Sashe 107
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A daddafe ta haqura ta kai ranar alhamis kamar yadda ta gayawa anty dije,sannan ta shirya tafiya,wanda ya rage sauran kwanaki goma sha hudu bikin,anty dije ta bata saqonni gun mama sannan tace suma nan da kwana bakwai suna tafe,wannan karon saboda tsabar zaquwa ta tafi bata iya jira abban laila ya dawo daga kaduna da yaje ba ya hadata da driver,motar haya ta hawo ta tafi,ba yadda anty dije bata yi ba amma ta kasa daurewa ta jira.
Tana hanya taji kira,lambar amira ce,tun kafin ta daga ta saki murmushi
"Amaryar saifullahi bada kanki a sare" kamar wadda ke shirin sakin kuka ta soma mata qorafin kota nemeta ko?,sun hada baki da saifullahi sun sace mata wayarta,shi din ma ya rufe gidan ba shiga ba fita wai sai sun huta,ya kuma hanata wayarshi sai yau ya bata wayan,dariya ta dinga mata din yasan da wannan plan din,sai da ta gama qorafinta sannan suka gaisa tace yaushe zata zo don Allah
"Kin ganni hanyar kano,wani bikin ya sake kira na,bikin zainab dita"
"Wayyo,dama a kusa da namu ne,naci burin zuwa fa namecy" dariya tayi
"saidai ki tara ana halima idan Allah ya kawo"haka nan suka gama hirarsu ta baiwa saifullahin suka gaisa sannan sukayi sallama.
Kamar ko yaushe sunyi murna da zuwanta,mama nata tsokanar abdallah wai ya qara qiba
"Amma dai zaka koma ko?" Wuya ya maqale a kafadarsa
"Nan yafi dadi,can kullum kuna rufe a gida" dariya suka saki don abdallahn badai son yawo da wasa ba,hararshi sumayya tayi
"Nima babu inda zaka bini,rigimammen kawai" ko a jikinsa dariyarsa ma ya sanya abinsa,washe gari yaya yahansu tazo ta daukeshi ma sukayi tafiyarsu,sai ranar kamun zainab tace zata dawo da shi.
Tunda tazo babu zama suna ta shirye shirye ba kama hannun yaro,ita da anty salma qanwar mama da anty amina matan yaya abubakar,sunyi waya abdur rahman bai nan amma zai dawo da shi za'a yi daurin auren shi yasa take hidimarta hankali kwance ba wani damuwa ko takura,cikin ikon Allah da baiwarsa komai yana tafiya daidai,sumayya taga yadda ake komai cikin tsari saboda haka ta dage ta tsarawa 'yar uwarta komai yadda zai qawatar ya kuma burge,kudi sosai tasa yaya abubakar ya bata bayan wanda anty dije da uncle farouq suka bata,dinkuna sosai ta yiwa mama,atamfofi masu tsada da kyau,harda mayafai da takalma duk da yaya abubakar yayi musu amma tace wannan nata ne,sannan ta siyawa malam gezna ta asalin wadda zai sanya ranar daurin aure,takalmi mai kyau harda agogo da turare da sabon rawani fari qal,kasancewar malam din ba baya bane wajen tsafta shi yasa kusan kayansa galibi farare ne,aka yi masa dinkin babbar riga 'yar ciki da wando,ita kam dama bata da matsalar sutura sai anko kawai data yi,sai abdallah data masa shaddar daurin aure duk da dumbin kayan da yake da su,saura kwana tara biki kuwa saiga anty dije da iyalinta,nan aka shiga hidima sosai.
Kan hanyarsa yake ta dawowa daga airphort bayan ya kai anty dije da yaranta sun tashi zuwa kano,tun daga nesa yaga kamar motar baabaa prof a tsaye,hakan ya sanya ya rage gudun motar ya qaraso a hankali ya faka tashi motar bayan tasu sannan ya bude ya fito.
