Sashe 81
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gajiyayyun idanunshi ya ware sosai akanta kafin ahankali ya hadiye wani abu daya tsaya masa a makoshi sannan yace "karki manta aikinki kika zo ,kuma kema Kinsan ke kad'ai zasu bukaci gani banda ni ?" duk da haka idan a son raina ne mu shiga tare "ta fad'a tana mai tsareshi da narkakkun idanunta ." suna zaune wnn saurayin da yayi masu iso ya shigo yana cewa "madam ki shiga ke kad'ai mai gida yake jira "ok but dan allah ko zamu iya shiga mu biyu ?cike da jin haushin maganarta yace "tare zakuyi aikin ne ?no ni kad'ai ce !to ke kad'ai ake buqatar gani aciki dan mai gida baya son hayaniya "ya qarasa maganar tare da ta'be baki sannan ya fice ya shige wani office ."
hankalin maryama ya tashi matuka dan har ga allah haka nan taji bata son shiga ita kad'ai qarara damuw ta bayyana acikin kwayar idanunta da shi kad'ai yaya sadam yake iya gani har ya fahimci halin da take ciki ,ahankali yaya sadam ya tsiyaya mata drik ya miko mata ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba ,"why ?! ya tmbyeta yana sake tsareta da idanunshi dafe goshinta tayi tana cewa "bana jin shan komai a yanzu ,tun daya ga haka yasan ko me zai yi 'bata lokacinsa kawai zai yi dan bazata kar'ba ba, dan haka ya mike tsaye suka fito tare tana gabansa yana take mata baya har suka fito dogon hanyar da zata kai su office din ATA wanda alokacin yana tsaye acikin tangamemen office dinsa ya hard'e hannuwansa duka a faffad'an qirjinsa idanunsa kyam akan maryama da yaya sadam ta cikin glass door ,har ta fara taku domin qarasowa zuwa inda office dinsa yake yaga ta tsaya ta koma baya kad'an tana magana da wani da bai san ko waye ba ,sai dai idanuwanta yana kansa ,kwakwa luwarta na hasko mata fuskarsa daga nesa kamar tasan fuskar yayinda shi din ma kallonta yake cikin shigarta ta mutunci kamar ranar farko daya fara d'aura kwayar idanunshi akanta ."doguwar riga ce sanye ajikinta har qasa mai dogon hannu da qaramin hijab dinta mai zip a gaba,sai nikaf kalar hijab din da take sanye dashi wanda iya kwayar idanunta kad'ai ake iya gani ,tsaki yaja da karfi fuskar nan tashi babu wani annurin kirki dan babu abinda ya tsana arayuwarsa kamar 'bata lokaci ,yana wasa da komai arayuwarsa amman baya ta'ba wasa da lokacinsa ,ita kuma abinda ya fahimta kenan daga gareta tana da matukar wasa da lokacinta da kuma damarta ".
"ya kuma kika tsaya madam bayan an fad'a miki ke kad'ai mai gida yake jira ?"ta jiyo sautin muryar segun daga bayansu ta juyo a natse idanunta kyam akan yaya sadam sannan tace "yanzu zan shiga na d'an tsaya muna magana da mijina ne "miji kuma alokacin aiki ? yayi mata tambayar da mamaki akan fuskarsa dan shi a tunaninsa bata da aure tunda ta amsa gayyatarsu a weekend mutumin daya gansu tare kuwa ya d'auka d'an rakiya ne ko kuma saurayinta ."a natse ta gyad'a masa kai tana cewa "Eh mijina ne kuma yayana ne ". ATA wanda yake tsaye yana ciza lip's dinsa da karfi cikin zafin rai bai san wainar da'ake toyawa ba amman haka nan yake jin matsanancin bugun zuciya da kuma 'bacin rai mara misaltuwa "any way kiyi sauri ki shiga kiyi abinda ya kawoki dan mai gida baya wasa da lokacinsa ,akan lokacinsa zai iya aikata komai kafin ta bashi amsa yaya sadam yayi murmushi ya matso kusa daita sosai tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihu wondonsa fuskarsa a sake "karka damu yanzu zata shiga kuma zata maku abinda kuke so "ya fad'a masa haka sannan ya maida hankalinsa kan maryama kamar zai mata numfashi"k'anwata kuma amaryata karki wani damu da jiran da zan miki ni kad'ai abinda nake so dake ki natsu sosai kiyi abinda ya kawoki ina sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda zaki kasance nasan zaki kame min kanki da kuma mutuncina "nan take idanuwanta suka cicciko da ruwan hawaye "yaya sadam na gode sosai ,na gode da yarda daka min ya allah ka yarda dani kamar yadda mijina ya yarda dani "ameen ya hayyu ya qayyum "ya fad'a tare da ciro handkey fari daga gaban aljihun rigarsa ya goge mata hawaye then ya kai bakinsa yayi kissing foring head dinta yana mai karfafa mata gwiwa murmushin gamsarwa ta sakar masa sannan tayi gaba tana d'aga masa hannu ."
