maryama tayi aure “
“so what idan tayi aure what’s my business with her ?wai menene matsalarka adam ?"da nayi me kenan ?wallahi ban san baka da sa'a arayuwarka ba sai da maryama tayi aure "tô ni menene damuwa ta da aurenta ?kaga dan Allah karka sake min maganar ta karka qara min damuwa akan wanda nake ciki "kai ne kuwa kake da  damuwa daita ."hade rai ata  yayi sosai yana yiwa amar wani irin mugun kallo mai bugar da zuciya "kasani inada dalilina na son ku hadu daita tun kafin tayi aure.ata yayi taku daya biyu yana mai juya masa baya wallahi da ka daure kaga maryama da  zaka fahimci abinda na gani har yasa nake son ku hadu  daita."

juyowa ata  yayi ya fuskancesa yana hura masa hanci tare da kai hannu yana sunce tie din wuyansa "kai ma tunda kaga na na nace ai ya kamata kayi amfani da sense dinka ,bazaka ta'ba jin dadin wata mace a duniya ba sama daita" look ammar bana son damuwa ,"my friend you have to  use your common sense and think akwai dalili mai karfi dayasa naso ku hadu "ata ya sauke hanunsa daga wuyansa ya maida cikin ajihunsa yana nazarin maganar ammar "ba dai ka rasa maryama ba kasani zuciyarka zatayi  nadama fiyye da kowani nadama da d'an adam keyi a rayuwarsa "ya d'ago ya tsurawa ammar idanunshi tare da cire hannunsa d'aya cikin aljihunsa ya rike kugunsa," wasu ma suna janyota jikinsu domin su amfana daita bare kai da ..."wai meye haka ammar ?ka dameni ka cika min kunne da surutun banza da wofi dole ne sai na aureta ko dole sai na janyota jikinta ?"kaga enough please ka rabani da maganar wata maryama din banza  bana son jin ko sunanta bare na aureta "yayi maganar a tsawace yana furzar da iska mai zafi "ai kuwa ka shiryawa shiga tashin hankali da damuwa domin duk ranar da zaka ganta kuma amatsayin matar aure sai kayi nadamar rashin haduwarku akan lokaci ,kuma lallai bazan daina fad'a maka rashin haduwa daita  damuwa ne  akan damuwa kuma har qarshen rayuwarka bazaka daina da kasani ba kai in takaice maka zaka iya rasa ranka ". ata ya dafe goshinsa da hannunsa daya "ammar kana rikita min kwakwaluwa zuciyata tana tsinkewa magangunka gabad'aya suna nema tarwatsa min zuciya gabad'aya na kasa fahimtar abinda kake nufi yayi maganar kamar zai yi kuka tare da zama akan kujera  yana kallonsu "you are mad adam yanzu abinda ya rage maka ka zauna kayi tunani akan maganganuna " yana gama fad'ar haka ya buga masa table din gabansa ya juya  ya fita a fusace ."

ata ya kai hannu goshinsa kafin daga baya ya soma  jujjuya jikinsa akan kujera wani irin ihu yayi yana kai hannusa ya ture tarin file din dake Kan table sannan ya mike tsaye zambur Kmr zaki ya dafe kanshi gabad'aya ya rasa meke masa dadi  dan wani irin abu yaji yana yawo acikin ilahirin jikinsa mai kama da abinda yake ji akan mafarkinsa yau shine karo na biyu da yaji wani abu wanda ya shafi mafarkinsa akan wata mace "wacece mai zanen creation wacece maryama datai aure coz the same abu yake ji akansu wanda yake da kusanci da abinda yake ji akan mafarkinsa “karka matso kusa dani domin bazan ta'ba kasancewa cikin wawayen mata masu cin amanar mazajensu ba itama matar aure ce “ya rabbi what’s wrong with me ?yana  cikin wannan halin james yayi knocking yana neman izinin shiga sai da ata ya dauki lokaci sannan yace "coming !" ya shiga cikin taka tsantsa "mai gida ina son nayi magana da kai ko zan iya magana ?" leave!"  mai gida magana ce mai mahimanci "I said  leave bana bukatar jin komai yanzu."da sauri ya juya ya fice .cikin company ranar kam kowa ya kama kanshi dan dukkanin alamun sun nuna an tabosa, duk kuma wanda yayi kuskuren shiga track dinsa zai sha bala'i idan ma bai ce ya kori mutun ba har ya dawo gida maganar ammar na damunsa cikin rai sai yayi kamar ya kirasa   ya sake masa karin bayani  sai muguwar zuciyarsa ta gargadesa "