Baabaan ne tsaye gaban motar,kana dubanta kasan matsala ta basu,qarfen nasara da bashi da tabbas,motar kwata kwata shekararta guda,ba yadda mustapha baiyi kan a canzata ba kamar yadda ya saba sauya masa motocin hawanshi amma yace a sauya sauran amma ita banda ita,yana jin dadin motar,da ita yake zuwa gidan gonan sulensa duk qarshen sati,duk randa zai tafin baya tafiya da wasu motocin face wadda ita kadai zai hau,kuma daga shi sai druvansa,yana jin dadin zama gidan gonar,ya zazzaga yaga gidan gonar sosai,yanajin nishadi da farincikin yadda dukiyar sulensa ke habaka,fatanshi Allah nuna masa ranar da zaiga sulenshi,a irin haka ne yau motar ta tsaya musu a hanya.
A aladabce uncle farouq ya qaraso
"Subhanallah,baba kada dai ace qarfen nasara ya muku tsiya?" Cikin murmushi mai dauke da dattako yace
"Wallahi kuwa,to ya za'ayi,yau da gobe ai sai Allah,babu wani abu dake matabbaci"
"Gaskiya ne" inji uncle farouq yana fidda waya daga aljihunshi yana fadin
"Bari a kira gida to a turo wata ko baabaa,tamu motar ba lallai ka iya shiga irinta ba" murmushi ya kuma subucewa baban,har ya sanyashi ya juya ya sake kallon motar duk da ya santa,motace mai lafiya wadda bata da wani aibu ko makusa,ko kai waye zaka iya hawanta,amma ya sani cewa irin motocin da mustapha ke ajjiye masa yana hawa shi ya sanya farouq din tunanin yafi qarfin wannan
"Haba faruqu,saidai kawai idan rawar hawa motar take kake min,amma ni din waye da bazan hau wannan motar ba" ya fada yana dariya,bakinsa ya rufe shima yana dariya
"Afuwa baabaa" ya fada yana bude masa gaban motar,kafin ya shiga ya waiwaya ya dubi drivan nashi
"Kada ka tsawaita tsaiwa a nan,ka kira bakaniken nan,idan bakaniken ya iso ka bashi muqullan ka taho gida" a ladabce yace
"Yallabai man yace kada a sake barinka ka hau motar da baniken hanya ya tabata ranka ya dade" murmushi ya saki
"Qyale wannan,idan na biye masa ma a jirgin sama zan dinga yawo,ni waye da bakaniken hanya bazai taban mota ba,shi yasa na hana a kira gida agaya musu motarmu ta tsaya nasan zai iya jin zancan ya damu mutane da batub sauyan motoci,bayan ni din duka kwana nawa ya rage mana a duniya,kayi yadda nace kawai"
"To ranka ya dade" inji drivan,baban ya juya ya shiga motar faruqun ya rufe ya zagaya shima ya shiga ya tadata suka fara tafiya.
"Asalina daga qauye na fito faruqu,kiwon dabbobi na dinga yi ni da aminina,da can ko jaki bani da shi na hawa bare a kai ga mota,din me zan dinga manta asalina,ita duniya gaba dayanta yadda ka dauketa haka take zuwa maka,mafi daraja cikin mutane shine wanda a zahiri ya isan amma yake daukan kanshi ba'a bakin komai ba,girman kai rawanin tsiya ne,wanda ke zaton ya isa kuma sai Allah ya qasqantar da shi a duk inda baiyi zato ba" kai uncke farouq ke gayadawa cike da gamsuwa,tsohon dattijon qwarai ne,yana bala'in son zama da shi saboda dole ka dauki darasin rayuwa,idan ya shiga cikin wasu baka isa kace shine wannan professor din ba,kuma tsohon jakadan nijeria a qasar amurka.
