Sashe 85
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
baba qarami ya kalli ata yana jin haushi irin haushin da mutun zai iya kashe mutun "na dauka ko wani ka ga yayiwa hindu haka sai inda karfinka ya qare kuma zaka taimaki rayuwarta amman wulakanci ka bar min 'ya a tsare har tsawon watani sannan aka wuce daita gidan yari bancin na tashi tsaye da haka rayuwarta zata qare . tsakanina da kai adamu allah Ya isa ban yafe maka ba duniya da lahira "kayi hakuri baba qarami duk abun bai kai haka ba zai sa a sakota in sha allahu "wani irin kallo ata yayiwa mami ta juyo ta kallesa a tsanake tace "me yasa kayi haka adamcy ?dokarki nabi kikace a dauki mataki akan duk wanda yayi yunkurin kashe miki maryam ko ba haka ba ?mami tayi shiru tana dubansa sam bashi da tsoro akan komai "naji amman kasa a sakota bana jin ma itace zata aikata haka "kiyi hakuri sweetheart babu ta yadda zaayi na saka baki saboda abinda ta aikata mummunar laifi ne kuma ta amsa da bakinta ta aikata "a gidan ubanka ta amsa haka ?"
"mugun kawai mai mugun hali ni nasan hindu bazata aikata hakan ba sai dai idan azabtar daita akayi yasa ta amsa laifin da ba nata ba gefen bakinsa ya ciza da karfi "nifa duk abinda zaa fad'a akaina ba damuwata bace idan kuna da hujjar da zata wanke kanta tayi ,ku kuma ku sake shigar da qara kotu amman ni Adam bazan saka baki a fito da tantiriya yar tasha irinta ba." tayi laifi kuma ta amsa laifinta dole hukuma ta hukuntata ni na gama magana sweetheart ko zan iya tashi ?"daga baba qarami har mami suka zuba masa ido suna kallonsa ranshi fess ya mike yayiwa mami sallama ya wuce yana fita ya iske masu tsaronsa a inda suka saba tsayawa suna ganinsa suka qaraso da sauri cike da girmamawa suna gaishesa atakaice ya dinga amsa masu batare da bata lokaci ba aka bude masa bayan mota ya shiga suka bar gidan a can parlour'n mami kuwa hakuri kawai take bawa baba qarami tana tabbatar masa lallai hindu zata fito ya bar komai a hannunta da kyar ta samu ya wuce sai dai kallo daya zaka masa kasan ransa a bace yake kuma zai iya aikata komai akan adam ."
*****
Bangaren maryama kuwa har karfe goma na dare babu su babu labarinsu, aunty da umma da habib da sauran yanuwan ummah wadan da suka zo biki da dangin mahaifinsu da basu wuce gida ba duk suka damu sukai ta neman layinsu amman shiru ga dai wayoyinsu yana ringin amman ba d'agawa nan fa hankalinsu ya tashi matuka zuciyarsu ta fará tsinkewa gabad'aya suka taru acikin parlour'n umma cikin jimami da tashin hankali ."Allah sarki umma duk yadda take jin mummunar faduwar gaba da tsinkewar zuciya amman sai ta dake ta kasa nunawa kowa damuwarta da yanayin da take ji sai ma ta dinga kwantar masu da hankali tana cewa "babu komai wata killa yanayin aikin ne ko kuma ababen hawa né sukai yawa a hanya "haka suka kwana zaune cikin tashin hankali da zullumi ."