bayanta yabi da kallo cike da tausayawa take taka kasa kamar bata son takawa yana tsaye har sai daya ga ta tura kofar office din ahankali ta shiga kusan second biyar ya d'auka tsaye yana kallonta ya kasa d'auke idanunshi akanta ,ATA wanda yake rike da waya a daidai bakinsa da hananu d'aya yayinda d'ayan hannunsa ke rike da wata farar takarda yana magana yana kai kawo acikin office din hakazalika segun na tsaye a gefe guda cike da girmamawa bai kalli inda take ba .”
ahankali yaya sadam ya juya ya fara taku zuwa kasa jikinsa a matukar sanyaye ya bud'e mazauninsa na direba ya shiga ya zauna yana sauke wani irin naunayen ajiyar zuciya sannan ya d'auki wayarsa ya rike yana dubawa missed call's din nadiya ya gani rututu ya sauke numfashi sannan ya kirata tana d'auka ta fashe masa da kuka "menene kuma abun kuka ?"na fad’a miki zan cika miki alkwarin da nayi miki bazan ta’ba cin amanarki ba nan da wasu watanni masu zuwa zamu kasance tare amatsayin ma’aurata ,oh my god dan an d'aura aurena shi yake nufi me ?kinga nadiya banason abinda kike min wallahi kukanki yana mugun 'bata min rai ."
"a natse ATA ya juyo mata fuskarsa sosai tare da tsayawa ya tokare hannunsa dake rike da farar takardar a makeken table din gabansa yana cigaba da wayarsa ."idanun maryama suka sauka kan kyakkyawar fuskar ATA wanda zuwa lokacin ya runtse idanunsa gam zuciyarshi da bakinsa ne kawai ke aiki ,ta tsura masa idanuwanta sosai tana cigaba da kallonsa " tabbas ba gezo idanuwanta suke mata ba shine shararren d'an kasuwan nan data d'auki tsawon lokaci wajen zanashi wanda a qarshe ta kai zanensa ma'aikatansa babu wata gamsashiyar magana mai dadi daga ma'aikatansa ."tayi shiru tana dubansa a tsanake tana shakar kamshn turarensa mai sanyi da ratsa zuciya "tun daga ranar data kai masu zanensa suke nemanta a waya "to mai yasa suke bibiyarta ?"mai yasa suka jawota zuwa nan ?"
ta yiwa kwakwaluwarta tambyr da bata da mai bata amsa wani irin mummunar fad'uwar gaba take ji babu abinda kwakwaluwarta bata hasko mata akansu ba amman tai qoqarin sharewa ta cigaba da tsayuwar jiransa ."bakinta na furta hasbiyallahu la ila a illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim sakamakon wani sabon tsoro da ya shigeta ."