Danja ta tsaidasu uncle farouq yaci burki da sauri saboda yana dan gudu,wanda hakan ya sanya katinan dake zube gaban motarshi suka zubo,jiya ya karbosu shi yasa aka yiwa malam su na daurin auren zainab ya baiwa anty dije ta tafar mai da su ragowar ya ajjiye wajansa zai bawa kawunshi
"Bismillahi" malam ya fada yana cewa
"Kaima ashe kana dan taba irin tuqin almustapha kenan ko?" Ya fada yana murmushu tare da duqawa yana kwaso katinan sa sukw zube din.
Caraf idanunshi suka kai kan sunan dake jikin katin wanda ke qunahe sa sanarwar daurin auren SULAIMAN AMINU DAHIRU GOMBE,sake maimata sunan yayi,sunann da ya kasance sak irin na tsohon amininshi sule,tsohon aminin da kullum zuciya ke begen ganawarsu,maimaita sunan ya dinga yi tare da kallon rubutun da aka tsarashi kalar golden,tamkar zai gano masa da zargin da zuciyarshu ta fara yi,uncle farouq ya lura da hakan sai yace
"Bikin qanwar mai sunan mama ne,wato 'yar yayar khadija" wawiyar ajiyar zuciya ya sauke ya maida dubanshi ga farouq
"A ina suke faruqu"
"A kano suke"
"Kano?,meys asalin mai gidan" kai ya girgiza cikin kokwanto
"Bamu taba zancan gaskiya da ita ba,amma dai a kano na sansu,wani abu ne baabaa?" Kai ya kada yana maida katinan mazaunansu
"Sunan ne kawai ya yimin kama da na wani tsohon aminina wanda har yau nake neman bayan ya bata tsahon shekaru"
"Ayyah,Allah ya bayyana shi"
"Amin amin faruqu". Bai bar babaan ba sai daya dangana da shi har cikin gidan sannan baabaan ya sauka yaba masa godiya,kunya duk ta kama faruqun,a rayuwa babu wani abu da zaiwa baban da har zai masa godiya,bayan babu wani nau'in karamci da kyautatawa da baban bai masa ba tun daga sanda ya sanshi har zuwa yau.
Tunda ya koma gidan baki daya ya kasa sukuni,katinan da sunan sun tsaye masa a rai,daren ranar kasa cikakken bacci yayi,yayi salloli sosai kafin ya samu bacci yayi awon gaba da shi,da asuba da ya tashi da abun ya tashi cikin ransa,har gari yayi haske,sai kawai ya tsinci kanshi da jawo kiran wayar uncke farouq ya buqaci adress din gidan mamallakin sunan da ya gani jikin katin,babu haufi ya tura masa don baya shakka cikin nagartan baabaan,yasan cewa koma mene alkhairi ne IN SHA ALLAH.
Waya kawai ya sake dagawa,ya lalubi lambar mahmoud ya buqaci ganinsa,ba bata lokaci ya iso kasancewar yana cikin gidan,sanar masa yayi ya laluba idan akwai jirgin da zai tashi daga abuja zuwa kano ya yankar masa ticket guda hudu,shi daya mahmoud din daya mus'ab wanda yazo biki bai koma thailand ba,da kuma drivansu,bai wani mamaki ba saboda yasan lokaci zuwa lokaci baaban nasu nayin tafiya kota ziyara ko duba gidajen gonar wannan babban aminin nashi da tunda suka taso suke jin sunanshi suka kuma haddaceshi,tare da riqe girma da matsayinsa wajen babansu,lokaci lokaci sukan yi bita da tilawarsa,saidai har kawo yanzu idanuwa basu taba ganinshi ba,cikin sa'a aka samu jirgin azaman wanda zai tashi ne da la'asar qarfe hudu na yamma,ba haka baban yaso ba amma haka ya karba.
