← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 102 OF 102

Sashe 102

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

“karki damu subai ba akanki bane haka allah ya qaddaromin Kiyi min fatan alkhairi.““ dan allah kiyi hakuri nasan duk laifina ne “nace karki damu ko na karba da farko haka zasu min dan da gani mai kanfani har wadan da suke aiki karkashinsa duk mahaukata ne na ma gode da ban samu aiki akarkashinsa ba suna cikin wannan halin sai ga yusura ta fito daga office din daakaita ,kusa da maryama taje ta tsaya tana tmbyarta “aikinta ta rasa adalilina aikinta da bar min “wata uwar harara yusura ta maka mata “ai gsky ne adalilinki ta rasa wancan aikin yanzu ma ta rasa wanna kenan ?subai’a ta gyada mata kai “a wani dalili ?”Ke !me ma ya kawoki ma tunda ai baa nan kike aiki ba ?karki manta da mai wannan kamfanin da A&Z duk mutun daya ne wani mahiman aiki ne ya kawoni “karku tsya bata lokaci please zaku iya wucewa kuje kasa ku cigaba da magana inji cewar some“maryama bari na dauko jakata mu tafi tare kawai zaman me zanyi ?no yusura karki damu kiyi zamanki bazan zama sanadin rugujewa farincikinki ba ,ina miki fatan alkhairi all the best to both of you tana gama fadar haka ta juya ta soma taku ,da kyar take iya d’aga wafafuwanta saboda nauyin da suka mata ,wani matashin mutun ta gani tsaye bata bi ta kansa ba ta raba ta gefensa ta wuce shi tana sauke nikaf din fuskarta shi kam kamewa yayi ya kasa kwakkwaran motsi shin mafarki yake ko kuwa zahiri yake gani ?.”

ya kai second goma yana kallon bayanta har ta kusan ‘bacewa ganinsa sannan ya juyo ya dubi some “ kinga wata doguwar yarinyar ta wuce yanzu ? “ yes sir ! da sauri yace “ mutun ce ko fataluwa ce ?mutunce sir sunanta maryam hussein “.maryam hussein !? ya furta a dan razane adaidai lokacin da yusura ta fito ta tabi bayan maryama da sauri tana kiran sunanta hankalin salim a matukar tashe yace “Adam ya ganta kuwa ?No sir aiki tazo nema har an dauketa yace akoreta” da sauri yace “kai bari naje na sake tabbatarwa itace ko kuwa dai kama ce ya bi bayanta da sauri ya sauka har kasan kamfanin yana nemanta bai ganta ba tsaki yaja yana cewa “ amman Adam ya cika hauka me yasa bai tsaya yaga yarinyar nan ba yana tsaye sai gasu ita da yusura maryama tana magana muryata da alamun tayi kuka sosai “karki damu yusura ki tsaya Kiyi aikinki karki yi Kuskure irin wanda nayi ,kin dai ga yadda abun alkhairi ya zame min ko? to ki tsaya kiyi aikinki ina miki fatan alkhairi “ta fad’a tana tsaida yusura tare da rike hannunta cikin nata .”Ahankali salim ya kara taku ya matso kusa dasu “shikenan maryama naji kuma na gode da shawarki allah yasa haka shine mafi alkhairi arayuwarki sai mun hadu a gida dan allah karki saka damuwa aranki komai yana da lokaci kuma in sha allahu zai zama alkhairi .”

numfashi ta sauke sannnan ta saki hannun yusura dake cikin nata ta juya itama ta juya ta soma tafiya da sauri kawai taga mutun agabanta yana sauke numfashi bai tsaya wata wata ba kawai ya daga nikaf din fuskata tare tsura mata ido byn Kmr second biyu ya saki wani irin murmushi wanda bashi da maraba dana farinciki muryarsa cike da in.. ina.. ya soma mgn”itace wallahi tabbas itace wallahi itace wacce danuwana ya dade yana nema yayi maganar yana riko tsintsiyar hannunta “dan Allah kiyi hakuri mu koma ciki akwai wanda zan nuna wa ke .”bai gama rufe bakinsa ba ta fixge hannunta tare da daukeshi da wani gigitaccen mari tana cewa “itace wa ?”
“Akan wani dalili zaka kai hannunka jikina ?”ammm but da kin ..”“kar kace min komai bana bukatar jin komai dan baka zo da siffar da zan saurareka ba daga ganin mutun sai ka wani kai hannunka jikinsa kasani koni matar aurece ta fad’a a fusace tana sake juyawa ya sake shan gabanta”wallahi babu inda zaki sai na kai ki gurin ..”“wallahi ka sake kuskure tabani sai na maka wulakanci da har ka matu bazaka manta dani ba ,matsa ka bani hanya na qara gaba da rayuwata “.

