Sashe 29
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Babu ruwanki da kallonsa kiyi abinda ya kaiki maza tashi ki tafi dan ki samu ki dawo da wuri “numfashi ta sauke” gsky aunty bazanje yanzu ba “ya fad’a tana wasa da yatsun hannunta “sai yaushe zaki?maryama tayi shiru ta kasa mgn “da dai kin daure tunda kinga baki da lokaci sai asabar da ladidi tsaki maryama taja kana tace “wallahi ban san dalili ba hakan nan najin fad’uwar gaba kuma dai yau bana son zuwa koina “aunty ta numfasa tace “to shikenan Kiyi zamanki muje kiyi wanka ki karya ki sha maganin ciwon kai ta mike ta fito wanka tayi ta shirya ta karya aunty ta bata magani ta sha tayi kwanciyarta akan kujera .”
Ahankali ta rufe idanunta lokaci d’aya kwakwalu warta ta bud’e tunani ya kusantota yaki barinta ta huta duk da bata son tayi tunani akan matsalarta amman haka tunani ya mamayeta , ahankali ta dinga tunanin maganganun yusif ,me yasa zaki damu kanki maryama already kin rigada kin yarda kin rasa yusif har abada kamata yayi kin haka rami ki binne komai ya zama tahiri arayuwarki” zanyi haka zan cire komai araina kuma zan dage da addua har na samu nasara arayuwata ahankali tabi shawarar zuciyarta ta haka rami mai zurfi aciki zuciyarta ta binne duk wata matsalarta .”
tun daga wannan ranar maryama ta cire tunani da damuwar komai acikin ranta ta toshe kunnenta duk abinda ke faruwa aciki gidan tana ji kuma tana gani amman ta share sannna taki bari mahaifiyarta tasan halin da’ake ciki yayinda kullum sai aunty ta sheida mata sakon kiran aunty fati har sanda sati ta cika aunty ta matsa mata lallai taje taji dalilin kiran da take mata “Allah aunty bana son zuwa duk sanda kika fad’a min sakonta gabana faduwa yake “kiyi hakuri ki daure kije bana son tazo gidan nan “ta fad’a muryarta a raunane ganin yanayin aunty yasa ta riko hannunta “shikenan aunty zani bari na sauya kaya naje yanzu na dawo .”
“Yauwa princess maza tashi kije Allah ya tsare min Ke “Ameen !ta furta a tsanake ta fito ahankali take taku har fito titin unguwarsu ta mike zuwa captor road tana gama garasawa bakin titi ta samu adaidai mai zuwa unguwarsu aunty fati tafiya kad'an suka yi ta sauka pencilima ta mikawa mai adaidaita kudi ta ta tsallako hannunta na hagu inda zai shigar daita amawo ."a natse ta shiga gidan kai tsaye bangaren aunty fati ta nufa bakinta dauke da sallama ta shiga parlour'n inda ta iske muktar da aunty fati zaune ."
Rike da remut tana qoqarin canza tasha a tare suka kallo kofar tare da amsa sallama .”
tun daga kasa muktar ya dauki kallon maryama ransa nayi masa dadi wani irin yanayi ya tsinci kanshi ciki mai wuyar misaltuwa yana jin yadda soyayyarta ke fixgarsa yayinda maryama ta had'e fuska sosai tmkr taga wani mugun abu ta qarasa ta tsugunna har kasa ta gaishe da aunty fati ,aunty fati ta amsa mata fuskarta a d'an sake wanda hakan ya dan bawa maryama mamaki domin tunda suke daita kyara da hantara tattare da zagi né a tsakaninsu ."
Maryama ta dauke kanta tare da mikewa tsaye ta zauna tana jiran taji dalilin nemanta da aunty fati take "ke maryama baki ga muktar bane da bazaki iya bud'e ki gaishesa ba ko shi kike jira ya gaisheki ?
"murmushi ya saki yana cewa"Kinsan ‘yan boko ba dai girman kai ba " wani kallon takaici maryama tayi masa daga sama har kasa wanda yasa ma kasa cigaba da magana illa ya zuba mata kwala kwalan idanusnhi masu firgitarwa ."sama da awa daya tana zaune tana wasa da yatsun hannunta sannan aunty fati ta gyara zama ta kira sunanta .”
