Sashe 82
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daren da zasu tafi kanon kasa bacci tayi baki daya,tsaf ta gama hada komai,hatta da kayan da zata sanya goben ta waresu gefe,cikin irin wannan zaman taji kuwwar wayarta,ta janyota tana dubawa,baquwar lamba cr,maidata tayi ta aje don a yanzun tsoron daga baquwar lamba take,sai data fuskanci wayar na neman hanata sakewa ya sanya ta dagawa,muryar alqasim ce ta bayyana,yasan kadan daga aikinta ta datse wayar wanda baya fatan haka,saboda yaci wahala kafin ya kai ga samun lambarta,hakan ya saka ya cikata da magiyar ta tsaya ta saurareshi,bai kyautu ta watsa masa qasa a ido bo saboda qimar mahmoud,hakan ya sanya ta tsaya tana sauraronsa zuciyarta fal da mamakin inda ya samu ainihin lambarsa,gaisuwa sukayi ta mutunci ya sake mata sannu da jiki ta amsa masa,shiru yayi kamar ba zaice komai ba hakan ya sanya ta buqaci kashe wayarta,wanda shi ya zaburar da shi ya soma magana,tatsuniyar gizo dai bata wuce ta qoqi,
"Alqasim,ni bazawara ce na taba aure,ko da ina da ra'ayin aure banda ra'ayim auren saurayi,ballantana ma mi ban hango shekarun da na tsara ba kafin na sake aure,babu lokaci,saboda haka ina mai godiya bisa qaunar daka nunan,kuma ina mai baka haquri tare da addu'ar ubangiji ya baka wadda ta fini" ta kaiwa qarshe ta kashe wayar ta cillar gefe tare da mirginawa ta kwanta ta runtse ido tana son bacci ya dauketa ko zata samu damar tashi gobe da wuri ta shirya.
******** ******* *******
Qarfe sha daya na rana dukkan shirin tafiya ya kammala,wannan karon har da abban laila zasu tafi a mota daya,sun gama komai har motar ma drivern ta faka ta bakin get din gidan,duka suna ciki zaune,abban laila kawai da ya shiga yiwa baaba sallama suke jira,wanda sabonsa ne baiyin kowacce tafiya bai sanarwa baban ba,saboda ya daukeshi a mazaunin mahaifi.
Anty dije ce tayi mantuwa cikin gidan,botiki ne data zubawa mama sabulun salo mai yawa a ciki wanda su zainab zasu hada sabulun gyaran jiki,sau biyu tana aiken laila bata ganshi ba,ganin zata bata mata lokaci kada abbansu ya fito ba'a dauko ba ya sanyata tura sumayya.
Kunnenta maqale da waya suna waya da abdur rahman,yayin da daya hannun ke riqe da dan botikin,ta sanyo qafarta waje kenan kunnenta ya jiyo mata muryar tasa ginshira yana fadin
"Amma why not kubi jirgi,akwai jirgi daga nan zuwa kano 12"dariya uncle farouq yayi
"wannan kam ai su ku manya,ba damuwa,awa biyar ne ba dadewa zamuje" hannu ya bashi yana fadin
"Allah ya tsare"
"Amin amin,wataqil kafin mu dawo kun koma,sai gani na gaba" murmushi kawai yayi ya juya,har a lokacin tana labe bakin qofar,hakanan jikinta ke rawa har wayar hannunta ta subuce ta fadi bata sani ba
"Ah ah,ashe kin dauko me kuma kike a tsaye a nan?" Anty dije ta tambayeta wadda ta biyo sahunta jin shirun yayi yawa
"Ba komai...fitowa zanyi dama" ta fada muryarta na rawa tana durqusawa tare da soma tattare wayarta data watse a gun,bin wayar anty dije tayi da kallo cikin ranta tana tambayar kanta me ya faru har ta kammala tattarewar ta juya tabi bayanta bayan ta rufe gidan.
TOFA!
