Sashe 142
Kundin Kaddarata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ya tako zuwa gabanta bai gushe ba sai sa ya zo gab da gwiwoyinta sannan ya durqusa,dora hannunshi guda daya yayi saman kujerar gab da inda cinyarta take saidai basu hadu ba,ya sake motsa bakinsa zaiyi magana aka soma knocking qofar,dauke fuskanshi yayi ya maida qofar yana cewa
"Yes" wanda hakan ya baiwa mai son shigowar daman budewa ya shigo,daya daga cikin ma'aikatan asibitin ne,cikin mamakin ganin ogan nasu a haka yayi saurin cewa
"Am sorry sir" ya juya da niyyar ficewa,cikin sanyin murya yace
"Baka da damuwa,ya ake ciki?" Jin haka ya sashi dawowa yana satar kallon sumayya wadda kanta ke qasa,tuntube yayu da rug din dake shimfide wajen bai kula ba saboda kallon da yake matan,da sauri yace subahanalla sannan yayi hanzarin maida idonshi ga mustapha,wata muguwar harara ua watsa masa wadda ta sanya hanjinsa kadawa,ba tun yau ba yasan murtala mayen mata ne,ya sha bashi warning akan yadda yaje zuwa ya taddashi da mata suna hira suna qyaqyata dariya,cikin rawar jiki ya miqa masa wasu takaddu
"Gasu yallabai,mun gama komai mun bata gado,an gayara dakin thierther din"
"Good,kun tabbatar tun jiya bayan isha'in bata sake cin komai ba?"
"Eh yallabai"
"Ok,nan da one hour zamu shiga in sha Allah"
"To yallabai" ya fada yana juyawa,har ya kai qofa mustaphan ya sake tsaidashi
"Ban amince ku bad mijinta ya shiga dakin ba koda yazo,sannan ku san yadda zakuyi da sauran patient din dake jira,kwashe wadan can files din ka fita da su"
"To" ya amsa cikin rawar jiki ya tattare ya fita da su saboda yadda yake ta faman jifansa da wani irin kallo.
Da idanu ya rakashi har sai da yaga fitarsa sannan ya dauke idonshi ya sake maidawa kanta ya kafeta da su
"Da ba sai kinzo ba ma,ko baki zo ba dole baaba yace yau nazo" da sauri ta watsa masa idanunta wadanda ke jiqe da hawaye,me yake so yace?,biyoshi tayi?ciwon da take ji ita shi ya dameta,amma dole ta fahimtar da shi don bazata lamunce tana ji tana gani ya mata wata fassara ba
"Allah ya sawwaqe...i bab...ba kai na biyo ba,bansan ka ba bare....." Takaici ya turnuqeta ta kasa qarasawa
"Idan ba haka bane mai ya kawoki?,na tambayeki baki amsa ba,tabbacin maganata tana kan gaba kenan" banza tayi da shi tana digar hawaye,yayin da shi kuma yaci gaba da kallonta yana nazarinta,sai a sannan ya lura da hannunta wanda ke zaune saman mararta,hannun yabi da kallo sannan ya maida dubanshi fuskarta
"Tashi ki cire hijabin na duba miki" ya fadi yana matsawa da baya sannan ya miqe tsaye,shiru tayi masa kamar bata jiba,don bata ga dalilin da zai sanyata cire hijabinta ba,ransa ya soma baci da shariyarta,abinda bai qauna tsawon rayuwarsa,uhmmm wanzami dama hausawa suka ce baya son jarfa,sake matsawa baya yayi hannayensa zube cikin aljihunsa yana dubanta
"Ko kaxa baaba ya bani da hannunshi yace na kula da ita daga ranar tafi qarfin wulaqanci ko tozarci a wajena,kina neman ki hasalani nayi miki abinda banyi niyya ba ko?,kada ki yarda raina ya baci,idan kuwa ba haka ba bazakiji da dadiba,kina iya tashi ki tafi idan har ba zaki bari baaban yasan asibitina kuma gurina kika zo ba,kiyita zama da cutarki wannan ba damuwata bace" ya qarashe maganar yana daga kadunshi,hakan ya bata qwarin gwiwa ta muqe da hanzari duk da ciwon da takeji na tsikarinta,ta isa ga jakarta ta tattare kayanta ta maida ciki cikin hanzari,wanda hakan ya sabba ba mata manta hotunan mukhtar guda biyu qananu wanda suka zube ta doshi qofa abinta.