"maryama !
muryarta a raunane ta amsa da “na’am !"na kiraki né domin na samu labari wannan yaron yusif ya canzaki da shukura yanzu ita zai aura shine muktar yace abashi ke tunda kowa gudnki yake kinga kenan shi zai taimaka ya aureki sai yanzu na na gane dashi kika dace ba da sauran mazan da suke zuwa neman aurenki suna guduwa , d'ago idanunta tayi ta zubawa aunty fati tana kallonta gabanta na dukan tara tara sannan ta waiga ta kalli inda muktar din yake yana kallonta kamar tsohon maye ."
"Karki dauka ya rasa wacce zai aura ne yasa zai aureki aa tausayi kika bashi domin yaji babu dadi aransa , yanzu me kika gani zaki auresa ko kuwa zaki tsaya jiran masu kudin da basamu zakiyi ba ?ta tambayeta tana gyara zamanta tare da tsareta da idanunta "parlour'n ya dauki shiru na kusan mintuna goma batare da maryama tace uhm ba bare uhmm illa nazari maganar aunty fati da take da kuma tunani amsar da zata bata domin dai a halin yanzu wannan shine labari mafi muni daya kusanto rayuwarta muktar fa ? "ke nake sauraro !?"
Murayarta can kasa ta soma magana a tsanake "a zahirin gasky ni ina da wanda nake só kuma wanda a shirye yake da aurena idan da hali zaa iya bashi kaulat ko Islam ,ko kuma sakina amman ni dai gsky ayi min hakuri akwai wanda muka tsaida magana dashi ."ta tsinci kanta da fad’ar haka ba dan akwai din ba sai dan tsiratar da rayuwata daga shiga maseefa”waye shi kuma a ina yake ?"maryama tayi shiru ta kasa magana hankalinta idan yayi dubu tô a tashe yake tayi datasani zuwa gidan amman tasan ko bata zo wannna maseefar sai ta biyota har gida "
“ke banson iskanci banza bayan nasan babu kowa a kasa shine zaki ce kina da wanda zaki aura tô ke nake son ya aura ,oh a zuwan kinfi karfin aurensa shine kika lissafo min daidai shi ko ?"ko d'aya aunty a dai bashi cikinsu shine zai samar da kwanciyar hankali "bata son wata fitina ta kuma lura kamar fitinar ce take bibiyarta arayuwarta, ran a aunty fati a matukar bace tace "d'an ma Kinsamu zai taimaka miki maza tashi ki bani waje na sallameki sannan ki fara shirin aurensa dan dolenki ki auresa"
Jiki a sanyaye maryama ta mike hankalinta a matukar tashe bazata ki dan shaye shaye ba dan mahaifinta ma har ya bar duniya yana sha babu komai acikin rayuwarsu sai matsala ita me kai ta saka rayuwarta cikin ha'ula'i ?kuma tasan idan ba tsanarta da aunty fati tayi ba babu yadda zaa yi tace ta auri d’anta domin ko ita take da diya kamarta tayi imani bazata dauketa ta bawa muktar aure ba mutumin da idan yayi shaye shayensa har kwata yake fadawa haka maryama ta koma gida tana cika tana batsewa duk ranta a dagule ."
Aunty ce ta fito daga kitchen tace "lafiya kuwa naga har kin dawo yanzu ?hawaye maryama ta share tace" aunty laifin me nayi da allah ya qaddaroni cikin wannan dangin ?basa sona basa qaunar cigabanna idan akwai wacce suka tsana a duniya tô nice suna jin kamr su kasheni wallahi suzo su kasheni su huta da muguwar tsanar da suka min na rasa me nayi masu arayuwar nan da suka tsane ni."aunty ta zauna kusa daita jikinta na rawa tace "me ya faru maryama ?"na gaji da wannan rayuwar aunty fati so take ta kasheni dan Allah ku barta ta kasheni ni yanzu nafi bukatar mutuwa da rayuwata akan dai ta hadani da muktar .”ta qarasa maganar tana kuka .”
“kwantar da hankalinki kiyi min bayani da kyau ban fahimceki ba ta hadaki da muktar kamar ya ?"
"Wai ya aureni !"numafashi aunty ta sauke cikin rarrashi tace "haba maryama ki daina daga hankalinki tunda ga maganar yusif nasan baba gali zai yi mata bayanin komai maryama ta fashe da wani sabon kuka dan ta ta’bo mata wani ciwo ne data binne "babu wannna auren bilkisu .”muryar umma suka jiyo daga bakin kofa aunty ta juya da sauri qirjinta na bugawa fiyye da kaida ummah ta gyada mata kai "haka né abinda kikaji na fada shima an canza masa tunani har ma dana iyayensa ahankali ta tako ta dafa kafandan aunty dake kallonta a tsorace cikin tsananin tashin hankali ."