*Mrs muhammad ce👑*
📚📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
6⃣2⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN SABODA BALA'I DA JAHANNAMA KE DA SHI HAR WANI SASHE NATA YANA NEMAN TSARI DA WANI SASHEN?*
*Allahumma ajirna minan nar*
_________________________________
Luf tayi cikin motar idanuwanta a lumshe,duk da hayaniya da karadin da suke tayi cikin motar amma babu ita,bata san me ya haddasa mata mutuwar jiki ba,batasan me take tsoro ba,abu daya ta sani muryar na daga mata hankali,muryar na sanyata ta tuna da mukhtarinta,anty dije ma tayi tsammani bacci take saboda ta san jiya batayi wani isashshen bacci ba,yau kuma ta riga kowa sammakon tashi,tun tana jin hayaniyarsu sama sama har bacci barawo yayi awon gaba da ita.
Kamar kullum yau ma sun tsayawa wannan restaurant din don cin abinci saidai banda ita,zaman ta tayi cikin mota sai takeaway sukayi mata sannan suka wuce.
Yamma lis suka isa kano ta dabo tumbin giwa,ko da me kazo an fika,gari ba kani ba dajin Allah,wani farinciki ya dinga shigarta tun kafin su qarasa gida,iskar garin na kano take shaqa sosai,taje farinciki ya lullube zuciyarta,doki ya mamaye zuciyarta,kewar mama malam abdallah dama su zainab suka dawo mata sabuwa fil,kamar kuwa uncle farouq ya sani yace a fara biyawa gida a sauke sumayyan,anty dije zatayi qorafi kan ba haka ba su wuce gida idan sun huta baki daya sazo gobe yace a'a sam tana son taga mamanta,hakan ya mata dadi matuqa duk da ta boye dokinta,suna sauketa kuwa suka wuce kan sai gobe zasu shigo,tana fara'a ta daga musu hannu sannan ta sanya kanta cikin gidan yaran maqota na shiga mata da jakarta.
A tsakar gidan ta ware muryarta tana kwada sallama,abdallah ne ya soma fitowa da gudu halima na biye da shi,da gudu ya qarasa wajenta yana kiran
"Mami na"
"Abdallah na" itama ta fada cike da kewa ta durqusa tare da ware hannayenta ya fada ciki ta miqe rungume da shi tana dubansa fuskarta fal murmushi,ya qara kyau wayo da girma kamar ba abdallahnta ba,kallo daya zakayi masa ka tabbatarwa kanka yana cikin kwanciyar hankali tare da samun cikakkiyar kulawa,yayi bul bul da shi,fes kamanninsa da babanshi kan fuskarsa.
Dakin mama ta shige tare da su halima da maman,tana sanya kanta falon taga amina zaune matar abubakar ciki a gaba,baki sumayyan ta bude tana kallonta
"Antynmu kice kema kina gidan namu yau?"
"Gidanku ko gidanmu,aike kam yanzu baquwarmu ce" dariya sumayya tayi
"Allah sarki anty amina,kice kinyi nauyi shi yasa kika kasa tasowa ki tarbeni" dariya aminan tayi a dan kunyace saboda mama na gurin,gaban maman sumayya ta qarasa idonta a kanta tana jin wani dadi na gajin mahaifiyar tata,itama maman kallonta take,a gabanta ta durqusa ta gaidata,cikin farinciki maman ta amsa tana tambayarta ina dijen kuma,nan ta sanar mata sai gobe zasu shigo,hira ce ta barke babu qaqautawa tsakaninsu abdallah na kan cinyarta,yaqi yarda ko nan da can yaje,halima ke dungureshi tana cewa
"Zata tafi ta barmu da kai ne mai qaton kai da kaqi zuwa wajen kowa" amina ke kareshi
"Barshi malama,yaro da uwarsa,ai yayi qoqari ma,yaushe rabon da ya ganta?" Har magariba suna hira,sai da aka gama sallah magariba sannan sumayya ta cewa zainab ta hada mata ruwa zata yi wanka,dariya zainab tayi
"Wankan lafiya da daren nan?"