Bayan sati d’aya wanda yayi daidai da kwanaki shabiyu da daura auren maryama  da yaya sadam sultana ta dirá a kasar kuma kai tsaye abdullahi estate aka nufo daita murna wajen aunty abida abun baa magana ,tun daga lokacin da sultana ta shigo estate din aunty abida ta fara aiwatar da shirinta kullum suna bangaren mami sai dai basa samun ganin ata suna samun sa’banin shiyasa yau sukai sakamakon yau .ahankali yake ssukowa daga Kan step cikin shigarsa na kullum sai kamshi yake idanunsa bai sauka akan kowa ba sai akan aunty abida da sultana kallo daya yayi masu ya dauke idanunshi ya cigaba da taku har ya wucesu ta mike ta sha gabansa tana kiran sunansa “adamcy barka da saukowa.” ya tsaya kawai yana kallonta batare da yace mata komai ba “ga sister ta kawo mana ziyara Ya ganta ta hadu ko ?still dai bai tanka mata ba tayi murmushin yake tana cewa “daman nace bari na kawota ku gaisa sultana ga cup din tea dinsa can dauko ki bashi .” jikinta na rawa ta juya ta dauko Orenge cup din dake ajiye wanda daman dan shi aka tanada ta mika masa ,sai dai bai kar’ba ba yace "am okay coz am oready late” zai wuce ta sake tsaidashi Ya tsaya cak yana duba agogon dake daure da tsintsi yar hannunsa kamr yadda kasani sultana kanwarmu ce kuma ta kware a harkar zane dan naji ance kana bukatar kwararun masu zane shiyasa nace tazo dan tasan Kan aikinta sosai idan bazaka damu ba ko zaka bata dama kaga irin nata kwarewar ?shiru yayi bai ce uffan ba “.

“nasan bazaka ta'ba zuba ma yaruwarka kasa a ido ba zaka gwada yaruwarka kaga irin nata baiwar bayan shi ma ina son ka taimaka ka bata aiki a maakatarku Z&A idan ma da hali ka barta a kusa kusa da kai wato P.A dinka dan na yi imani zaka ji dadin aiki daita dan ....”duk naji bayaninki.” ya katseta ta hanyar fad’ar haka kafin ya cigaba tayi saurin cewa “ zata joining compaing kenan ? kai amman na gode sosai  sultana bana fada miki ba bashi da matsala gashi da sauki kai ga kirki da son yanuwa gyaran murya yayi yace " ammm karki yi Godiya tukun dan bani zan bata aikin ba kiyiwa mijinki magana I know he can do more that for her “mijina kuma ?tai masa tmbyr tana kallonsa tare da nazarin maganarsa tana kallonsa ya zagayesu ya kama gabansa “nifa Aunty duk ba wannan bane matsalata ni dai kawai kisan yadda zakiyi na kasance a kusa dashi nasan komai zai zo da sauki “amman yanzu a gabanki kikaji ina masa magana zaki ce bakiji abinda yace ba, wai nayiwa Ibrahim mgn Ibrahim din da ba wuri daya suke ba .”

Dan allah ayi min afuwa posting zai koma a sati sau daya sakamakon bana samu lokaci ga hidima da mai gidana ga business ga typing sannan ina bukatar hutu Kunga abun yayi min yawa ina maku fatan alkhairi sai Saturday ko sunday in sha allahu.”

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 27

Jiki a sanyaye ATA  ya fito cikin 'bacin rai daga d'ayan bedroom dinsa wanda ya rasa dalilin 'bacin ransa , a yanzu kusan kullum ransa a 'bace yake azaba yake ji sosai a cikin zuciyarsa  so yake ya rabu da damuwar dake damunsa amman ya rasa yadda zai yi ,cike da natsuwa yake taku acikin d'akin yadda jikinsa ke fitar da kamshi mai sanyaya zuciya  haka d'akinsa ke d'auke da kamshin dad'ad'an turarukan sa .a natse  ya d'auki farin glass dinsa ya manna a kwayar idanunshi sannan ya qaraso ya d'auki agogon fata mai  tsada ya d'aura a tsintsiyar hannunsa, ya bud'e bedside domin ya d'auki wallet dinsa." ya kai hannu ya d'auka ya tura a bayan aljihun wondonsa yana qoqarin rufe bedside din ne  idanuwanshi suka sauka akan agogon sarka hannun maryama daya zamo cikin hannunsa a wancan ranar ,yayi shiru yana kallon agogon  yana jin wani iri a gaba d'aya ilahirin jikinsa, ya kusan minti goma tsaye yana  cigaba da kallon agogon gabansa na wani irin bugawa da sauri sauri tunowa da yayi matar aure ce yarinyar yasashi jan dogon tsaki yana ciza lip's dinsa."
Chapter 87 · 0% Book details