Sashe 9
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru ya d'an ratsa d'akin can baba ya d'ago ya dubesa sannan yace "hisham ya dace ace ka kama hanyar komawa gida ko akwai abinda kake so ne...?" ya jefa masa tambayar domin yaji meye raayisa akan nuzla ." sake shafa keyarsa yayi sannan ya d'ago cikin yanayin jin kunya ya fara magana "ammm baba .."dama...dama"!! sai kuma ya fara in ina, shiru baba babba yayi yana kallonsa duk ya wani rikice ahankali yace "relaxes hisham kwantar da hankalinka kayi min magana ina sauraronka" .
da kyar ya samu nutsuwa sannan ya fara magana "dama baba na shigo ne na qara baka hak'uri akan abinda nuzla tayi wallahi tayi nadama baba baza ta sake kwatanta abinda tayi ba dan Allah kayi hak'uri ka yafe mata ka kuma bata wani dama zata gyara
Still shiru baba babba yayi yana kallonsa kawai cike da tausayawa duk mai hankalin da ya kallesa yasan yana cikin shaukin só ,koma yace soyayya na tangalili da rayuwarsa ,lumshe idanunshi yayi kawai dan ba hakurinsa yafi buqata daga garesa ba,a halin yanzu babu abinda yake bukatar ji kamar ya furta masa cewar zai aure nuzla ya had'ata da yar'uwarta".
"kayi hak'uri baba nasan kayi fushi sosai daita yanzu idan ka koreta daga gidan nan ina kake tunanin zata ?".mu godewa allah ma data dawo gida da ba'a nemeta gbdy an rasa ba" still dai shiru baba yayi "baba bana son rayuwarta ta lalace dan Allah kayi hak'uri ka barta ta cigaba da rayuwa acikinmu shine kwanciyar hankalina ;;" yai maganar cikin yanayin tausayi yana zubar da hawaye"..
Hmmm....!!! baba babba ya sauke nannauyen numfashi sannan ya fara magana "hak'ik'a hisham nuzla ta aikata min babban laifi wanda kullum na kan zauna nayi tunanin abinda yasa tayi min haka .
"ina tarbiyar dana bata?"wallahi rai na yab'aci sosai akan abinda tayi amma ba komai komai ya wuce ka daina kuka taci darajanka wallahi banci kai da sai dai ta koma inda ta fito ka tashi ka wuce gida dare nayi Allah yayiwa rayuwarka albarka ka gaishe min da matarka tashi kaje"
wani irin sanyin dad'i hisham yaji ya mamayesa bai san sanda ya rungume baba babba ajikinsa kamar wani k'aramin yaro yana fad'ar "thanks my dad i love you so so much am very proud of u my dad" nima ina alfahari da kai hisham Allah yayiwa rayuwarka albarka "ya sakesa ya fita yana murna baba babba kuwa banda murmushi babu abinda yake yana mamakin irin son da yakewa nuzla "....
karfe d'aya daidai hisham ya shigo gidan kuma akan idanun hajiya zulfa'u da nana hauwa'u ya shigo bayan ya shigo ya rufe koina yana qoqarin kwanciya akan kujera mai zaman mutun uku ya ga mumy tsaye akanshi tana masa mazurai da idanunta gabansa né yayi wani irin mummunar fad'uwa muryarta a kausashe ta soma magana "daga ina kake adaidai wannan lokacin?"shiru yayi tare da sunkuyar da kai cikin tsananin tashin hankali dan bai san me zai fad'a mata ba ,gashi shi bai iya karya ba daya girba mata karya ya huta ."
"Ba da kai nake magana ba kana jina kayi min shiru.?"amm daman ..."sai kuma ya sake yin shiru yana shafa sumar kanshi alokacin da nana hauwa'u take taku domin fitowa daga daki "kai nake sauraro ka ji dani bacci nake ji daman me ?".daman mumy nuzla ce ta kirani shine naje na d'aukota na kaita gida ."
"what ?"!