"Bazan iya bacci ba sai nayi wallahi" dariya ta kuma yi
"Kice ba banza ba yaya sumayya kika dad wannan dan banzan kyan,wallahi abuja ta karbeki,baki ga yadda kika koma 'yar gayu ba"
"Hada min ruwan sai kizo kici gaba da sharhin naki" sumayya ta fadi tana dariya,anty amina ce ta karbe
"Gaskiya ai ta fadi,wallahi garin ya amsheki sosai"
"Kin biye mata kenan antynmu" ta fada tana dariya anty aminan na tayata.
Bayan tayi wanka ta sake shiryawa cikin doguwar riga ta wani cotting din yadi mau gajeran hannu,ta yane kanta da dan qaramin mayafi ta dawo falon mama,a nan suja zuba tuwon dare baki daya idan ka dauke maman,suna ci suna ci gaba da hira,har yanzun idanuwan maman ma kanta,ita kanta tasan diyar tata ta soma sauyawa kamar ba ita ba,ta tabbatar sauyin rayuwa ya fara samuwa a gareta,cikin zuciyarta ta dinga mata addu'ar Allah ya azurta ta da miji na gari,wanda zaici gaba da dawainiya da ita cikin ingantacciyar rayuwa.
Suna gab da kammala cin tuwon malam da yaya abubakar sukayi sallama,amina tayi saurin janyo hijabinta ta sanya,yau malam da kanshi ya shigo falon maman,fuskanshi shina dauke da farincikin ganin diyar tasa,cikin girmamawa ta gaida malam din ya amsa yana tambayarta mutan abuja,tace kowa lpy suna gaida ka,amma gobe su antyn zasu shigo,madallah malam din yace sannan ya fice yana cewa bari ya barta ta huta da gajiyan hanya,murmushin jin dadi kawai tayo ganin yadda kowa cikin 'yan uwanta ke qoqarin nuna mata qauna da kulawa.
"Hala nan gaba kadan zamu kasa ganeki sumayya,irin wannan kumatu haka" sosai ya bata dariya,bama ita kadai ba duk jama'ar falon,don babu wata qiba da tayi tsabar tsokana ce,saidai duk wanda ya kalleta zauga yadda fatarta ta murje tayi kyau,hutu da wayewa suka sake bayyana a jikinta,sai da ya gama tsokanar tasa sannan yace
"Dazun dama nake cewa ko baku zo ba cikin satin nam zaki ganni kafin ku wuce london,inaso muyi maganar kudin abdallah dake hannuna,sun fara yawa gaskiya ya kamata kuma ayi tunanin sake fadada wani kasuwancin da su" dubanshi tayi
"Haba ya abbakar,kaima fa kamar uba kake gunsa,duk abinda ka yanke dai dai ne,baya ga haka ga malam ga mama ga yaya yahanasu ko su sun isa kayi shawara da su ku zartar da duk hukuncin da ya dace ko?"
"Eh duk munyi magana da su kuma su suka ce aji ta bakinki,amma koma me ake ciki kan ki koma zamuyi magana,yaushe zaku koma?"
"Ba zamu wuce sati daya ba"
"To ba damuwa....ke taso mu tafi" ya fada yana miqewa,amina tasan da ita yake,sai ta shiga yunqurin miqewa
"Dakata mata mana,yanzu fa ta gama cin abinci ko fada mata baiyi ba,koma ki zauna ki shirya a nutse" cewar mama tana hade rau,dariya ta kama sumayya,ba shakka idan da duka haka surukai suke da ba'a dinga samun baraka tsakanin surukai ba.
"Idan kin gama ki kirani a waya,zan je ayimin aski" ya fada yana ficewa ta amsa da to.