Qarfe hudun jirgin ya lula da su sararin subhana zuwa kanon dabo,wanda cikin mintuna suka isa cikin yarjewa da ikon ubangiji tare da sahalewar ci gaban zamani irin na yanzu,kano tamkar gida take wajen baaban,saboda haka suna sauka suka tarar da motoci guda biyu suna jiran isowarshi,ba bata lokaci suka shiga suka fice daga airphort din.
Tana hanya taji kira,lambar amira ce,tun kafin ta daga ta saki murmushi
"Amaryar saifullahi bada kanki a sare" kamar wadda ke shirin sakin kuka ta soma mata qorafin kota nemeta ko?,sun hada baki da saifullahi sun sace mata wayarta,shi din ma ya rufe gidan ba shiga ba fita wai sai sun huta,ya kuma hanata wayarshi sai yau ya bata wayan,dariya ta dinga mata din yasan da wannan plan din,sai da ta gama qorafinta sannan suka gaisa tace yaushe zata zo don Allah
"Kin ganni hanyar kano,wani bikin ya sake kira na,bikin zainab dita"
"Wayyo,dama a kusa da namu ne,naci burin zuwa fa namecy" dariya tayi
"saidai ki tara ana halima idan Allah ya kawo"haka nan suka gama hirarsu ta baiwa saifullahin suka gaisa sannan sukayi sallama.
Kamar ko yaushe sunyi murna da zuwanta,mama nata tsokanar abdallah wai ya qara qiba
"Amma dai zaka koma ko?" Wuya ya maqale a kafadarsa
"Nan yafi dadi,can kullum kuna rufe a gida" dariya suka saki don abdallahn badai son yawo da wasa ba,hararshi sumayya tayi
"Nima babu inda zaka bini,rigimammen kawai" ko a jikinsa dariyarsa ma ya sanya abinsa,washe gari yaya yahansu tazo ta daukeshi ma sukayi tafiyarsu,sai ranar kamun zainab tace zata dawo da shi.
Tunda tazo babu zama suna ta shirye shirye ba kama hannun yaro,ita da anty salma qanwar mama da anty amina matan yaya abubakar,sunyi waya abdur rahman bai nan amma zai dawo da shi za'a yi daurin auren shi yasa take hidimarta hankali kwance ba wani damuwa ko takura,cikin ikon Allah da baiwarsa komai yana tafiya daidai,sumayya taga yadda ake komai cikin tsari saboda haka ta dage ta tsarawa 'yar uwarta komai yadda zai qawatar ya kuma burge,kudi sosai tasa yaya abubakar ya bata bayan wanda anty dije da uncle farouq suka bata,dinkuna sosai ta yiwa mama,atamfofi masu tsada da kyau,harda mayafai da takalma duk da yaya abubakar yayi musu amma tace wannan nata ne,sannan ta siyawa malam gezna ta asalin wadda zai sanya ranar daurin aure,takalmi mai kyau harda agogo da turare da sabon rawani fari qal,kasancewar malam din ba baya bane wajen tsafta shi yasa kusan kayansa galibi farare ne,aka yi masa dinkin babbar riga 'yar ciki da wando,ita kam dama bata da matsalar sutura sai anko kawai data yi,sai abdallah data masa shaddar daurin aure duk da dumbin kayan da yake da su,saura kwana tara biki kuwa saiga anty dije da iyalinta,nan aka shiga hidima sosai.
Kan hanyarsa yake ta dawowa daga airphort bayan ya kai anty dije da yaranta sun tashi zuwa kano,tun daga nesa yaga kamar motar baabaa prof a tsaye,hakan ya sanya ya rage gudun motar ya qaraso a hankali ya faka tashi motar bayan tasu sannan ya bude ya fito.