maryama na tsaye har kusan mintuna shabiyar ATA bai gama wayar da yake ba haka zalika bai bud'e kwayar idanunshi ya bata umarnin zama ba haka ma segun na tsaye bai zauna ba adaidai lokacin da qarfe d'aya na rana ta buga wanda a daidai lokacin wasu masallatan sun tada sallarsu dan haka ranta ya soma 'baci ta soma tunanin an janyota ne kawai dan a sake wulakantata a karo na biyu ji tayi kamar ta juya ta wuce shi da segun ta kama gabanta ,ta kalli inda segun yake tsaye shima ya kalleta haka nan ya tsinci kansa da shafa mata qirjinsa alamun tayi hakuri "segun !yes sir ya fad’a cike da girmamawa ya mika masa farar takardar dake rike a hannunsa batare daya bud'e idanunshi ba "ina bukatar copy's dinsu "okay sir ya amsa ya fita da sauri ."ko bayan fitar segun ata bai bud'e idanunshi ba bare yayi mata magana sai kuma taga bai kamata ace tana jiran sai shi ne zai fara mata magana ba dole dai sai itace zata fara masa magana kafin ya saurareta ,dan haka ta qara taku d'aya ta tsaya daidai saitin kunnensa cikin muryar dake nuna alamun gajiya "ta gaishesa bai amsa ba sai ma ya matsa baya ransa a 'bace yayinda zuciyarsa na tafasa dan ya tsani yazo jira duk abinda zaayi masa dole shi zaa jira karo na farko kenan daya zauna jira jiran ma akan itace zata qaru dashi .”
wulakanci da yayi mata yayi mata ciwo, dan ta tsani disgi da wulakanci kamar taja masa tsaki ta fice daga office din sai kuma tayi wani tunani su manyan nan haka halinsu yake kafin kayi nasara akansu dole sai ka kwantar da kai dan haka ta sanyawa zuciyarta hakuri tayi kasa da muryarta da kanta tana wasa da yatsun hannunta "ranka shi dade lokaci na tafiya yana da kyau abani aikin daya kawoni nayi ga kuma lokacin sallah yayi ina buqatar nayi sallah "sake jin sautin zazzakar muryarta ya sanyashi bude idanunshi ahankali tamkar mai tsoron ganin wani abun agabansa ,ya zuba mata tsumammun idanunshi masu mugun rikitarwa yana kallon cikin qwayar idanunta dake d'auke da zara zaran gashi ido itama shi take kallo tana jira daga garesa ".
shiru yayi yana cigaba da kallon cikin kwayar idanunta gabansa na wani irin luguden bugu da karfin gaske,kallon da yake wa kwayar idanunta kallon né na sani "jiki a sanyaye ya nuna mata wata kofa dake manne da office din "ki shiga kiyi alwala "yana gama fad'ar haka ya juya mata baya .”
hankalin maryama ya tashi matuka dan har ga allah haka nan taji bata son shiga ita kad'ai qarara damuw ta bayyana acikin kwayar idanunta da shi kad'ai yaya sadam yake iya gani har ya fahimci halin da take ciki ,ahankali yaya sadam ya tsiyaya mata drik ya miko mata ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba ,"why ?! ya tmbyeta yana sake tsareta da idanunshi dafe goshinta tayi tana cewa "bana jin shan komai a yanzu ,tun daya ga haka yasan ko me zai yi 'bata lokacinsa kawai zai yi dan bazata kar'ba ba, dan haka ya mike tsaye suka fito tare tana gabansa yana take mata baya har suka fito dogon hanyar da zata kai su office din ATA wanda alokacin yana tsaye acikin tangamemen office dinsa ya hard'e hannuwansa duka a faffad'an qirjinsa idanunsa kyam akan maryama da yaya sadam ta cikin glass door ,har ta fara taku domin qarasowa zuwa inda office dinsa yake yaga ta tsaya ta koma baya kad'an tana magana da wani da bai san ko waye ba ,sai dai idanuwanta yana kansa ,kwakwa luwarta na hasko mata fuskarsa daga nesa kamar tasan fuskar yayinda shi din ma kallonta yake cikin shigarta ta mutunci kamar ranar farko daya fara d'aura kwayar idanunshi akanta ."doguwar riga ce sanye ajikinta har qasa mai dogon hannu da qaramin hijab dinta mai zip a gaba,sai nikaf kalar hijab din da take sanye dashi wanda iya kwayar idanunta kad'ai ake iya gani ,tsaki yaja da karfi fuskar nan tashi babu wani annurin kirki dan babu abinda ya tsana arayuwarsa kamar 'bata lokaci ,yana wasa da komai arayuwarsa amman baya ta'ba wasa da lokacinsa ,ita kuma abinda ya fahimta kenan daga gareta tana da matukar wasa da lokacinta da kuma damarta ".