"hisham kana da hankali kuwa?"ka tsallake matarka kaje ga wata nuzla din banza " numfashi ya sauke sannan ya motsa lip's dinsa yana mai d'ago kanshi daga sunkuyar wa da yayi "mumy nuzla fa ba banza bace, bai kamata dan tayi d'an wannan Kuskuren ba ki d'auki zafi dayawa akanta ,sannan ko babu komai nuzla diyarki kuma kinga dai irin halin da kowa ya shiga akan rashinta ,"kiyi hakuri dan allah nasan nayi ba daidai ba dana fita adaidai wannan lokacin amman nuzla tana da matukar mahimanci arayuwata domin zuciyata ce bazan.."
saukar mari akan kuncinsa ya katse masa maganarsa ,hatta nana hauwa sai da jiyo saukar marin ajikinta dan tana daf da fitowa parlour'n mumy tayi masa marin ."cak ya tsaya yana kallon fuskar mumy dafe da kuncinsa yayinda nana hauwa'u ta fito jiki a matukar sanyaye ta tsaya abakin kofa tana dubansu cike da tashin hankali idanunta suka cicciko da ruwan hawayen abu biyu rashin son da hisham yake nuna mata da kuma na dawowar nuzla gida." "hakika tayi farinciki da jin wannan labari dan daman kullum zuciyarta cike take da tunanin inda take ."
"wallahi wallahi !! sau nawa kaji na rantse idan ka sake min magana akan nuzla zuciyarka ce sai nayi mummunar sa'ba maka ,idan ban iya tsine maka akanta ba allah yayi min yadda yake so, kai shashan ina ne ?da zata gudu tayi shawara da kai sai da zata dawo gida ne tasan da kai ? kai kuma ga shasha tantabara sarkin alqawari ka girba wa matarka karya an kiraka an contract ka kwashi jiki kaje wajenta ,in da da wani abu ya sameka fa ?"tayi masa Kmr zata zubar da hawaye ."
"yarinyar nan tace bata sonka bata sonka !! dole ne hisham ?ko dole ne soyayya da bazaka hakura daita ba "? hisham ya sauke numfashi yana shafa kuncinsa yace "wallahi mumy sai kin ganta ,tayi nadama sosai "babu ruwana da wata nadamarta tunda bata min alkunya akanka ba nima bazan mata ba ,kai kad'ai fa na mallaka arayuwata ni duk yadda muke da mutun yace bai sonka ai sai inda karfi ya qare akan kiyayyarsa ,kasani nuzla diyar dan'uwana ce amman bana sonta da kai tayi rayuwarta kayi naka allah ya bata wani mijin ."
"Haba mumy take it easy now duk fa abun bai kai haka ba "ka kamin baki anan karka sake min magana akanta bana són ji ta fad'a à hargitse, tsayawa yayi kawai yana duban mahaifiyarsa gbdy ta hargitse ta canza masa Kmr wata mai ciwon iska " wallahi ka sake zuwa inda take sai na ...."saukar hannun abba taji a bakinta yana cewa "haba my dear wai meye haka ne ?hucin numfashi ta fesar na 'bacin rai tana dubansa cike da takaici, bai sake barin tace komai ba yaja hannunata zuwa d'akin baccin su yana rarrashinta."
Ahankali nana hauwa'u ta tako ta tsaya gaban hisham tana kallonsa rasa abun yi tayi saboda ganin yadda fuskar hisham tayi tana cikin yanayi na tsnanin damuwa dan haka ta zuba masa idanunta tana canza fuskarta zuwa yanayi na murmushin farinciki shi kuwa sunkuyar da kanshi kasa yayi zuciyarsa na tafasa"yaya hisham !" ta kira sunansa ahankali bai amsa ba yaji ta cigaba da mgn "ina tayaka murnar ganin nuzla hakika naji dadi sosai."
d'ago kanshi yayi ya zuba mata kwayar idanunshi yana kallonta kamar yadda take kallonsa sai dai nashi kallon mai cike da tsananin mamakin jin abinda ta fad'a ne sai daya d'auki wasu mintuna sannan ya motsa bakinsa ya fara magana "idan har da gaske kinji ddin dawowarta na gode "yaya hisham me kake nufi ?". abinda kike nufi nima shi nake nufi ya fad'a a d'an tsawa ce ."
Ta girgiza masa kai jikknta na rawa tace "walalhi har cikin zuciyata naji dadi sosai kuma allah yafi kowa sani meye acikin zuciyata ,meye riba ta idan naji dadin rashin dawowarta?rashin dawowarta ba zai ta'ba canza zani daga halin da nake ciki ba ta fad'a tare da juyawa ta shiga kitchen bata jima ba ta fito hannunta rike da qaramin cup ta durkusa gabansa ta mika masa tana kallon cikin kwayar idanunshi cike da tashin hankali sakamakon rashin sonta da take hangowa acikinsu ."