Wata zuciya ta taso masa,tana jin bata da kunya kenan?,ita din wace?,bai manta rashin kunyar data yi masa ba randa ta bigeshi duk don yace ta dinga kula,me take da shi da take wani qunshe qunshe,taku daya biyu ya isa inda take,hannunshi ya sanya ya finciko hijabin baki daya ya fiddashi daga jikinta wanda hakan ya sanya gashin kanta warwarewa baki daya,dama daureshi kawai tayi ba tare data sanya komai ba,hakan ya tilas ta mata tsayawa cak,waiwayowa tayi da niyyar sauke masa magana kwarjininsa ya cika idanuwanta
"Mijinki ne",kalaman malam suka dawo mata,ita din ba mai tsiwa ko rashin kunya bace tun da can baya,tun daga aurenta daga mukhtar zuwa lukman,bata iya kallon tsabar idon wanda ya girme mata tayi masa rashin kunya ba,sai yanzu zata fara?,a kan dan mutumin dake qaunarta,uba a gareta babban masoyi amini ga mahaifinta,sai ta runtse idanuwa,yayin da juyawar tata ya tilastawa mustapha kau da idamuwansa daga kanta,skert ne a jikinta da riga 'yan kanti,irin masu robar nan wadanda suke bin jikin mutum,gajeran hannu gareta,wuyanta kuma v.hape ne wanda ya fidda kyawun wuyanta zuwa qirjinta
"Idan ka wulqanta sumayya ka tabbatar wa kanka ni ka wulaqanta" maganar baabaa ta dawo mishi shima kwanyarsa,dukkaninsu lokaci guda umarnin iyayensu ya yi musu linzami,lokaci guda ya sauke dukkan wani abu da kowannansu keji game da dan uwansa a zuciyarsa,hijabinta ya wurga mata ba tare da ya dubeta ba,da yatsa yayi mata nuni da gadon dake bakin na'urar scanning,bata ce komai ba ta maida hijabinta jikinta,ta taka a hankali zuwa bakin gadon ta hau,sai da ya bada wasu mintuna sannan ya soma takawa zuwa kan gadon
"Kwanta" yace mata,idanu ta fiddo har sai da ya sake dubanta,da baya ta koma ta kwanta saman gadon
"Janye hijabin da rigarki" ya sake fada yana duban wani gurin,hijabin ta janye amma sai ta kasa janye rigar,sake waiwayowa yayi yaga abinda tayi,bai ce mata komai ba ya sanya hannunshi ya dage rigar,idanunta ta runtse zuciyarta na bugawa,da sauri ya sake rigar ya koma da baya,bai iya tuna mata nawa yayi wa scanning tun daga farawarsa aikin likita kama yau,mata daga nau'in yare jinsi da qasashe daban daban,amma haka kawai yake jin wannan bazai iyaba.
Bakin teburinsa ya isa ya soma qoqarin kiran reception ta wayar landline yana tambayarta
"Duk wata kina period dinki?"
"Eh" ta bashi masa murya can qasa cikin jin haushi da kunya
"When last kika ga period din" shiru tayi tana tunani,a qalla kusan watanni biyu kenan baizo mata ba
"Wata biyu"tabe baki yayi yana mamakin rashin damuwa da kai da har zakayi wannan watannin baka ga al'adarka ba kana zaune.
Wata nurse ce ta shigo wadda a qalla ta kusa shekara arba'in,cikin harshen nasara da tataccen engishinsa yake gaya mata abinda zata yi duka sumayyan na jinsu sai,a ladabce ta amsa ta qarasa inda sumayyan ke kwance,yayin da shi kuma yayi lamo cikin kujerarsa idanunshi a lumshe,yanajin yadda wata gajiya da kasala ke saukar masa,bai sake motsawa ba har nurse din ta kammala ta masa bayani idanunshi na arufe yana gyada kai,idanuwa sumayyan ta fiddo jin tana zancan scanning din da ake ta qasa za'a yi mata wanda nurse din bata iya ba,qirjinta ya dinga bugawa,ta soma ayyanawa a ranta yadda hakan zata kasance,sai data bayyana bayaninta tsaf sannan ya bude idanunshi wanda suka sauya launi kadan,ya jawo wata paper yayi rubutu da baifi layi hudu ba ya miqa mata yace ta karbo masa yanzu yana jira,karba tayi a ladabce ta fice.
