← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 102

Sashe 17

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ina baki hakuri ne dan kin janye maganrki "to bazan janye ,ba dai ka raina ni ba to wallahi bazaka qara jin dadina ba haka kawai ka dinga gana min azaba kana ganawa yarinyar mutane azaba, laifi ne dan ta rufa maka asiri ta aureka? "wace azaba kuma sweetheart yarinyar da babu abinda ya taba hadani daita ya qarasa maganar yana kallon maryam"ke nace ki bar nan ko ?"ta tsaya tana kallon fuska mami ya sake mata alamar ta bar gun akaro na biyu a matukar fusace ya mike tsaye "Ke kina hauka ne ina mgn kina zaune ? ya buga mata tsawa "

"babu fa inda zata karki sake ki bar wajena matsawar bani nace ba "wai sweetheart me nene haka né ?ya fad'a yana sake kallon maryam dake qoqarin komawa ta zauna yace "wallahi kika cigaba da zama a wajen nan sai na canza miki kamani"maryam ta kalli mami cikin tsananin tashin hankali tace "mami dan girman allah kiyi hakuri ki barni na bar wajena" ai kafin mami ta sake cewa wani abu tuni maryam ta bace .”mami tayi shiru ta zuba tagumi tana dubansa kawai domin ta rasa me za tayi har kusan mintuna goma sannan yace "sweetheart kinyi shiru kina kallona "me zance tunda kafi karfina ka rainani ka nuna min ban isa da kai ba ,duk lokacin da nace ga abinda zakayi bazakayi ba ,”amman wallahi bazanyi kaffara ba muddin baka cigaba da kwana a cikin gidan nan ba na rantse da girman allah babu ni babu kai har abada kuma zan cireka acikin ya'yana sai dai ka nemi wata uwar amman bani zulai ba ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 6

"Wai meye haka ne sweetheart ?"dan  Allah ki daina fad'ar wannan maganar, karki manta nine fa d'anki wannan yarinyar kuma diyar wasu ce "  me yasa zaki dinga fad'ar  wad'an kalaman akaina?me yasa zaki min wannan hukunci ?ya fad'a cikin tsananin 'bacin rai tunda wannan hukunci kika zartar akaina ai gara ki kasheni kawai ki huta nasan bani da gata da galihu just kill me sweetheart ko  kuma  ki janye wannan hukuncin naki ." yayi maganar Kmr zai yi kuka ."

"Okay haka ma zaka fad'a ko ?ta daka masa tsawa yana qoqarin sake bude baki mami ta zuba masa lafiyayyen mari  tana cewa "kaji magana kawai sannan  kayi abinda nace kuma bazan janye kudirina ba wannan umarni ne na baka wallahi idan ka kuskura ka sa'bawa umarnina zaka ji abinda yafi haka daga bakina."

Maryam dake tsaye akan step a tun sanda ta bar wajensu   jin saukar mari  yasa da  sauri ta dafe qirjinta saboda  tashin hankalin data tsinci kanta ciki ,ta qara taku biyu idanunta ya sauka akan mami da ata dake  huci  tmkr zakuna ,wani hawaye ne masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata ,kuka take sosai  tana datasanin kiran mami datai a daren jiya ,dan tasan da bata kirata ba da hankalinta bai tsaidu akanta ba har tayi musu diran makiya da sassafe ba ."

" wayyo allah nah ni maryam na shiga uku nah wannan duk laifina ne”. ta fad'a tana toshe bakinta da hannunwanta duka dan kar sautin kukanta ya bayyana ." cikin tsananin fushi ata yace "okay  sweetheart bazan bi umarninki akan wannan banzar yarinyar ba   "ya fad'a  atakaice yana furza da iska mai zafi daga bakinsa ."

"Naji bazaka bi umarnina ba amman kasani daga yau  babu ni babu kai  ka cigaba da rayuwarka kai kad'ai  har duniya ta nade " tana gama fad'ar  haka ta nufi hanyar step tana  kwallawa maryam  kira da karfi "maryam !!! mrym  ta qarasa saukowa da sauri  ta tsaya  cike da fad'uwar gaba  tana duban mami "d'auko  mayafinki muje "ina kuma mami ?tayi mata tambayar a matukar firgice ."

"gida mana dan bazan tafi na barki acikin  wannan gidan ba "kallon mami take cike da matsanamcin mamaki sannan ta waiga ta kalli ata dake tsaye  taga yadda yake  fidda numfashi har qirjinsa na sama da kasa wanda yake nuna tsananin tashin hankali".
cike da tashin hankali ta shiga girgiza ma mami kai  sannan ta soma magana "mami dan girman allah kiyi hakuri ki barni kiyi tafiyarki ni zan  yi  hakurin zama dashi haka ta fad'a voice dinta na rawa ".

"dan ubanki zaman me zaki cigaba dayi dashi yana  wulakantaki ?maryam tayi narai narai da idanunta tana damke hannuwanta cikin juna ,kin kuwa san babu wulakanci daya kai  miji  yaki kwana a gidan amaryarsa a daren farkonta zafi da ciwo ?"nasani mami dan ni kad'ai nasan halin damuwar dana kwana ciki jiya , tayi mgnr acikin zuciyarta tana qoqarin daidaita natsuwarta ."

"Ya wulakantanki ya tozartaki ya qunsa miki bakincikin da bazaki iya mantawa dashi ba har abada amman ki tsaya kina 'bata min lokacin" mrym ta girgiza mata kai tana mai share hawayenta "amman bake ya wulakanta ya tozarta ba ni yayiwa kuma na gode masa amman kisani bazan tafi na barki cikin wannan halin ba  dan haka ki hau sama yanzu ki d'auko mayafinki muje an gama wannan auren". mami ta fad'a cikin tsanani 'bacin rai.”