Yaki amsa ta kai hannunta ta kamo laulusan tafin hannunsa ta saka cup din ciki ,yaki amsa ya cigaba da kallonta "kayi hakuri kasha zaka ji sauki zugin da zuciyarka take maka "na sani akwai zafi akwai radadi da ciwo sosai abaka wanda baka so ,ka sani ni nana hauwa'u bazan takura maka ba bazan hanaka abinda kake so ba ,idan ma ta kama ka auro nuzla ka had'amu kana da damar yin haka bazan damu ba ."
Idan kuma bazaka iya had'amu ba zaka iya sakina ka zauna daita kad'ai na yarda na amince idan kuma zaka iya cigaba da zama dani shima na yarda na amince koda baza kayi komai na aure dani ba, abu daya kawai nake so daga gareka shine ka bani kwanciyar hankali." tsareta yayi da oly eye's dinsa masu firgitartata a yanzu , hakan yasa tayi saurin kawar da kanta gefe tana danne kukanta."
Bin jikinta da kallo yayi yana mamakin jin abinda ta fad'a ,hakan nan yaji tausayinta ya mamaye jinin jikinsa tana da matukar saukin kai sannan bata da yawon damuwa da fari ta tayi qoqarin tsaida mutuncinsa dana iyayensa har ma dana dangi gabdaya domin auresa, sannnan tayi qoqarin karesa a wajen mahaifiyarsa daya fita yanzu kuma tana tayasa murnar dawowar masoyiyarsa har ma da albishir din ya aurota "kai sakarai ka dawo cikin haiyacinka bata son kaga dole zata fad'a haka ,kai ba haka bane to me yasa taki fad'awa mumy komai bayan taji wayarka da zaka fita .?"
Wani zazzafan numfashi ya sauke yana cewa" idan ni kuma bana raayin aurenta fa? ya fad'a tare da amsar cup din hannunta yana sauke numfashi "bazai ma yuwu kace baka son aurenta ba wannan ma ba abinda hankali zai dauka bane nuzla fa zuciyarka ce ta fad'a tana qoqarin mikewa tsaye zata juya taji ya hard'e mata kafafu nan da nan gbdy ta juyo ta zubo jikinsa a gigice take kallonsa duk da tasan shine ya hard'eta amman hakan nan ta tsinci kanta da bashi hakuri ."
"Ka..Ka... kayi haku... "shiiiii! ya fad'a yana kai cup din hannunsa ya ajiye akan table din dake gefensa ya tsura mata ido suna shakar numfashi juna yayinda ita kam tuni ta runtse idanunta dan bazata iya jurar kallon ba dan duk yadda take jin numfashinsa na saukar a fuska da wuyanta hakan bai sa ta bude idanunta ba ."
da kyar ya samu nutsuwa sannan ya fara magana "dama baba na shigo ne na qara baka hak'uri akan abinda nuzla tayi wallahi tayi nadama baba baza ta sake kwatanta abinda tayi ba dan Allah kayi hak'uri ka yafe mata ka kuma bata wani dama zata gyara
Still shiru baba babba yayi yana kallonsa kawai cike da tausayawa duk mai hankalin da ya kallesa yasan yana cikin shaukin só ,koma yace soyayya na tangalili da rayuwarsa ,lumshe idanunshi yayi kawai dan ba hakurinsa yafi buqata daga garesa ba,a halin yanzu babu abinda yake bukatar ji kamar ya furta masa cewar zai aure nuzla ya had'ata da yar'uwarta".
"kayi hak'uri baba nasan kayi fushi sosai daita yanzu idan ka koreta daga gidan nan ina kake tunanin zata ?".mu godewa allah ma data dawo gida da ba'a nemeta gbdy an rasa ba" still dai shiru baba yayi "baba bana son rayuwarta ta lalace dan Allah kayi hak'uri ka barta ta cigaba da rayuwa acikinmu shine kwanciyar hankalina ;;" yai maganar cikin yanayin tausayi yana zubar da hawaye"..
Hmmm....!!! baba babba ya sauke nannauyen numfashi sannan ya fara magana "hak'ik'a hisham nuzla ta aikata min babban laifi wanda kullum na kan zauna nayi tunanin abinda yasa tayi min haka .