Shiru ya ratsa office din sai qarar a.c dake buso sanyi tare da wani ni'imtaccen qamshi dake gauraye da office din,tana kwance wajen zuciyarta na bugawa
"sauko"ya fadi yana miqewa tsaye ya shige toilet,da hanzari ta sauko ta sanya takalmanta sannan ta dauki hijabinta ta nufi qofar,sau uku tana murzawa taqi buduwa,dole ta dawo ta zauna,wanda tana zama nurse din ta sake turo qofar ta shigo,saman teburin kawai ta dora maganin ta fice.
Fitowa yayi daga toilet din fuskarsa da hannayenaa wanda ya nannade hannun 'yar cikin suit dinsa jiqe da lema,da alamu alwala ya daura duk da ba lokacin yin sallah bane,bai dubeta ba ya isa gaban teburin ya fidda magungunan ya dudduba sannan ya koma gaban freezer din ya ciro ruwan roba,ya balli magungunan ya zube gabanta tare da ruwan sannan ya juya ya bude daya qofar wanda ke kusa data toilet ya shige bayan ya sanyawa qofar office din baki daya key,ba musu ta kwashi magungunan ta zuba a bakinta baki daya ta kora da ruwa ta hadiye,duk yadda taje qin magani haka ta hadasu baki daya ta hadiye,wannan karon ma ta sake jarraba bude qofar don bata ga mai zai zaunar kuma da ita na saidai taqi buduwa,a gaban idanunta ya rufe ba kuma tasan yanda zata bude din ba.
Fitowa yayi sanye da kayan da likitoci ke sanyawa duk sanda zasu shiga yin c.s,saidai nashi sun dan banbanta,saboda ash ne nasa,wanda suke a wanke fes da karin guga muraran a jikinsu,riga ce iya cinya mai qaramin hannu,sai dogon wando da hula,kamar ba kayan aiki ba sun masa kyau,qafanshi sanye takalmi plate sabanin dazu da yake sanye da ciki,qwanqwasa qofar aka soma yi baki dayansu suka dubi qofar,yana qoqarin sanya abun hanci yace
"Waye"
"Ranka ya dade Dr maqarfi ne" aka fada daga waje,takawa yake zuwa bakin qofar yana fadin
"Ki koma wancan dakin,ki dauki jakarki"
"Gida zan wuce,me zanyi a ciki?" Ta fada cikin zafi zafi,bai gasa nufar qofar ba bai kuma juyo ba yace
"Ba shi na tambayeki ba,kada ki yarda ya shigo ua ganki a nan"cikin qunan rai ta miqe ta dauki jakar tata,tana gunguni cikin zuciyarta ta tura qofar ta shige.
Baya yi zaton ganin dakin ba haka,daki ne sosai mai dauke da madaidaicin gado wanda ya wadatu da shimfidar bedsheet fara qal bayan lallausar katifar dake kai,shimfide dakin yake da carfet maroon sai fararen labulaye,daga daya bangon kwaba ce ta glass wadda aka tsarata cike da littattafai da suka shafi aikin likitanci,saj wata iriyar hanger kai kyau ta silver ta rataye kaya,qamshi dakin yake kamar ba cikin asibiti yake ba,gefan gadon ta qarasa a hankali ta yiwa kanta mazauni gefan gadon tana kalle kalle tana jiyo maganan mutumin da ya kira kanshi da dr maqarfi a cikin office din,magana suke kan tiyatar da zasu shiga yanzu.
Sauka idanuwanta sukayi kan wani dan qaramin frem dake zaune kan wata 'yar bedside,idanu ta saka sosai sai ta gane su'ad ce,sanye take cikin qananun kaya masu fidda sura,tayi makeup sosai tana dariya cikin hoton,kanta ta dauke tana wassafa yaya zama zai kasance tsakaninsu,tun tana karanta wasiqar jaki har bacci ya fara rinjayar idanuwanta,batasan sanda ta jingina da fuskan gadon ba yayi awon gaba da ita.