washegari kuwa tun da asuba fari habib da a bokinsa faisal suka d'auki hanyar ogun state kasamcewar duk inda maryama zata aiki tana tura masa address gabad'aya habib baya cikin natsuwarsa ji yake kamar zuciyarsa zata buga hakan ne ma yasa sam baya ganin gudun da motar tasu take akan titi har ma yaji kamar su fita su canza wata motar kamar bazasu kai ba sai gashi sun karaso jikinsa na tsuma kamar wanda ake zubawa ruwan zafi suka dauki hanyar ma'aikatan isarsu ke da wuya aka sheida masu sunzo amamn tun a yammacin jiya suka wuce
cikin tsananin tashin hankali habib ya shiga kiran number aunty kira d'aya ta dauka tana kiran sunansa nan dai habib ya sheida mata komai
tunda aunty ta kira sunan habib idanun ummah ke kanta tana jiran ta gama wayar taji mai zata fad'a ganin yadda ta fashe da kuka tana salati yasa ummah ta dawo kusa daita jikinta na wani irin rawa "balkisu meke faruwa mutuwa sukai ko me ?
"Cikin muryar kuka aunty tace "ummah wai tun da yammacin jiya suka baro kamfanin salati ta saka tana addua tare da karfafa zuciyarta data aunty "karki damu balkisu babu abinda zai samesu koma menene in sha allahu Allah zai kawo masu mafuta ta fad'a tana share hawaye "gsky ummah ina ji ajikina akwai wani abu dake faruwa dasu." numfashi ummah ta sauke cikin karfafa ma aunty zuciya "haba bilkisu ki daina wannan tunani kisa aranki babu abinda zai samesu "Allah yasa amman tun jiya da yammaci suka baro kamfani amman har zuwa wannan lokacin babu su babu alamunsu "ke dai kiyi masu addua kawai ta fad'a cike da tausayawa kanta dan ita kanta tana ji ajikinta akwai wani abu dake faruwa dasu sai dai tana fatan ya zama alkhairi arayuwarsu gabad'aya."ta mike ta shiga dakinta ta zauna cikin tsananin tashin hankali hawaye ne ya dinga zuba daga idanunta ahankali idanunta ya sauka akan frem din hoton sadam dake ajiye akan qaramar durowarta yana sanye da kananan kaya ya daura rigar sanyi akan kayan idanunshi manne da bakin glass ,tayi shiru kawai tana kallonsa kallonsa take saboda shi kadai ne ya rage mata a duniya bata da uwa bata da uba bata da miji yanzu idan wani abu ya samesa dole zata shiga damuwa ta qarasa zancen zuci tana fashewa da kuka mai ban tausayi "in sha allahu bazan rasaku ba sadam da maryama ina maku fatan alkhairi a duk inda kuke Allah ya dawo mun daku cikin koshin lafiya ."
suna nan zaune cikin tsananin jimami da tashin hankali har yamma sai ga habib da abokinsa ajigace suka karaso gida sakamakon yanayin damuwar da suke ciki cikin tashin hankali aka kira baba gali da sauran yan'uwan dangin mahaifinsu cikin kankani lokacin suka hallara dan daman suna bangaren aunty hassana .bayan sun gama jin komai suka fara zuba ruwan maseefa hajiya fatima tace "ai duk abinda ya faru laifin umman sadam ne dan itace ta basu gudunmuwa tafiya , inda take shiga batan take fita ba nan da nan sauran yan'uwa suka kama ita dai ummah shiru tayi kawai tana karanto duk adduar datazo bakinta ita yanzu batasu take ba yadda ya'yanta zasu dawo gareta take ."yadda suka wuni jiya cikin tashin hankali haka suka wuni yau din ma dan har karfe 12:00 na dare ba labarinsu ummah tace kowa yaje ya kwanta aga zuwa gobe ."washgari baba gali da habib da sauran yanuwa maza suka bazama nemansu har ogun state din aka sake komawa sai dai babu wani labari duk hankulansu a tashe yake aunty kuka kawai take ummah kam tayi dauriya habib ma kuka yake yana kiran sunan maryama da yaya sadam abun gwanin ban tausayi ."