"ina tarbiyar dana bata?"wallahi rai na yab'aci sosai akan abinda tayi amma ba komai komai ya wuce ka daina kuka taci darajanka wallahi banci kai da sai dai ta koma inda ta fito ka tashi ka wuce gida dare nayi Allah yayiwa rayuwarka albarka ka gaishe min da matarka tashi kaje"
wani irin sanyin dad'i hisham yaji ya mamayesa bai san sanda ya rungume baba babba ajikinsa kamar wani k'aramin yaro yana fad'ar "thanks my dad i love you so so much am very proud of u my dad" nima ina alfahari da kai hisham Allah yayiwa rayuwarka albarka "ya sakesa ya fita yana murna baba babba kuwa banda murmushi babu abinda yake yana mamakin irin son da yakewa nuzla "....
karfe d'aya daidai hisham ya shigo gidan kuma akan idanun hajiya zulfa'u da nana hauwa'u ya shigo bayan ya shigo ya rufe koina yana qoqarin kwanciya akan kujera mai zaman mutun uku ya ga mumy tsaye akanshi tana masa mazurai da idanunta gabansa né yayi wani irin mummunar fad'uwa muryarta a kausashe ta soma magana "daga ina kake adaidai wannan lokacin?"shiru yayi tare da sunkuyar da kai cikin tsananin tashin hankali dan bai san me zai fad'a mata ba ,gashi shi bai iya karya ba daya girba mata karya ya huta ."
"Ba da kai nake magana ba kana jina kayi min shiru.?"amm daman ..."sai kuma ya sake yin shiru yana shafa sumar kanshi alokacin da nana hauwa'u take taku domin fitowa daga daki "kai nake sauraro ka ji dani bacci nake ji daman me ?".daman mumy nuzla ce ta kirani shine naje na d'aukota na kaita gida ."
"what ?"!
"hisham kana da hankali kuwa?"ka tsallake matarka kaje ga wata nuzla din banza " numfashi ya sauke sannan ya motsa lip's dinsa yana mai d'ago kanshi daga sunkuyar wa da yayi "mumy nuzla fa ba banza bace, bai kamata dan tayi d'an wannan Kuskuren ba ki d'auki zafi dayawa akanta ,sannan ko babu komai nuzla diyarki kuma kinga dai irin halin da kowa ya shiga akan rashinta ,"kiyi hakuri dan allah nasan nayi ba daidai ba dana fita adaidai wannan lokacin amman nuzla tana da matukar mahimanci arayuwata domin zuciyata ce bazan.."
saukar mari akan kuncinsa ya katse masa maganarsa ,hatta nana hauwa sai da jiyo saukar marin ajikinta dan tana daf da fitowa parlour'n mumy tayi masa marin ."cak ya tsaya yana kallon fuskar mumy dafe da kuncinsa yayinda nana hauwa'u ta fito jiki a matukar sanyaye ta tsaya abakin kofa tana dubansu cike da tashin hankali idanunta suka cicciko da ruwan hawayen abu biyu rashin son da hisham yake nuna mata da kuma na dawowar nuzla gida." "hakika tayi farinciki da jin wannan labari dan daman kullum zuciyarta cike take da tunanin inda take ."
"wallahi wallahi !! sau nawa kaji na rantse idan ka sake min magana akan nuzla zuciyarka ce sai nayi mummunar sa'ba maka ,idan ban iya tsine maka akanta ba allah yayi min yadda yake so, kai shashan ina ne ?da zata gudu tayi shawara da kai sai da zata dawo gida ne tasan da kai ? kai kuma ga shasha tantabara sarkin alqawari ka girba wa matarka karya an kiraka an contract ka kwashi jiki kaje wajenta ,in da da wani abu ya sameka fa ?"tayi masa Kmr zata zubar da hawaye ."
"yarinyar nan tace bata sonka bata sonka !! dole ne hisham ?ko dole ne soyayya da bazaka hakura daita ba "? hisham ya sauke numfashi yana shafa kuncinsa yace "wallahi mumy sai kin ganta ,tayi nadama sosai "babu ruwana da wata nadamarta tunda bata min alkunya akanka ba nima bazan mata ba ,kai kad'ai fa na mallaka arayuwata ni duk yadda muke da mutun yace bai sonka ai sai inda karfi ya qare akan kiyayyarsa ,kasani nuzla diyar dan'uwana ce amman bana sonta da kai tayi rayuwarta kayi naka allah ya bata wani mijin ."
"Haba mumy take it easy now duk fa abun bai kai haka ba "ka kamin baki anan karka sake min magana akanta bana són ji ta fad'a à hargitse, tsayawa yayi kawai yana duban mahaifiyarsa gbdy ta hargitse ta canza masa Kmr wata mai ciwon iska " wallahi ka sake zuwa inda take sai na ...."saukar hannun abba taji a bakinta yana cewa "haba my dear wai meye haka ne ?hucin numfashi ta fesar na 'bacin rai tana dubansa cike da takaici, bai sake barin tace komai ba yaja hannunata zuwa d'akin baccin su yana rarrashinta."