"Yes" wanda hakan ya baiwa mai son shigowar daman budewa ya shigo,daya daga cikin ma'aikatan asibitin ne,cikin mamakin ganin ogan nasu a haka yayi saurin cewa
"Am sorry sir" ya juya da niyyar ficewa,cikin sanyin murya yace
"Baka da damuwa,ya ake ciki?" Jin haka ya sashi dawowa yana satar kallon sumayya wadda kanta ke qasa,tuntube yayu da rug din dake shimfide wajen bai kula ba saboda kallon da yake matan,da sauri yace subahanalla sannan yayi hanzarin maida idonshi ga mustapha,wata muguwar harara ua watsa masa wadda ta sanya hanjinsa kadawa,ba tun yau ba yasan murtala mayen mata ne,ya sha bashi warning akan yadda yaje zuwa ya taddashi da mata suna hira suna qyaqyata dariya,cikin rawar jiki ya miqa masa wasu takaddu
"Gasu yallabai,mun gama komai mun bata gado,an gayara dakin thierther din"
"Good,kun tabbatar tun jiya bayan isha'in bata sake cin komai ba?"
"Eh yallabai"
"Ok,nan da one hour zamu shiga in sha Allah"
"To yallabai" ya fada yana juyawa,har ya kai qofa mustaphan ya sake tsaidashi
"Ban amince ku bad mijinta ya shiga dakin ba koda yazo,sannan ku san yadda zakuyi da sauran patient din dake jira,kwashe wadan can files din ka fita da su"
"To" ya amsa cikin rawar jiki ya tattare ya fita da su saboda yadda yake ta faman jifansa da wani irin kallo.
Da idanu ya rakashi har sai da yaga fitarsa sannan ya dauke idonshi ya sake maidawa kanta ya kafeta da su
"Da ba sai kinzo ba ma,ko baki zo ba dole baaba yace yau nazo" da sauri ta watsa masa idanunta wadanda ke jiqe da hawaye,me yake so yace?,biyoshi tayi?ciwon da take ji ita shi ya dameta,amma dole ta fahimtar da shi don bazata lamunce tana ji tana gani ya mata wata fassara ba
"Allah ya sawwaqe...i bab...ba kai na biyo ba,bansan ka ba bare....." Takaici ya turnuqeta ta kasa qarasawa
"Idan ba haka bane mai ya kawoki?,na tambayeki baki amsa ba,tabbacin maganata tana kan gaba kenan" banza tayi da shi tana digar hawaye,yayin da shi kuma yaci gaba da kallonta yana nazarinta,sai a sannan ya lura da hannunta wanda ke zaune saman mararta,hannun yabi da kallo sannan ya maida dubanshi fuskarta
"Tashi ki cire hijabin na duba miki" ya fadi yana matsawa da baya sannan ya miqe tsaye,shiru tayi masa kamar bata jiba,don bata ga dalilin da zai sanyata cire hijabinta ba,ransa ya soma baci da shariyarta,abinda bai qauna tsawon rayuwarsa,uhmmm wanzami dama hausawa suka ce baya son jarfa,sake matsawa baya yayi hannayensa zube cikin aljihunsa yana dubanta
"Ko kaxa baaba ya bani da hannunshi yace na kula da ita daga ranar tafi qarfin wulaqanci ko tozarci a wajena,kina neman ki hasalani nayi miki abinda banyi niyya ba ko?,kada ki yarda raina ya baci,idan kuwa ba haka ba bazakiji da dadiba,kina iya tashi ki tafi idan har ba zaki bari baaban yasan asibitina kuma gurina kika zo ba,kiyita zama da cutarki wannan ba damuwata bace" ya qarashe maganar yana daga kadunshi,hakan ya bata qwarin gwiwa ta muqe da hanzari duk da ciwon da takeji na tsikarinta,ta isa ga jakarta ta tattare kayanta ta maida ciki cikin hanzari,wanda hakan ya sabba ba mata manta hotunan mukhtar guda biyu qananu wanda suka zube ta doshi qofa abinta.