Halima ce ya shiga tsokanarta kan tafiyarsu london
"Yaya sumayya dama nice,ki barmim don Allah" haka ta dinga fada,murmushi kawai tayi tana kallonsu,abinda basu sani ba ita din ce ke jin dama ita ce su,basu taba fuskantar wata matsala ba,ko yaushe suna tare da mamarsu da babansu,suna cikin garinsu,basu da wata damuwa da ke hanasu bacci ko ta sanyasu a halin tunani,tana ganin quruciya ce kadai ke sasu sha'awar zamowa ita.
Sai takwas na dare amina suka tafi da ya abubakar,zuwa lokacin itama bashin baci da gajiyar hanya sunyo mata kabbara,tilas ta musu sallama ta dauki abdallah da yayi bacci kan kafadarta suka nufi daki.
******* ******* *******
"Alqasim,ni bazawara ce na taba aure,ko da ina da ra'ayin aure banda ra'ayim auren saurayi,ballantana ma mi ban hango shekarun da na tsara ba kafin na sake aure,babu lokaci,saboda haka ina mai godiya bisa qaunar daka nunan,kuma ina mai baka haquri tare da addu'ar ubangiji ya baka wadda ta fini" ta kaiwa qarshe ta kashe wayar ta cillar gefe tare da mirginawa ta kwanta ta runtse ido tana son bacci ya dauketa ko zata samu damar tashi gobe da wuri ta shirya.
******** ******* *******
Qarfe sha daya na rana dukkan shirin tafiya ya kammala,wannan karon har da abban laila zasu tafi a mota daya,sun gama komai har motar ma drivern ta faka ta bakin get din gidan,duka suna ciki zaune,abban laila kawai da ya shiga yiwa baaba sallama suke jira,wanda sabonsa ne baiyin kowacce tafiya bai sanarwa baban ba,saboda ya daukeshi a mazaunin mahaifi.
Anty dije ce tayi mantuwa cikin gidan,botiki ne data zubawa mama sabulun salo mai yawa a ciki wanda su zainab zasu hada sabulun gyaran jiki,sau biyu tana aiken laila bata ganshi ba,ganin zata bata mata lokaci kada abbansu ya fito ba'a dauko ba ya sanyata tura sumayya.
Kunnenta maqale da waya suna waya da abdur rahman,yayin da daya hannun ke riqe da dan botikin,ta sanyo qafarta waje kenan kunnenta ya jiyo mata muryar tasa ginshira yana fadin
"Amma why not kubi jirgi,akwai jirgi daga nan zuwa kano 12"dariya uncle farouq yayi
"wannan kam ai su ku manya,ba damuwa,awa biyar ne ba dadewa zamuje" hannu ya bashi yana fadin
"Allah ya tsare"
"Amin amin,wataqil kafin mu dawo kun koma,sai gani na gaba" murmushi kawai yayi ya juya,har a lokacin tana labe bakin qofar,hakanan jikinta ke rawa har wayar hannunta ta subuce ta fadi bata sani ba
"Ah ah,ashe kin dauko me kuma kike a tsaye a nan?" Anty dije ta tambayeta wadda ta biyo sahunta jin shirun yayi yawa
"Ba komai...fitowa zanyi dama" ta fada muryarta na rawa tana durqusawa tare da soma tattare wayarta data watse a gun,bin wayar anty dije tayi da kallo cikin ranta tana tambayar kanta me ya faru har ta kammala tattarewar ta juya tabi bayanta bayan ta rufe gidan.
TOFA!
*Mrs muhammad ce👑*
📚📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
6⃣2⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*KO KUNSAN SABODA BALA'I DA JAHANNAMA KE DA SHI HAR WANI SASHE NATA YANA NEMAN TSARI DA WANI SASHEN?*
*Allahumma ajirna minan nar*
_________________________________
Luf tayi cikin motar idanuwanta a lumshe,duk da hayaniya da karadin da suke tayi cikin motar amma babu ita,bata san me ya haddasa mata mutuwar jiki ba,batasan me take tsoro ba,abu daya ta sani muryar na daga mata hankali,muryar na sanyata ta tuna da mukhtarinta,anty dije ma tayi tsammani bacci take saboda ta san jiya batayi wani isashshen bacci ba,yau kuma ta riga kowa sammakon tashi,tun tana jin hayaniyarsu sama sama har bacci barawo yayi awon gaba da ita.