“Ummah ban gane ba me kike qoqarin fad’a min ?“abinda kika ji shi na fad’a miki balkisu yusif ya koma wajen shukura “inna lillahi wa inna ilahi rajiun shi kawai tayita fad’a tana maimatawa nan da nan yanayinta ya sauya ta zauna shiru taji duk wani kuzari na jikinta yayi kasa tsawon mintuna talatin sannan ta bud’e bakinta da kyar tace “shima yusif din ya koma wajensu "Ki kwantar da hankalinki babu abinda allah bazai iya ba kuma in sha allahu allah zai kai maryama matakin da ba'a só allah yasa hakan shine mafi zama alkhairi arayuwarta ummah ta zauna ta dinga tausar aunty da maryama tana bata baki har aunty ta saki ranta sai dai hawaye yaki tsayawa umma ta qara da tabbatar masu duk runtse maryama bazata auri muktar ba “
Maryama ta rungume ummah ajiknta “na gode umma dan allah karki bari a aura min shi wallahi na hakura da auren ma har abada “bazaki hakura da aure ba akan wani dalili domin duk dan sunah baya gudun aure yadda akayi aure aka haifeki in sha allahu kema zakiyi aure har ma da ya’ya da jikoki ummah ta fad’a tana shafa bayanta suna cikin wannan hali habib ya shigo aunty tayi sauri ta goge hawayenta tana daidaita natsuwarta ganinsu haka ya fahimci akwai damuwa dan haka da hanzari ya qaraso ya riko hannun aunty cikin nashi yana tmbyarta “lafiya na ganku haka ?babu komai aunty ta basu amsa “ya babu komai ?ya kalli ummah fuskasa dauke da tambaya .”
“Me yasa zaku boye masa yana da kyau ya sani ko babu komai zai taya yaruwarsa addua nan ummah ta fad’a masa komai “shiyasa nace ta hakura da batun wani aure ,bafa dole sai mutun yayi aure zai shiga aljanna ba “kul kar na sake jin ka fad’a haka zatayi aure musa aranmu dukkaninsu babu mijin aurenta acikinsu mu godewa allah da yasa har tana masu sonta baa barta haka ba babu abinda zai zo da bazai wuce ba wata sai labari ahankali ummah ta shawo kansu suka shiga wata hirar ,”
******
Ahankali ta rufe idanunta lokaci d’aya kwakwalu warta ta bud’e tunani ya kusantota yaki barinta ta huta duk da bata son tayi tunani akan matsalarta amman haka tunani ya mamayeta , ahankali ta dinga tunanin maganganun yusif ,me yasa zaki damu kanki maryama already kin rigada kin yarda kin rasa yusif har abada kamata yayi kin haka rami ki binne komai ya zama tahiri arayuwarki” zanyi haka zan cire komai araina kuma zan dage da addua har na samu nasara arayuwata ahankali tabi shawarar zuciyarta ta haka rami mai zurfi aciki zuciyarta ta binne duk wata matsalarta .”
tun daga wannan ranar maryama ta cire tunani da damuwar komai acikin ranta ta toshe kunnenta duk abinda ke faruwa aciki gidan tana ji kuma tana gani amman ta share sannna taki bari mahaifiyarta tasan halin da’ake ciki yayinda kullum sai aunty ta sheida mata sakon kiran aunty fati har sanda sati ta cika aunty ta matsa mata lallai taje taji dalilin kiran da take mata “Allah aunty bana son zuwa duk sanda kika fad’a min sakonta gabana faduwa yake “kiyi hakuri ki daure kije bana son tazo gidan nan “ta fad’a muryarta a raunane ganin yanayin aunty yasa ta riko hannunta “shikenan aunty zani bari na sauya kaya naje yanzu na dawo .”
“Yauwa princess maza tashi kije Allah ya tsare min Ke “Ameen !ta furta a tsanake ta fito ahankali take taku har fito titin unguwarsu ta mike zuwa captor road tana gama garasawa bakin titi ta samu adaidai mai zuwa unguwarsu aunty fati tafiya kad'an suka yi ta sauka pencilima ta mikawa mai adaidaita kudi ta ta tsallako hannunta na hagu inda zai shigar daita amawo ."a natse ta shiga gidan kai tsaye bangaren aunty fati ta nufa bakinta dauke da sallama ta shiga parlour'n inda ta iske muktar da aunty fati zaune ."