bangaren aunty salma kam abun yayi mata dadi fiyye da tunanin mai karatu ,dan adduar mutuwa ma ta dinga masu ,allah yasa mummunar hatsari suka samu a hanya "burinta daman maryama ta bar duniya ko kuma tayi rayuwar kaskanci ko zama babu aure. sai gashi burinta ya cika batare da ta 'bata kudinta ba ,tana zaune baba gali ya shigo ya tsaya akanta "salma ina fatan dai babu hannunki cikin rasa sadam da maryama ?wani irin kallo ta watsa masa "idan da hannuna me zai faru ?Aa to gsky ni dai babu ruwana kuma muddin da hannunki Kiyi maza kisa a dawo dasu "gsky a wasu lokutan sai naga kamar kana bin bayana amman kuma wani lokacin sai naga kana nuna min wariyar launi ,kai yanzu meye damuwarka dan an nemesu an rasa kai daya kamata kaji dadi kayi farinciki an nemesu an rasa maryama bazata yi rayuwar jin dadi a gidan ba zata bar ya'yanmu suyi rayuwarsu cikin jin dadi ko da yake shi kanshi yusif din yanzu mun rasa gane kanshi ko shekaranjiya da suka zo daurin aure da abbansa bai leko inda muke ba da alamun aikin daakayi masa ya fara barin jikinsa sai an sabanta wani sabo ".
"ni yanzu ba wannan bane damuwata ki fad'a min gsky da hannunki a rashin dawowar su gida ko babu hannunki ciki ?"ta sosa idanunta da hannunwanta duka tace "babu hanuna !"to amman ai shekarajiya naji kina waya da malaminki kina cewa ayi duk yadda zaayi a salwantar da .."kaga dakata daka ji ina magana cewa nayi a salwantar dasu duka ko maryama ?to ai ni ko maryama ma bana son ta rasa rayuwarta bare kuma sadam "tsaki taja tana turo masa baki "ai daidai ne ma idan sadam ya mutu idan bakasani ba bari na fahimtar da kai, idan sadam ya mutu kai ne zakaji dadin rayuwarka dan duk wani abu daya mallaka zai zama naka halak malak kai da sauran yanuwanka hassalima naka ne zai fi na kowa yawa tunda bashi da magaji ,mahaifiyarsa ce kawai ita kadai ranta kuma bazata gajesa ba "kinji zaki sake lalata komai ni dai bana son ran kowa ya salwanta a hannuna ".yana gama fad'ar hk ya fice tabi shi da kallon kaskanci tana ta'be baki "ina ganin shima wannan sokon sai nasa an gama min dashi gabad'aya na huta tai murmushi "wallahi ina farinciki da rashin dawowarsu allah yasa ko gawar su kar agani ."
"mugun kawai mai mugun hali ni nasan hindu bazata aikata hakan ba sai dai idan azabtar daita akayi yasa ta amsa laifin da ba nata ba gefen bakinsa ya ciza da karfi "nifa duk abinda zaa fad'a akaina ba damuwata bace idan kuna da hujjar da zata wanke kanta tayi ,ku kuma ku sake shigar da qara kotu amman ni Adam bazan saka baki a fito da tantiriya yar tasha irinta ba." tayi laifi kuma ta amsa laifinta dole hukuma ta hukuntata ni na gama magana sweetheart ko zan iya tashi ?"daga baba qarami har mami suka zuba masa ido suna kallonsa ranshi fess ya mike yayiwa mami sallama ya wuce yana fita ya iske masu tsaronsa a inda suka saba tsayawa suna ganinsa suka qaraso da sauri cike da girmamawa suna gaishesa atakaice ya dinga amsa masu batare da bata lokaci ba aka bude masa bayan mota ya shiga suka bar gidan a can parlour'n mami kuwa hakuri kawai take bawa baba qarami tana tabbatar masa lallai hindu zata fito ya bar komai a hannunta da kyar ta samu ya wuce sai dai kallo daya zaka masa kasan ransa a bace yake kuma zai iya aikata komai akan adam ."