Kamar kullum yau ma sun tsayawa wannan restaurant din don cin abinci saidai banda ita,zaman ta tayi cikin mota sai takeaway sukayi mata sannan suka wuce.
Yamma lis suka isa kano ta dabo tumbin giwa,ko da me kazo an fika,gari ba kani ba dajin Allah,wani farinciki ya dinga shigarta tun kafin su qarasa gida,iskar garin na kano take shaqa sosai,taje farinciki ya lullube zuciyarta,doki ya mamaye zuciyarta,kewar mama malam abdallah dama su zainab suka dawo mata sabuwa fil,kamar kuwa uncle farouq ya sani yace a fara biyawa gida a sauke sumayyan,anty dije zatayi qorafi kan ba haka ba su wuce gida idan sun huta baki daya sazo gobe yace a'a sam tana son taga mamanta,hakan ya mata dadi matuqa duk da ta boye dokinta,suna sauketa kuwa suka wuce kan sai gobe zasu shigo,tana fara'a ta daga musu hannu sannan ta sanya kanta cikin gidan yaran maqota na shiga mata da jakarta.
A tsakar gidan ta ware muryarta tana kwada sallama,abdallah ne ya soma fitowa da gudu halima na biye da shi,da gudu ya qarasa wajenta yana kiran
"Mami na"
"Abdallah na" itama ta fada cike da kewa ta durqusa tare da ware hannayenta ya fada ciki ta miqe rungume da shi tana dubansa fuskarta fal murmushi,ya qara kyau wayo da girma kamar ba abdallahnta ba,kallo daya zakayi masa ka tabbatarwa kanka yana cikin kwanciyar hankali tare da samun cikakkiyar kulawa,yayi bul bul da shi,fes kamanninsa da babanshi kan fuskarsa.
Dakin mama ta shige tare da su halima da maman,tana sanya kanta falon taga amina zaune matar abubakar ciki a gaba,baki sumayyan ta bude tana kallonta
"Antynmu kice kema kina gidan namu yau?"
"Gidanku ko gidanmu,aike kam yanzu baquwarmu ce" dariya sumayya tayi
"Allah sarki anty amina,kice kinyi nauyi shi yasa kika kasa tasowa ki tarbeni" dariya aminan tayi a dan kunyace saboda mama na gurin,gaban maman sumayya ta qarasa idonta a kanta tana jin wani dadi na gajin mahaifiyar tata,itama maman kallonta take,a gabanta ta durqusa ta gaidata,cikin farinciki maman ta amsa tana tambayarta ina dijen kuma,nan ta sanar mata sai gobe zasu shigo,hira ce ta barke babu qaqautawa tsakaninsu abdallah na kan cinyarta,yaqi yarda ko nan da can yaje,halima ke dungureshi tana cewa
"Zata tafi ta barmu da kai ne mai qaton kai da kaqi zuwa wajen kowa" amina ke kareshi
"Barshi malama,yaro da uwarsa,ai yayi qoqari ma,yaushe rabon da ya ganta?" Har magariba suna hira,sai da aka gama sallah magariba sannan sumayya ta cewa zainab ta hada mata ruwa zata yi wanka,dariya zainab tayi
"Wankan lafiya da daren nan?"
"Bazan iya bacci ba sai nayi wallahi" dariya ta kuma yi
"Kice ba banza ba yaya sumayya kika dad wannan dan banzan kyan,wallahi abuja ta karbeki,baki ga yadda kika koma 'yar gayu ba"
"Hada min ruwan sai kizo kici gaba da sharhin naki" sumayya ta fadi tana dariya,anty amina ce ta karbe
"Gaskiya ai ta fadi,wallahi garin ya amsheki sosai"
"Kin biye mata kenan antynmu" ta fada tana dariya anty aminan na tayata.