Rike da remut tana qoqarin canza tasha a tare suka kallo kofar tare da amsa sallama .”
tun daga kasa muktar ya dauki kallon maryama ransa nayi masa dadi wani irin yanayi ya tsinci kanshi ciki mai wuyar misaltuwa yana jin yadda soyayyarta ke fixgarsa yayinda maryama ta had'e fuska sosai tmkr taga wani mugun abu ta qarasa ta tsugunna har kasa ta gaishe da aunty fati ,aunty fati ta amsa mata fuskarta a d'an sake wanda hakan ya dan bawa maryama mamaki domin tunda suke daita kyara da hantara tattare da zagi né a tsakaninsu ."
Maryama ta dauke kanta tare da mikewa tsaye ta zauna tana jiran taji dalilin nemanta da aunty fati take "ke maryama baki ga muktar bane da bazaki iya bud'e ki gaishesa ba ko shi kike jira ya gaisheki ?
"murmushi ya saki yana cewa"Kinsan ‘yan boko ba dai girman kai ba " wani kallon takaici maryama tayi masa daga sama har kasa wanda yasa ma kasa cigaba da magana illa ya zuba mata kwala kwalan idanusnhi masu firgitarwa ."sama da awa daya tana zaune tana wasa da yatsun hannunta sannan aunty fati ta gyara zama ta kira sunanta .”
"maryama !
muryarta a raunane ta amsa da “na’am !"na kiraki né domin na samu labari wannan yaron yusif ya canzaki da shukura yanzu ita zai aura shine muktar yace abashi ke tunda kowa gudnki yake kinga kenan shi zai taimaka ya aureki sai yanzu na na gane dashi kika dace ba da sauran mazan da suke zuwa neman aurenki suna guduwa , d'ago idanunta tayi ta zubawa aunty fati tana kallonta gabanta na dukan tara tara sannan ta waiga ta kalli inda muktar din yake yana kallonta kamar tsohon maye ."
"Karki dauka ya rasa wacce zai aura ne yasa zai aureki aa tausayi kika bashi domin yaji babu dadi aransa , yanzu me kika gani zaki auresa ko kuwa zaki tsaya jiran masu kudin da basamu zakiyi ba ?ta tambayeta tana gyara zamanta tare da tsareta da idanunta "parlour'n ya dauki shiru na kusan mintuna goma batare da maryama tace uhm ba bare uhmm illa nazari maganar aunty fati da take da kuma tunani amsar da zata bata domin dai a halin yanzu wannan shine labari mafi muni daya kusanto rayuwarta muktar fa ? "ke nake sauraro !?"
Murayarta can kasa ta soma magana a tsanake "a zahirin gasky ni ina da wanda nake só kuma wanda a shirye yake da aurena idan da hali zaa iya bashi kaulat ko Islam ,ko kuma sakina amman ni dai gsky ayi min hakuri akwai wanda muka tsaida magana dashi ."ta tsinci kanta da fad’ar haka ba dan akwai din ba sai dan tsiratar da rayuwata daga shiga maseefa”waye shi kuma a ina yake ?"maryama tayi shiru ta kasa magana hankalinta idan yayi dubu tô a tashe yake tayi datasani zuwa gidan amman tasan ko bata zo wannna maseefar sai ta biyota har gida "
“ke banson iskanci banza bayan nasan babu kowa a kasa shine zaki ce kina da wanda zaki aura tô ke nake son ya aura ,oh a zuwan kinfi karfin aurensa shine kika lissafo min daidai shi ko ?"ko d'aya aunty a dai bashi cikinsu shine zai samar da kwanciyar hankali "bata son wata fitina ta kuma lura kamar fitinar ce take bibiyarta arayuwarta, ran a aunty fati a matukar bace tace "d'an ma Kinsamu zai taimaka miki maza tashi ki bani waje na sallameki sannan ki fara shirin aurensa dan dolenki ki auresa"
Jiki a sanyaye maryama ta mike hankalinta a matukar tashe bazata ki dan shaye shaye ba dan mahaifinta ma har ya bar duniya yana sha babu komai acikin rayuwarsu sai matsala ita me kai ta saka rayuwarta cikin ha'ula'i ?kuma tasan idan ba tsanarta da aunty fati tayi ba babu yadda zaa yi tace ta auri d’anta domin ko ita take da diya kamarta tayi imani bazata dauketa ta bawa muktar aure ba mutumin da idan yayi shaye shayensa har kwata yake fadawa haka maryama ta koma gida tana cika tana batsewa duk ranta a dagule ."