"ya kuma kika tsaya madam bayan an fad'a miki ke kad'ai mai gida yake jira ?"ta jiyo sautin muryar segun daga bayansu ta juyo a natse idanunta kyam akan yaya sadam sannan tace "yanzu zan shiga na d'an tsaya muna magana da mijina ne "miji kuma alokacin aiki ? yayi mata tambayar da mamaki akan fuskarsa dan shi a tunaninsa bata da aure tunda ta amsa gayyatarsu a weekend mutumin daya gansu tare kuwa ya d'auka d'an rakiya ne ko kuma saurayinta ."a natse ta gyad'a masa kai tana cewa "Eh mijina ne kuma yayana ne ". ATA wanda yake tsaye yana ciza lip's dinsa da karfi cikin zafin rai bai san wainar da'ake toyawa ba amman haka nan yake jin matsanancin bugun zuciya da kuma 'bacin rai mara misaltuwa "any way kiyi sauri ki shiga kiyi abinda ya kawoki dan mai gida baya wasa da lokacinsa ,akan lokacinsa zai iya aikata komai kafin ta bashi amsa yaya sadam yayi murmushi ya matso kusa daita sosai tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihu wondonsa fuskarsa a sake "karka damu yanzu zata shiga kuma zata maku abinda kuke so "ya fad'a masa haka sannan ya maida hankalinsa kan maryama kamar zai mata numfashi"k'anwata kuma amaryata karki wani damu da jiran da zan miki ni kad'ai abinda nake so dake ki natsu sosai kiyi abinda ya kawoki ina sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda zaki kasance nasan zaki kame min kanki da kuma mutuncina "nan take idanuwanta suka cicciko da ruwan hawaye "yaya sadam na gode sosai ,na gode da yarda daka min ya allah ka yarda dani kamar yadda mijina ya yarda dani "ameen ya hayyu ya qayyum "ya fad'a tare da ciro handkey fari daga gaban aljihun rigarsa ya goge mata hawaye then ya kai bakinsa yayi kissing foring head dinta yana mai karfafa mata gwiwa murmushin gamsarwa ta sakar masa sannan tayi gaba tana d'aga masa hannu ."
bayanta yabi da kallo cike da tausayawa take taka kasa kamar bata son takawa yana tsaye har sai daya ga ta tura kofar office din ahankali ta shiga kusan second biyar ya d'auka tsaye yana kallonta ya kasa d'auke idanunshi akanta ,ATA wanda yake rike da waya a daidai bakinsa da hananu d'aya yayinda d'ayan hannunsa ke rike da wata farar takarda yana magana yana kai kawo acikin office din hakazalika segun na tsaye a gefe guda cike da girmamawa bai kalli inda take ba .”
ahankali yaya sadam ya juya ya fara taku zuwa kasa jikinsa a matukar sanyaye ya bud'e mazauninsa na direba ya shiga ya zauna yana sauke wani irin naunayen ajiyar zuciya sannan ya d'auki wayarsa ya rike yana dubawa missed call's din nadiya ya gani rututu ya sauke numfashi sannan ya kirata tana d'auka ta fashe masa da kuka "menene kuma abun kuka ?"na fad’a miki zan cika miki alkwarin da nayi miki bazan ta’ba cin amanarki ba nan da wasu watanni masu zuwa zamu kasance tare amatsayin ma’aurata ,oh my god dan an d'aura aurena shi yake nufi me ?kinga nadiya banason abinda kike min wallahi kukanki yana mugun 'bata min rai ."