Ahankali nana hauwa'u ta tako ta tsaya gaban hisham tana kallonsa rasa abun yi tayi saboda ganin yadda fuskar hisham tayi tana cikin yanayi na tsnanin damuwa dan haka ta zuba masa idanunta tana canza fuskarta zuwa yanayi na murmushin farinciki shi kuwa sunkuyar da kanshi kasa yayi zuciyarsa na tafasa"yaya hisham !" ta kira sunansa ahankali bai amsa ba yaji ta cigaba da mgn "ina tayaka murnar ganin nuzla hakika naji dadi sosai."
d'ago kanshi yayi ya zuba mata kwayar idanunshi yana kallonta kamar yadda take kallonsa sai dai nashi kallon mai cike da tsananin mamakin jin abinda ta fad'a ne sai daya d'auki wasu mintuna sannan ya motsa bakinsa ya fara magana "idan har da gaske kinji ddin dawowarta na gode "yaya hisham me kake nufi ?". abinda kike nufi nima shi nake nufi ya fad'a a d'an tsawa ce ."
Ta girgiza masa kai jikknta na rawa tace "walalhi har cikin zuciyata naji dadi sosai kuma allah yafi kowa sani meye acikin zuciyata ,meye riba ta idan naji dadin rashin dawowarta?rashin dawowarta ba zai ta'ba canza zani daga halin da nake ciki ba ta fad'a tare da juyawa ta shiga kitchen bata jima ba ta fito hannunta rike da qaramin cup ta durkusa gabansa ta mika masa tana kallon cikin kwayar idanunshi cike da tashin hankali sakamakon rashin sonta da take hangowa acikinsu ."
Yaki amsa ta kai hannunta ta kamo laulusan tafin hannunsa ta saka cup din ciki ,yaki amsa ya cigaba da kallonta "kayi hakuri kasha zaka ji sauki zugin da zuciyarka take maka "na sani akwai zafi akwai radadi da ciwo sosai abaka wanda baka so ,ka sani ni nana hauwa'u bazan takura maka ba bazan hanaka abinda kake so ba ,idan ma ta kama ka auro nuzla ka had'amu kana da damar yin haka bazan damu ba ."
Idan kuma bazaka iya had'amu ba zaka iya sakina ka zauna daita kad'ai na yarda na amince idan kuma zaka iya cigaba da zama dani shima na yarda na amince koda baza kayi komai na aure dani ba, abu daya kawai nake so daga gareka shine ka bani kwanciyar hankali." tsareta yayi da oly eye's dinsa masu firgitartata a yanzu , hakan yasa tayi saurin kawar da kanta gefe tana danne kukanta."
Bin jikinta da kallo yayi yana mamakin jin abinda ta fad'a ,hakan nan yaji tausayinta ya mamaye jinin jikinsa tana da matukar saukin kai sannan bata da yawon damuwa da fari ta tayi qoqarin tsaida mutuncinsa dana iyayensa har ma dana dangi gabdaya domin auresa, sannnan tayi qoqarin karesa a wajen mahaifiyarsa daya fita yanzu kuma tana tayasa murnar dawowar masoyiyarsa har ma da albishir din ya aurota "kai sakarai ka dawo cikin haiyacinka bata son kaga dole zata fad'a haka ,kai ba haka bane to me yasa taki fad'awa mumy komai bayan taji wayarka da zaka fita .?"
Wani zazzafan numfashi ya sauke yana cewa" idan ni kuma bana raayin aurenta fa? ya fad'a tare da amsar cup din hannunta yana sauke numfashi "bazai ma yuwu kace baka son aurenta ba wannan ma ba abinda hankali zai dauka bane nuzla fa zuciyarka ce ta fad'a tana qoqarin mikewa tsaye zata juya taji ya hard'e mata kafafu nan da nan gbdy ta juyo ta zubo jikinsa a gigice take kallonsa duk da tasan shine ya hard'eta amman hakan nan ta tsinci kanta da bashi hakuri ."
"Ka..Ka... kayi haku... "shiiiii! ya fad'a yana kai cup din hannunsa ya ajiye akan table din dake gefensa ya tsura mata ido suna shakar numfashi juna yayinda ita kam tuni ta runtse idanunta dan bazata iya jurar kallon ba dan duk yadda take jin numfashinsa na saukar a fuska da wuyanta hakan bai sa ta bude idanunta ba ."