Aunty ce ta fito daga kitchen tace "lafiya kuwa naga har kin dawo yanzu ?hawaye maryama ta share tace" aunty laifin me nayi da allah ya qaddaroni cikin wannan dangin ?basa sona basa qaunar cigabanna idan akwai wacce suka tsana a duniya tô nice suna jin kamr su kasheni wallahi suzo su kasheni su huta da muguwar tsanar da suka min na rasa me nayi masu arayuwar nan da suka tsane ni."aunty ta zauna kusa daita jikinta na rawa tace "me ya faru maryama ?"na gaji da wannan rayuwar aunty fati so take ta kasheni dan Allah ku barta ta kasheni ni yanzu nafi bukatar mutuwa da rayuwata akan dai ta hadani da muktar .”ta qarasa maganar tana kuka .”
“kwantar da hankalinki kiyi min bayani da kyau ban fahimceki ba ta hadaki da muktar kamar ya ?"
"Wai ya aureni !"numafashi aunty ta sauke cikin rarrashi tace "haba maryama ki daina daga hankalinki tunda ga maganar yusif nasan baba gali zai yi mata bayanin komai maryama ta fashe da wani sabon kuka dan ta ta’bo mata wani ciwo ne data binne "babu wannna auren bilkisu .”muryar umma suka jiyo daga bakin kofa aunty ta juya da sauri qirjinta na bugawa fiyye da kaida ummah ta gyada mata kai "haka né abinda kikaji na fada shima an canza masa tunani har ma dana iyayensa ahankali ta tako ta dafa kafandan aunty dake kallonta a tsorace cikin tsananin tashin hankali ."
“Ummah ban gane ba me kike qoqarin fad’a min ?“abinda kika ji shi na fad’a miki balkisu yusif ya koma wajen shukura “inna lillahi wa inna ilahi rajiun shi kawai tayita fad’a tana maimatawa nan da nan yanayinta ya sauya ta zauna shiru taji duk wani kuzari na jikinta yayi kasa tsawon mintuna talatin sannan ta bud’e bakinta da kyar tace “shima yusif din ya koma wajensu "Ki kwantar da hankalinki babu abinda allah bazai iya ba kuma in sha allahu allah zai kai maryama matakin da ba'a só allah yasa hakan shine mafi zama alkhairi arayuwarta ummah ta zauna ta dinga tausar aunty da maryama tana bata baki har aunty ta saki ranta sai dai hawaye yaki tsayawa umma ta qara da tabbatar masu duk runtse maryama bazata auri muktar ba “
Maryama ta rungume ummah ajiknta “na gode umma dan allah karki bari a aura min shi wallahi na hakura da auren ma har abada “bazaki hakura da aure ba akan wani dalili domin duk dan sunah baya gudun aure yadda akayi aure aka haifeki in sha allahu kema zakiyi aure har ma da ya’ya da jikoki ummah ta fad’a tana shafa bayanta suna cikin wannan hali habib ya shigo aunty tayi sauri ta goge hawayenta tana daidaita natsuwarta ganinsu haka ya fahimci akwai damuwa dan haka da hanzari ya qaraso ya riko hannun aunty cikin nashi yana tmbyarta “lafiya na ganku haka ?babu komai aunty ta basu amsa “ya babu komai ?ya kalli ummah fuskasa dauke da tambaya .”
“Me yasa zaku boye masa yana da kyau ya sani ko babu komai zai taya yaruwarsa addua nan ummah ta fad’a masa komai “shiyasa nace ta hakura da batun wani aure ,bafa dole sai mutun yayi aure zai shiga aljanna ba “kul kar na sake jin ka fad’a haka zatayi aure musa aranmu dukkaninsu babu mijin aurenta acikinsu mu godewa allah da yasa har tana masu sonta baa barta haka ba babu abinda zai zo da bazai wuce ba wata sai labari ahankali ummah ta shawo kansu suka shiga wata hirar ,”
******