Baabaan ne tsaye gaban motar,kana dubanta kasan matsala ta basu,qarfen nasara da bashi da tabbas,motar kwata kwata shekararta guda,ba yadda mustapha baiyi kan a canzata ba kamar yadda ya saba sauya masa motocin hawanshi amma yace a sauya sauran amma ita banda ita,yana jin dadin motar,da ita yake zuwa gidan gonan sulensa duk qarshen sati,duk randa zai tafin baya tafiya da wasu motocin face wadda ita kadai zai hau,kuma daga shi sai druvansa,yana jin dadin zama gidan gonar,ya zazzaga yaga gidan gonar sosai,yanajin nishadi da farincikin yadda dukiyar sulensa ke habaka,fatanshi Allah nuna masa ranar da zaiga sulenshi,a irin haka ne yau motar ta tsaya musu a hanya.
A aladabce uncle farouq ya qaraso
"Subhanallah,baba kada dai ace qarfen nasara ya muku tsiya?" Cikin murmushi mai dauke da dattako yace
"Wallahi kuwa,to ya za'ayi,yau da gobe ai sai Allah,babu wani abu dake matabbaci"
"Gaskiya ne" inji uncle farouq yana fidda waya daga aljihunshi yana fadin
"Bari a kira gida to a turo wata ko baabaa,tamu motar ba lallai ka iya shiga irinta ba" murmushi ya kuma subucewa baban,har ya sanyashi ya juya ya sake kallon motar duk da ya santa,motace mai lafiya wadda bata da wani aibu ko makusa,ko kai waye zaka iya hawanta,amma ya sani cewa irin motocin da mustapha ke ajjiye masa yana hawa shi ya sanya farouq din tunanin yafi qarfin wannan
"Haba faruqu,saidai kawai idan rawar hawa motar take kake min,amma ni din waye da bazan hau wannan motar ba" ya fada yana dariya,bakinsa ya rufe shima yana dariya
"Afuwa baabaa" ya fada yana bude masa gaban motar,kafin ya shiga ya waiwaya ya dubi drivan nashi
"Kada ka tsawaita tsaiwa a nan,ka kira bakaniken nan,idan bakaniken ya iso ka bashi muqullan ka taho gida" a ladabce yace
"Yallabai man yace kada a sake barinka ka hau motar da baniken hanya ya tabata ranka ya dade" murmushi ya saki
"Qyale wannan,idan na biye masa ma a jirgin sama zan dinga yawo,ni waye da bakaniken hanya bazai taban mota ba,shi yasa na hana a kira gida agaya musu motarmu ta tsaya nasan zai iya jin zancan ya damu mutane da batub sauyan motoci,bayan ni din duka kwana nawa ya rage mana a duniya,kayi yadda nace kawai"
"To ranka ya dade" inji drivan,baban ya juya ya shiga motar faruqun ya rufe ya zagaya shima ya shiga ya tadata suka fara tafiya.
"Asalina daga qauye na fito faruqu,kiwon dabbobi na dinga yi ni da aminina,da can ko jaki bani da shi na hawa bare a kai ga mota,din me zan dinga manta asalina,ita duniya gaba dayanta yadda ka dauketa haka take zuwa maka,mafi daraja cikin mutane shine wanda a zahiri ya isan amma yake daukan kanshi ba'a bakin komai ba,girman kai rawanin tsiya ne,wanda ke zaton ya isa kuma sai Allah ya qasqantar da shi a duk inda baiyi zato ba" kai uncke farouq ke gayadawa cike da gamsuwa,tsohon dattijon qwarai ne,yana bala'in son zama da shi saboda dole ka dauki darasin rayuwa,idan ya shiga cikin wasu baka isa kace shine wannan professor din ba,kuma tsohon jakadan nijeria a qasar amurka.
Danja ta tsaidasu uncle farouq yaci burki da sauri saboda yana dan gudu,wanda hakan ya sanya katinan dake zube gaban motarshi suka zubo,jiya ya karbosu shi yasa aka yiwa malam su na daurin auren zainab ya baiwa anty dije ta tafar mai da su ragowar ya ajjiye wajansa zai bawa kawunshi
"Bismillahi" malam ya fada yana cewa
"Kaima ashe kana dan taba irin tuqin almustapha kenan ko?" Ya fada yana murmushu tare da duqawa yana kwaso katinan sa sukw zube din.