Bayan tayi wanka ta sake shiryawa cikin doguwar riga ta wani cotting din yadi mau gajeran hannu,ta yane kanta da dan qaramin mayafi ta dawo falon mama,a nan suja zuba tuwon dare baki daya idan ka dauke maman,suna ci suna ci gaba da hira,har yanzun idanuwan maman ma kanta,ita kanta tasan diyar tata ta soma sauyawa kamar ba ita ba,ta tabbatar sauyin rayuwa ya fara samuwa a gareta,cikin zuciyarta ta dinga mata addu'ar Allah ya azurta ta da miji na gari,wanda zaici gaba da dawainiya da ita cikin ingantacciyar rayuwa.
Suna gab da kammala cin tuwon malam da yaya abubakar sukayi sallama,amina tayi saurin janyo hijabinta ta sanya,yau malam da kanshi ya shigo falon maman,fuskanshi shina dauke da farincikin ganin diyar tasa,cikin girmamawa ta gaida malam din ya amsa yana tambayarta mutan abuja,tace kowa lpy suna gaida ka,amma gobe su antyn zasu shigo,madallah malam din yace sannan ya fice yana cewa bari ya barta ta huta da gajiyan hanya,murmushin jin dadi kawai tayo ganin yadda kowa cikin 'yan uwanta ke qoqarin nuna mata qauna da kulawa.
"Hala nan gaba kadan zamu kasa ganeki sumayya,irin wannan kumatu haka" sosai ya bata dariya,bama ita kadai ba duk jama'ar falon,don babu wata qiba da tayi tsabar tsokana ce,saidai duk wanda ya kalleta zauga yadda fatarta ta murje tayi kyau,hutu da wayewa suka sake bayyana a jikinta,sai da ya gama tsokanar tasa sannan yace
"Dazun dama nake cewa ko baku zo ba cikin satin nam zaki ganni kafin ku wuce london,inaso muyi maganar kudin abdallah dake hannuna,sun fara yawa gaskiya ya kamata kuma ayi tunanin sake fadada wani kasuwancin da su" dubanshi tayi
"Haba ya abbakar,kaima fa kamar uba kake gunsa,duk abinda ka yanke dai dai ne,baya ga haka ga malam ga mama ga yaya yahanasu ko su sun isa kayi shawara da su ku zartar da duk hukuncin da ya dace ko?"
"Eh duk munyi magana da su kuma su suka ce aji ta bakinki,amma koma me ake ciki kan ki koma zamuyi magana,yaushe zaku koma?"
"Ba zamu wuce sati daya ba"
"To ba damuwa....ke taso mu tafi" ya fada yana miqewa,amina tasan da ita yake,sai ta shiga yunqurin miqewa
"Dakata mata mana,yanzu fa ta gama cin abinci ko fada mata baiyi ba,koma ki zauna ki shirya a nutse" cewar mama tana hade rau,dariya ta kama sumayya,ba shakka idan da duka haka surukai suke da ba'a dinga samun baraka tsakanin surukai ba.
"Idan kin gama ki kirani a waya,zan je ayimin aski" ya fada yana ficewa ta amsa da to.
Halima ce ya shiga tsokanarta kan tafiyarsu london
"Yaya sumayya dama nice,ki barmim don Allah" haka ta dinga fada,murmushi kawai tayi tana kallonsu,abinda basu sani ba ita din ce ke jin dama ita ce su,basu taba fuskantar wata matsala ba,ko yaushe suna tare da mamarsu da babansu,suna cikin garinsu,basu da wata damuwa da ke hanasu bacci ko ta sanyasu a halin tunani,tana ganin quruciya ce kadai ke sasu sha'awar zamowa ita.
Sai takwas na dare amina suka tafi da ya abubakar,zuwa lokacin itama bashin baci da gajiyar hanya sunyo mata kabbara,tilas ta musu sallama ta dauki abdallah da yayi bacci kan kafadarta suka nufi daki.
******* ******* *******