"a natse ATA ya juyo mata fuskarsa sosai tare da tsayawa ya tokare hannunsa dake rike da farar takardar a makeken table din gabansa yana cigaba da wayarsa ."idanun maryama suka sauka kan kyakkyawar fuskar ATA wanda zuwa lokacin ya runtse idanunsa gam zuciyarshi da bakinsa ne kawai ke aiki ,ta tsura masa idanuwanta sosai tana cigaba da kallonsa " tabbas ba gezo idanuwanta suke mata ba shine shararren d'an kasuwan nan data d'auki tsawon lokaci wajen zanashi wanda a qarshe ta kai zanensa ma'aikatansa babu wata gamsashiyar magana mai dadi daga ma'aikatansa ."tayi shiru tana dubansa a tsanake tana shakar kamshn turarensa mai sanyi da ratsa zuciya "tun daga ranar data kai masu zanensa suke nemanta a waya "to mai yasa suke bibiyarta ?"mai yasa suka jawota zuwa nan ?"
ta yiwa kwakwaluwarta tambyr da bata da mai bata amsa wani irin mummunar fad'uwar gaba take ji babu abinda kwakwaluwarta bata hasko mata akansu ba amman tai qoqarin sharewa ta cigaba da tsayuwar jiransa ."bakinta na furta hasbiyallahu la ila a illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim sakamakon wani sabon tsoro da ya shigeta ."
maryama na tsaye har kusan mintuna shabiyar ATA bai gama wayar da yake ba haka zalika bai bud'e kwayar idanunshi ya bata umarnin zama ba haka ma segun na tsaye bai zauna ba adaidai lokacin da qarfe d'aya na rana ta buga wanda a daidai lokacin wasu masallatan sun tada sallarsu dan haka ranta ya soma 'baci ta soma tunanin an janyota ne kawai dan a sake wulakantata a karo na biyu ji tayi kamar ta juya ta wuce shi da segun ta kama gabanta ,ta kalli inda segun yake tsaye shima ya kalleta haka nan ya tsinci kansa da shafa mata qirjinsa alamun tayi hakuri "segun !yes sir ya fad’a cike da girmamawa ya mika masa farar takardar dake rike a hannunsa batare daya bud'e idanunshi ba "ina bukatar copy's dinsu "okay sir ya amsa ya fita da sauri ."ko bayan fitar segun ata bai bud'e idanunshi ba bare yayi mata magana sai kuma taga bai kamata ace tana jiran sai shi ne zai fara mata magana ba dole dai sai itace zata fara masa magana kafin ya saurareta ,dan haka ta qara taku d'aya ta tsaya daidai saitin kunnensa cikin muryar dake nuna alamun gajiya "ta gaishesa bai amsa ba sai ma ya matsa baya ransa a 'bace yayinda zuciyarsa na tafasa dan ya tsani yazo jira duk abinda zaayi masa dole shi zaa jira karo na farko kenan daya zauna jira jiran ma akan itace zata qaru dashi .”
wulakanci da yayi mata yayi mata ciwo, dan ta tsani disgi da wulakanci kamar taja masa tsaki ta fice daga office din sai kuma tayi wani tunani su manyan nan haka halinsu yake kafin kayi nasara akansu dole sai ka kwantar da kai dan haka ta sanyawa zuciyarta hakuri tayi kasa da muryarta da kanta tana wasa da yatsun hannunta "ranka shi dade lokaci na tafiya yana da kyau abani aikin daya kawoni nayi ga kuma lokacin sallah yayi ina buqatar nayi sallah "sake jin sautin zazzakar muryarta ya sanyashi bude idanunshi ahankali tamkar mai tsoron ganin wani abun agabansa ,ya zuba mata tsumammun idanunshi masu mugun rikitarwa yana kallon cikin qwayar idanunta dake d'auke da zara zaran gashi ido itama shi take kallo tana jira daga garesa ".
shiru yayi yana cigaba da kallon cikin kwayar idanunta gabansa na wani irin luguden bugu da karfin gaske,kallon da yake wa kwayar idanunta kallon né na sani "jiki a sanyaye ya nuna mata wata kofa dake manne da office din "ki shiga kiyi alwala "yana gama fad'ar haka ya juya mata baya .”