"kiyi hakuri mami duk laifina ne dana kiraki na d'aga miki hankali me yasa ma zan kiraki ? sannan me yasa zaki hukuntashi ? da  kin barshi ni ki hukuntani  mami akan abinda na aikata kina zaman zamanki na d'aga miki hankali " maryam ta fad'a hawaye na zubo mata ."you're very stupid so you're the one caused all this problems ? amman dan munafurci  kizo kinawa mutane  kukan munafurci ."

" ina zaman lafiya da mahaifiyata aurenki ya shiga tsakanina daita sannan dan kin cika mahaukaciya ballagaza kika kirata kikace ban kwana gida ba ,dan ubanki idan na kwana a gidan uban me zan miki ? "ya fad'a a fusace ".?a matukar rikice tace "please am sorry I never know she wil act like this "ta fad'a hawaye na sake zubo mata, wani irin mugun kallo ya watsa mata sannan yay qoqarin qarasowa inda take mami  na ganin haka tayi saurin  taresa da hannunta dan ta lura baya cikin  haiyacinsa "karka soma ta'ba min lafiyar yarinya mami ta fad'a muryarta na rawa bata ta'ba ganin yanayinsa haka ba ".

"Yau sai na kashe yarinyar nan da uban daya haifeta ya fad'a cikin cigaba da takowa cikin isa da 'bacin rai jin abinda ya fad'a yasa maryam rungume mami ta baya tana wani irin kuka tmkr qaramar yarinya "mami ki taimakeni dan girman allah "weetheart ki bani hanya naci ubanta na ganar daita kuskurenta wanda har abada bazata sake aikawata wani ba bare ni "ka shiga hankalinka “ita dai tashiga hankalinta “
“ adamcy banason abinda kake min dan babu laifinta ko d'aya idan hukunci ne ni dana mareka zaka hukunta."

"please sweetheart ki matsa dan babu abinda zai hanani ban hukunta wannan yarinyar ba akanta fa sweetheart kika mareni “yana qoqarin kamo  hannun maryam mami ta sake sauke masa wasu marukan ji  kake tas tass !! har biyu ajere ."wannan karon kam ata daskarewa yayi awaje d'aya yana kallon mami cike da tsananin mamaki  abun yayi mugun girgiza shi  "yau sweetheart dinsa ce tay masa mari har uku kuma duk akan wannan banzar yarinyar ".?

maryam kam fashewa tayi da wani sabon kuka ganin abinda  mami ta sake aikatawa " matsawar ka ta'ba maryam ban yafe maka ba tana gama fad'ar haka ta juya rike da hannun maryam sai dai abun mamaki mrym din taki biyota ta turje jikinta na kyamarrr , dole tasa mami ta tsaya ta juyo tare da zuba mata ido tana neman qarin bayani, amman mrym tayi shiru sai hawaye dake sauka akan kuncinta"kina ganin irin wulakanci da yayi min amman da yake ke baki da zuciya zaki ki biyoni wato ke gaki mai ..."

kafin mami ta qarasa maganrta mrym  ta zube kasa gabanta tana kuka tana bata hakuri .""Kiyi hakuri mami wallahi ba haka bane, ba kuma abinda kike nufi bane ,nayi nadama dan allah mami kiyi hakuri ki yafe masa ki daina fad'a masa kalamai haka marasa dadi ,kuma ni babu inda zan biki zan zauna a gidan mijina,da  dad'i da babu zanyi hakuri dashi "tana gama fad'ar haka ta sunkuyar da kanta kasa ganin irin kallon da mami take mata mami tayi shiru kawai tana kallonta gbdy taji kwarin gwaiwarta yayi kasa ."

Jin mami tayi shiru hankalin mrym yayi mugun tashi rawar da jikinta yake ya qaru ta d'ago kanta ahankali taga ita din mami take kallo har lokacin muryarta a sanyaye tace "kiyi hakuri mami kece fa kike bani hakuri da kwarin gwiwar da har muka kawo matakin maaurata ,to me yasa akwana d'aya kawai da nayi  a gidansa zaki d'auki zafi akansa alhalin kin fi kowa sanin waye shi ."?

nan kuma jikin mami yayi sanyi ta tsaya kawai tana cigaba kallon mrym , shi kuwa ata zuba masu ido kawai yayi yana jin zallar 'bacin rai na ratsashi  yaji tsanar mrym ya sake qaruwa da mamaye duk wani sansar jikinsa "wallahi  bancin mami dake tsakaninsu da shi kad'ai yasan irin azabar da zai gana mata amman duk da haka bata tsira ba zai ganar daita Kuskurenta ,runtse idanushi yayi yana cizan lip's dinsa  na kasa da karfi yayinda hawaye ke bin kuncin maryam , tsaki yaja sannan ya juya a fusace ya haye sama cikin tsananin fushi yake taka step ."

Yana shiga d'akin daya zamo nashi ne ya soma zariya aciki he's thinking of if someone else did what his mother did to him today da wallahi allah ne kadai zai rabasu amman sweetheart rayuwarsa ce yana matuqar qaunarta, yana son duk  wani abinda take so wajen had’in aurensa da wannan bazar yarinyar ne  kawai raayinsu ya sha bam bam tsaki yayita ja tare dafe goshinsa dan wani irin sara kanshi ya cigaba da yi ."
Chapter 17 · 0% Book details