*****
Bangaren maryama kuwa har karfe goma na dare babu su babu labarinsu, aunty da umma da habib da sauran yanuwan ummah wadan da suka zo biki da dangin mahaifinsu da basu wuce gida ba duk suka damu sukai ta neman layinsu amman shiru ga dai wayoyinsu yana ringin amman ba d'agawa nan fa hankalinsu ya tashi matuka zuciyarsu ta fará tsinkewa gabad'aya suka taru acikin parlour'n umma cikin jimami da tashin hankali ."Allah sarki umma duk yadda take jin mummunar faduwar gaba da tsinkewar zuciya amman sai ta dake ta kasa nunawa kowa damuwarta da yanayin da take ji sai ma ta dinga kwantar masu da hankali tana cewa "babu komai wata killa yanayin aikin ne ko kuma ababen hawa né sukai yawa a hanya "haka suka kwana zaune cikin tashin hankali da zullumi ."
washegari kuwa tun da asuba fari habib da a bokinsa faisal suka d'auki hanyar ogun state kasamcewar duk inda maryama zata aiki tana tura masa address gabad'aya habib baya cikin natsuwarsa ji yake kamar zuciyarsa zata buga hakan ne ma yasa sam baya ganin gudun da motar tasu take akan titi har ma yaji kamar su fita su canza wata motar kamar bazasu kai ba sai gashi sun karaso jikinsa na tsuma kamar wanda ake zubawa ruwan zafi suka dauki hanyar ma'aikatan isarsu ke da wuya aka sheida masu sunzo amamn tun a yammacin jiya suka wuce
cikin tsananin tashin hankali habib ya shiga kiran number aunty kira d'aya ta dauka tana kiran sunansa nan dai habib ya sheida mata komai
tunda aunty ta kira sunan habib idanun ummah ke kanta tana jiran ta gama wayar taji mai zata fad'a ganin yadda ta fashe da kuka tana salati yasa ummah ta dawo kusa daita jikinta na wani irin rawa "balkisu meke faruwa mutuwa sukai ko me ?
"Cikin muryar kuka aunty tace "ummah wai tun da yammacin jiya suka baro kamfanin salati ta saka tana addua tare da karfafa zuciyarta data aunty "karki damu balkisu babu abinda zai samesu koma menene in sha allahu Allah zai kawo masu mafuta ta fad'a tana share hawaye "gsky ummah ina ji ajikina akwai wani abu dake faruwa dasu." numfashi ummah ta sauke cikin karfafa ma aunty zuciya "haba bilkisu ki daina wannan tunani kisa aranki babu abinda zai samesu "Allah yasa amman tun jiya da yammaci suka baro kamfani amman har zuwa wannan lokacin babu su babu alamunsu "ke dai kiyi masu addua kawai ta fad'a cike da tausayawa kanta dan ita kanta tana ji ajikinta akwai wani abu dake faruwa dasu sai dai tana fatan ya zama alkhairi arayuwarsu gabad'aya."ta mike ta shiga dakinta ta zauna cikin tsananin tashin hankali hawaye ne ya dinga zuba daga idanunta ahankali idanunta ya sauka akan frem din hoton sadam dake ajiye akan qaramar durowarta yana sanye da kananan kaya ya daura rigar sanyi akan kayan idanunshi manne da bakin glass ,tayi shiru kawai tana kallonsa kallonsa take saboda shi kadai ne ya rage mata a duniya bata da uwa bata da uba bata da miji yanzu idan wani abu ya samesa dole zata shiga damuwa ta qarasa zancen zuci tana fashewa da kuka mai ban tausayi "in sha allahu bazan rasaku ba sadam da maryama ina maku fatan alkhairi a duk inda kuke Allah ya dawo mun daku cikin koshin lafiya ."