Wata zuciya ta taso masa,tana jin bata da kunya kenan?,ita din wace?,bai manta rashin kunyar data yi masa ba randa ta bigeshi duk don yace ta dinga kula,me take da shi da take wani qunshe qunshe,taku daya biyu ya isa inda take,hannunshi ya sanya ya finciko hijabin baki daya ya fiddashi daga jikinta wanda hakan ya sanya gashin kanta warwarewa baki daya,dama daureshi kawai tayi ba tare data sanya komai ba,hakan ya tilas ta mata tsayawa cak,waiwayowa tayi da niyyar sauke masa magana kwarjininsa ya cika idanuwanta
"Mijinki ne",kalaman malam suka dawo mata,ita din ba mai tsiwa ko rashin kunya bace tun da can baya,tun daga aurenta daga mukhtar zuwa lukman,bata iya kallon tsabar idon wanda ya girme mata tayi masa rashin kunya ba,sai yanzu zata fara?,a kan dan mutumin dake qaunarta,uba a gareta babban masoyi amini ga mahaifinta,sai ta runtse idanuwa,yayin da juyawar tata ya tilastawa mustapha kau da idamuwansa daga kanta,skert ne a jikinta da riga 'yan kanti,irin masu robar nan wadanda suke bin jikin mutum,gajeran hannu gareta,wuyanta kuma v.hape ne wanda ya fidda kyawun wuyanta zuwa qirjinta
"Idan ka wulqanta sumayya ka tabbatar wa kanka ni ka wulaqanta" maganar baabaa ta dawo mishi shima kwanyarsa,dukkaninsu lokaci guda umarnin iyayensu ya yi musu linzami,lokaci guda ya sauke dukkan wani abu da kowannansu keji game da dan uwansa a zuciyarsa,hijabinta ya wurga mata ba tare da ya dubeta ba,da yatsa yayi mata nuni da gadon dake bakin na'urar scanning,bata ce komai ba ta maida hijabinta jikinta,ta taka a hankali zuwa bakin gadon ta hau,sai da ya bada wasu mintuna sannan ya soma takawa zuwa kan gadon
"Kwanta" yace mata,idanu ta fiddo har sai da ya sake dubanta,da baya ta koma ta kwanta saman gadon
"Janye hijabin da rigarki" ya sake fada yana duban wani gurin,hijabin ta janye amma sai ta kasa janye rigar,sake waiwayowa yayi yaga abinda tayi,bai ce mata komai ba ya sanya hannunshi ya dage rigar,idanunta ta runtse zuciyarta na bugawa,da sauri ya sake rigar ya koma da baya,bai iya tuna mata nawa yayi wa scanning tun daga farawarsa aikin likita kama yau,mata daga nau'in yare jinsi da qasashe daban daban,amma haka kawai yake jin wannan bazai iyaba.
Bakin teburinsa ya isa ya soma qoqarin kiran reception ta wayar landline yana tambayarta
"Duk wata kina period dinki?"
"Eh" ta bashi masa murya can qasa cikin jin haushi da kunya
"When last kika ga period din" shiru tayi tana tunani,a qalla kusan watanni biyu kenan baizo mata ba
"Wata biyu"tabe baki yayi yana mamakin rashin damuwa da kai da har zakayi wannan watannin baka ga al'adarka ba kana zaune.
Wata nurse ce ta shigo wadda a qalla ta kusa shekara arba'in,cikin harshen nasara da tataccen engishinsa yake gaya mata abinda zata yi duka sumayyan na jinsu sai,a ladabce ta amsa ta qarasa inda sumayyan ke kwance,yayin da shi kuma yayi lamo cikin kujerarsa idanunshi a lumshe,yanajin yadda wata gajiya da kasala ke saukar masa,bai sake motsawa ba har nurse din ta kammala ta masa bayani idanunshi na arufe yana gyada kai,idanuwa sumayyan ta fiddo jin tana zancan scanning din da ake ta qasa za'a yi mata wanda nurse din bata iya ba,qirjinta ya dinga bugawa,ta soma ayyanawa a ranta yadda hakan zata kasance,sai data bayyana bayaninta tsaf sannan ya bude idanunshi wanda suka sauya launi kadan,ya jawo wata paper yayi rubutu da baifi layi hudu ba ya miqa mata yace ta karbo masa yanzu yana jira,karba tayi a ladabce ta fice.