“to to ki bani numberki ko address dinki “i cant! ta fad’a tana bin gefensa zata wuce shi sam sam marin da tai masa bai damesa ba kamar tafiyar da zatai Adam bai ganta ba da sauri ya sake shan gabanta “kinsan allah bazaki bar nan ba batare da danuwana ya ganki ba wuce mu koma sama maryama ta dafe goshinta cikin tsananin tashin hankali “wannan shine karo na biyu da ta fuskanci irin wannan matsalar “ kafin ta ankare taji ya rike tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita cikin sauri sauri gudu gudu ya dinga tafiya, tana ya sakar mata hannu amman yaki da kyar da bala’i ya shigar daita lifter ya fad’a office din ATA daita a tsaye ya gansa rike da kugu ya juyawa kofa baya yayinda cup din coffee ke rike a hannunsa yana kurban coffe a hankali bai juyowa ba har sai da yaji salim ya soma mgn “ATA…”ya kira sunansa cikin wata irin muryar mai cike da tashin hankali ATA ya juyo a natse yana fuskatarshi alokacin da salim ya cire nikaf din fuskarta maryama yana rike a hannunsa wani irin bugu qirjinsa da zuciyarsa yayi alokaci daya bai san sanda cup din hannunsa ya subuce kasa ba. take ya tarwatse zuciyarsa ta tsaya cak ta daina aiki na wuncin gadi ,duk yadda ATA ya kai ga son motsa sassan jikinsa bun ya faskara,tamkar wanda bai da numfashi a ganganr jikinsa haka ya dawo saka makon wani yanayi mai sarkakiya da wuyar faasarawa ya ziyarci zuciya dama gangar jikin ATA abangaren maryama ma wani irin mummunar bugu zuciyarta keyi da mugu mugu sauri “la haula wala kuwata illa billa” babu tsumi babu dabara sai na Allah haka ATA yake ta faman ambata acikin zuciyarsa dake karkarwa yayinda maryama wacce bata san dalilin dayasa mutumin dake tsaye a gefenta ya shigo daita ba sai dai ganin fuskar mutumin dake tsaye a gabanta yasa ta nemi natsuwarta ta rasa .”

hakan nan damuwar dake cunkushe cikin ranta ta ninku yayinda soyayya da kaunarta ya dinga bin dukkan sassa na jikinshi ji yake kamar acikin mafarikinsa ya Allah kasa a zahiri nake ganin komai ba mafarkin dana sabayi daita bane ,wani irin so mai zafi ya dinga huda zuciyarsa yana bin jinin jikinsa wanda ma'abota so da shauki kadai ne suka san zakinta,yana son yarinyar kamar ranshi shikanshi yana mamakin zazzafar soyayyr da yake mata mai tafiya da dukkan wani motsi na bugun numfashinsa “adam kayi maza ka dawo haiyacinka karka biyewa soyayya dake kutimemeniya da rayuwarka gizo ce ba zahiri ba “to Salim dake tare daita fa ?shima gizo ne ko me “? tsaki taja tana duban fuskar salim a wulakance cike da tarin bakinciki mara misaltuwa muryarta cike da sheshekar kuka tace “Allah ya isa tsakanina da kai bazan ta’ba yafe maka ba “.sautin muryarta ce ta dawo da mr ATA cikin haiyacinsa tun bai kai ga bawa kanshi amsa ba ya ware idanusnhi sosai ya zuba mata kwayar idanunshi yana kallonta tamkar zai cinyeta “.

Alhamdulillah
Anan zan dakata sai mun had’u a littafi na uku wanda zai zama na qarshe ina maku fatan alkhairi

Mmn suka
Chapter 102 · 0% Book details