Caraf idanunshi suka kai kan sunan dake jikin katin wanda ke qunahe sa sanarwar daurin auren SULAIMAN AMINU DAHIRU GOMBE,sake maimata sunan yayi,sunann da ya kasance sak irin na tsohon amininshi sule,tsohon aminin da kullum zuciya ke begen ganawarsu,maimaita sunan ya dinga yi tare da kallon rubutun da aka tsarashi kalar golden,tamkar zai gano masa da zargin da zuciyarshu ta fara yi,uncle farouq ya lura da hakan sai yace
"Bikin qanwar mai sunan mama ne,wato 'yar yayar khadija" wawiyar ajiyar zuciya ya sauke ya maida dubanshi ga farouq
"A ina suke faruqu"
"A kano suke"
"Kano?,meys asalin mai gidan" kai ya girgiza cikin kokwanto
"Bamu taba zancan gaskiya da ita ba,amma dai a kano na sansu,wani abu ne baabaa?" Kai ya kada yana maida katinan mazaunansu
"Sunan ne kawai ya yimin kama da na wani tsohon aminina wanda har yau nake neman bayan ya bata tsahon shekaru"
"Ayyah,Allah ya bayyana shi"
"Amin amin faruqu". Bai bar babaan ba sai daya dangana da shi har cikin gidan sannan baabaan ya sauka yaba masa godiya,kunya duk ta kama faruqun,a rayuwa babu wani abu da zaiwa baban da har zai masa godiya,bayan babu wani nau'in karamci da kyautatawa da baban bai masa ba tun daga sanda ya sanshi har zuwa yau.
Tunda ya koma gidan baki daya ya kasa sukuni,katinan da sunan sun tsaye masa a rai,daren ranar kasa cikakken bacci yayi,yayi salloli sosai kafin ya samu bacci yayi awon gaba da shi,da asuba da ya tashi da abun ya tashi cikin ransa,har gari yayi haske,sai kawai ya tsinci kanshi da jawo kiran wayar uncke farouq ya buqaci adress din gidan mamallakin sunan da ya gani jikin katin,babu haufi ya tura masa don baya shakka cikin nagartan baabaan,yasan cewa koma mene alkhairi ne IN SHA ALLAH.
Waya kawai ya sake dagawa,ya lalubi lambar mahmoud ya buqaci ganinsa,ba bata lokaci ya iso kasancewar yana cikin gidan,sanar masa yayi ya laluba idan akwai jirgin da zai tashi daga abuja zuwa kano ya yankar masa ticket guda hudu,shi daya mahmoud din daya mus'ab wanda yazo biki bai koma thailand ba,da kuma drivansu,bai wani mamaki ba saboda yasan lokaci zuwa lokaci baaban nasu nayin tafiya kota ziyara ko duba gidajen gonar wannan babban aminin nashi da tunda suka taso suke jin sunanshi suka kuma haddaceshi,tare da riqe girma da matsayinsa wajen babansu,lokaci lokaci sukan yi bita da tilawarsa,saidai har kawo yanzu idanuwa basu taba ganinshi ba,cikin sa'a aka samu jirgin azaman wanda zai tashi ne da la'asar qarfe hudu na yamma,ba haka baban yaso ba amma haka ya karba.
Qarfe hudun jirgin ya lula da su sararin subhana zuwa kanon dabo,wanda cikin mintuna suka isa cikin yarjewa da ikon ubangiji tare da sahalewar ci gaban zamani irin na yanzu,kano tamkar gida take wajen baaban,saboda haka suna sauka suka tarar da motoci guda biyu suna jiran isowarshi,ba bata lokaci suka shiga suka fice daga airphort din.