suna nan zaune cikin tsananin jimami da tashin hankali har yamma sai ga habib da abokinsa ajigace suka karaso gida sakamakon yanayin damuwar da suke ciki cikin tashin hankali aka kira baba gali da sauran yan'uwan dangin mahaifinsu cikin kankani lokacin suka hallara dan daman suna bangaren aunty hassana .bayan sun gama jin komai suka fara zuba ruwan maseefa hajiya fatima tace "ai duk abinda ya faru laifin umman sadam ne dan itace ta basu gudunmuwa tafiya , inda take shiga batan take fita ba nan da nan sauran yan'uwa suka kama ita dai ummah shiru tayi kawai tana karanto duk adduar datazo bakinta ita yanzu batasu take ba yadda ya'yanta zasu dawo gareta take ."yadda suka wuni jiya cikin tashin hankali haka suka wuni yau din ma dan har karfe 12:00 na dare ba labarinsu ummah tace kowa yaje ya kwanta aga zuwa gobe ."washgari baba gali da habib da sauran yanuwa maza suka bazama nemansu har ogun state din aka sake komawa sai dai babu wani labari duk hankulansu a tashe yake aunty kuka kawai take ummah kam tayi dauriya habib ma kuka yake yana kiran sunan maryama da yaya sadam abun gwanin ban tausayi ."
bangaren aunty salma kam abun yayi mata dadi fiyye da tunanin mai karatu ,dan adduar mutuwa ma ta dinga masu ,allah yasa mummunar hatsari suka samu a hanya "burinta daman maryama ta bar duniya ko kuma tayi rayuwar kaskanci ko zama babu aure. sai gashi burinta ya cika batare da ta 'bata kudinta ba ,tana zaune baba gali ya shigo ya tsaya akanta "salma ina fatan dai babu hannunki cikin rasa sadam da maryama ?wani irin kallo ta watsa masa "idan da hannuna me zai faru ?Aa to gsky ni dai babu ruwana kuma muddin da hannunki Kiyi maza kisa a dawo dasu "gsky a wasu lokutan sai naga kamar kana bin bayana amman kuma wani lokacin sai naga kana nuna min wariyar launi ,kai yanzu meye damuwarka dan an nemesu an rasa kai daya kamata kaji dadi kayi farinciki an nemesu an rasa maryama bazata yi rayuwar jin dadi a gidan ba zata bar ya'yanmu suyi rayuwarsu cikin jin dadi ko da yake shi kanshi yusif din yanzu mun rasa gane kanshi ko shekaranjiya da suka zo daurin aure da abbansa bai leko inda muke ba da alamun aikin daakayi masa ya fara barin jikinsa sai an sabanta wani sabo ".
"ni yanzu ba wannan bane damuwata ki fad'a min gsky da hannunki a rashin dawowar su gida ko babu hannunki ciki ?"ta sosa idanunta da hannunwanta duka tace "babu hanuna !"to amman ai shekarajiya naji kina waya da malaminki kina cewa ayi duk yadda zaayi a salwantar da .."kaga dakata daka ji ina magana cewa nayi a salwantar dasu duka ko maryama ?to ai ni ko maryama ma bana son ta rasa rayuwarta bare kuma sadam "tsaki taja tana turo masa baki "ai daidai ne ma idan sadam ya mutu idan bakasani ba bari na fahimtar da kai, idan sadam ya mutu kai ne zakaji dadin rayuwarka dan duk wani abu daya mallaka zai zama naka halak malak kai da sauran yanuwanka hassalima naka ne zai fi na kowa yawa tunda bashi da magaji ,mahaifiyarsa ce kawai ita kadai ranta kuma bazata gajesa ba "kinji zaki sake lalata komai ni dai bana son ran kowa ya salwanta a hannuna ".yana gama fad'ar hk ya fice tabi shi da kallon kaskanci tana ta'be baki "ina ganin shima wannan sokon sai nasa an gama min dashi gabad'aya na huta tai murmushi "wallahi ina farinciki da rashin dawowarsu allah yasa ko gawar su kar agani ."