Shiru ya ratsa office din sai qarar a.c dake buso sanyi tare da wani ni'imtaccen qamshi dake gauraye da office din,tana kwance wajen zuciyarta na bugawa
"sauko"ya fadi yana miqewa tsaye ya shige toilet,da hanzari ta sauko ta sanya takalmanta sannan ta dauki hijabinta ta nufi qofar,sau uku tana murzawa taqi buduwa,dole ta dawo ta zauna,wanda tana zama nurse din ta sake turo qofar ta shigo,saman teburin kawai ta dora maganin ta fice.
Fitowa yayi daga toilet din fuskarsa da hannayenaa wanda ya nannade hannun 'yar cikin suit dinsa jiqe da lema,da alamu alwala ya daura duk da ba lokacin yin sallah bane,bai dubeta ba ya isa gaban teburin ya fidda magungunan ya dudduba sannan ya koma gaban freezer din ya ciro ruwan roba,ya balli magungunan ya zube gabanta tare da ruwan sannan ya juya ya bude daya qofar wanda ke kusa data toilet ya shige bayan ya sanyawa qofar office din baki daya key,ba musu ta kwashi magungunan ta zuba a bakinta baki daya ta kora da ruwa ta hadiye,duk yadda taje qin magani haka ta hadasu baki daya ta hadiye,wannan karon ma ta sake jarraba bude qofar don bata ga mai zai zaunar kuma da ita na saidai taqi buduwa,a gaban idanunta ya rufe ba kuma tasan yanda zata bude din ba.
Fitowa yayi sanye da kayan da likitoci ke sanyawa duk sanda zasu shiga yin c.s,saidai nashi sun dan banbanta,saboda ash ne nasa,wanda suke a wanke fes da karin guga muraran a jikinsu,riga ce iya cinya mai qaramin hannu,sai dogon wando da hula,kamar ba kayan aiki ba sun masa kyau,qafanshi sanye takalmi plate sabanin dazu da yake sanye da ciki,qwanqwasa qofar aka soma yi baki dayansu suka dubi qofar,yana qoqarin sanya abun hanci yace
"Waye"
"Ranka ya dade Dr maqarfi ne" aka fada daga waje,takawa yake zuwa bakin qofar yana fadin
"Ki koma wancan dakin,ki dauki jakarki"
"Gida zan wuce,me zanyi a ciki?" Ta fada cikin zafi zafi,bai gasa nufar qofar ba bai kuma juyo ba yace
"Ba shi na tambayeki ba,kada ki yarda ya shigo ua ganki a nan"cikin qunan rai ta miqe ta dauki jakar tata,tana gunguni cikin zuciyarta ta tura qofar ta shige.
Baya yi zaton ganin dakin ba haka,daki ne sosai mai dauke da madaidaicin gado wanda ya wadatu da shimfidar bedsheet fara qal bayan lallausar katifar dake kai,shimfide dakin yake da carfet maroon sai fararen labulaye,daga daya bangon kwaba ce ta glass wadda aka tsarata cike da littattafai da suka shafi aikin likitanci,saj wata iriyar hanger kai kyau ta silver ta rataye kaya,qamshi dakin yake kamar ba cikin asibiti yake ba,gefan gadon ta qarasa a hankali ta yiwa kanta mazauni gefan gadon tana kalle kalle tana jiyo maganan mutumin da ya kira kanshi da dr maqarfi a cikin office din,magana suke kan tiyatar da zasu shiga yanzu.
Sauka idanuwanta sukayi kan wani dan qaramin frem dake zaune kan wata 'yar bedside,idanu ta saka sosai sai ta gane su'ad ce,sanye take cikin qananun kaya masu fidda sura,tayi makeup sosai tana dariya cikin hoton,kanta ta dauke tana wassafa yaya zama zai kasance tsakaninsu,tun tana karanta wasiqar jaki har bacci ya fara rinjayar idanuwanta,batasan sanda ta jingina da fuskan gadon ba yayi awon gaba da ita.